Sashe 18
Doguwar Hanya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mom Nu'aiym.
[11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: 🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇*
*Billy Galadanchi*
*Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)*
*please book nawa na siyarwa ne, idan kinaso ki karanta ki biya kud'in ki a sakaki a group, 07084161619*
15
K'uru zirga zirga yakeyi cikin tsananin tashin hankali, duk tsafin daya dace ya sanya ayi ya saka anyi amma har yanzun Lawurin sa bata dawo gida ba, anje garin kusa dasu ma amma shiru kakeji, tunda yae sa'a wani acikin bayinsa ya tsallaka ruwa ya samu sacrifice yake cikin murna sedai tashin hankalin rashin Lawuri, dole seya nemota amma besan akwai wata duniya ba bayan tasu data mutanen dake tsallako ruwa suzo, mutanen daya gani da wannan abun kashe mutum abun ya tsorata shi, ga K'uruwa ma ta dena cin abinci kullum zancen kenan Lawuri.
"So nakeyi aje nemanta har waccen duniyar dabansan ya ake zuwa ba, ina buk'atar yarinyar nan ta dawo ko anaso ko ba'aso" Kallonsa Barden garin yar
"Zamuje mu nemota, koda xamu mutu ne K'uru sarkin adalci ka kwanta kayi bacci dole zata dawo" haka suka shirya sunkai su 20 aka soma nausar jeji.
*************
Rik'e take da book a hannunta ta k'urawa rubutun ido kurun amma sam bata gane komai, bazata iya rubutu ba ko karatu tasani har abada amma hausar dai tanaso ta koya, so take ta iya yaren Aboo Wurairai (In Lawuri's voice), ta rik'ayin hira dashi kafin ta koma garin su, kife littafin tae ta mik'e zuwa cikin gidan sabida tanaso tasha ruwa, zuwa yanzu tasoma sabawa da d'and'anon ruwansu me sanyaya zuciya, kai tsaye ciki tashiga bayan tayi sallama ba kowa a parlor d'in, kitchen ta wuce ta bud'a fridge ta d'akko robar ruwa d'aya ta shiga dudduba kofi, sedaga cen ta samu tana fitowa sukai karo da Hanifer cup d'in ya sub'uce mata dama na glass ne lokaci d'aya ya tarwatse, cikin tsoro taja da baya bata tab'a tsammanin abun yana tarwatsewa har haka ba
"Hanty Anny hakuri kinji?" Ta furta muryanta yana rawa, tsaki hanifer tae
"Dama mana Arniyar jeji, yaya zaki yi abu cikin nutsuwa wama ya baki damar d'akko cup na daddy kizo harki fasa? Wlhy yau keda mommy ne, zuwa zan na fad'a mata abinda kikayi idan akwai wanda kika tab'a ganin ya d'akko cup d'in daddy yana amfani dashi" ta gano masifar takeyi dukda bajin me takecewa duka take ba,jin ta ambaci momy ma ya k'ara firgitar da ita tasani kashinta ya bushe, kuka ta hauyi tana rok'onta amma da gudu ta juya saman, segata sun dawo tare da mom har lokacin kuwa Lawuri tana nan tsaye tana sharar k'walla, salati mom ta hauyi tana tafa hannu
"Hanifer d'akkomun dorinan danake zane su Nu'aiym shida Khabbab kizo ki sameni a garden tare da ita zakizo" haka Ta wuce garden Hanifer kuwa ta wuce saman ta d'akko dorina ta kuma zo taja hannun Lawuri garin tsallakawa qatoton glass ya cake ta, k'ara ta kwalla yayinda hanifer ta tizgeta zuwa garden d'in cikeda fushi, d'ingishi ta somayi tana kuka amma ko kallonta hanifer batayi ba taci gaba da janta har garden, mom zama tae akan kujera hanifer ma haka
"Hanifer tashi ki nuna mata yanda zatayi kneeldown" mik'ewa tae tayi kneel down agabanta tana nuna mata da hannu akan itama tayi, ba musu tayi harda d'age hannayenta sama yanda hanny tae, tana ganin tayi ta mike itama ta mik'e wanka mata mari hanny tae
"Danla ki koma wayace ki mik'e?" Bata gane abinda take nufi ba ga glass a qafanta se kuka take tana ambatar kalmar ki Akuri da k'yar, duka sosai mom ta mata da dorina ta kira Dawood a waya
"Ga wannan mejin yarbancin Arniyar yarinyar dakuka kawomun agida na, ka sanar mata glass cup data d'auka tasha ruwa harta fasa na daddy ne nxt time idan taga abu ta rink'a bincikawa danni ba lamuni zan mata ba" tana kaiwa nan ta kara wayar a kunnen Lawuri daga cen yayi Lawurin bayani akan shine ga abinda akace tayi ta rik'a kiyaye, tana kuka ta ansashi da ta dena zata nasu hak'uri amma a mayar da ita garin su
"Zamuyi magana idan nazo Lawuri kinji, yanzu kiyi hak'uri" godiya ta masa sannan suka karb'i wayar dukai hanyar ciki ita duka barta nan
"Allah Hanifer banajin dad'in yanda nakewa yarinyar nan, kurun dai na tsane ta ne so nake wuya tasa tabar gidan ba komai ba" jinjina kai hanifer tae
"To mom harga Allah aibaki da laifi, tunda laifi tae kika hukuntata" Jinjina kai mom tae alamar gamsu kafin tace
"Amma naga kaman Glass yashiga k'afanta kidubata da kanki" Jinjina kai Hanifer tae
"To mom zan duba ta inshaa Allah" Barbo ce ta tattare kwalban ita kuwa hanifer tunda ta shiga hidimar girkin daza'aci na dare bata k'ara tunawa da wata Lawuri ba...
**************
Tunda ta sanya kiran wayansa agaba be d'aga ba take cikin yamutsi, ta cab'a ado iya ado sedai babu walwalar zuci, mesa ne ita Pure heart yake mata haka? Meta masa ina laifin masoyinka? Shirin zuwa gun k'awarta tafito da amma se kurun ta karkata akalar motarta zuwa Tile making company nasu ta tabbatar yana cen yanzu.
Kai tsaye office nashi ta nufa, akai mata iso ta shiga, fuskar nan babu walwala ya tarbeta
"Me kika zo kimun anan?" Kallon sa tae har idanta sun sauya sunyi ja
"Meye laifi na sufyan? Mena maka hakane wai? Na dinga kiranka kenan a waya baka d'agawa? Sannan kuma baka kirana, baka zuwa inda nake ni idan nazo seya zama laifi? Yaya kakeso nayi da rayuwata ne wai?" Hannunshi ya ssanya ya shafi sumar kansa
"Na sanar dake ai banaso kike yawaita kirana a waya ko? Nakuma sanar dake ba girmanki bane ba ace kina kawomun ziyara da kanki" cikin damuwa ta furta
"Amma idan nakira baka d'auka bafa? Kokuma idan na kira baka kirani back ba fa? Idan inaso na ganka amma bakazo bafa ya zanyi ehm Abu sufyan?" Ta k'arashe maganar cikin tausayawa kanta har tana zubar da hawaye, tausayi sosai ta bashi ya tashi daga kan kujerar da take yazo ya zauna kujerar dake fuskantar nata, cikin sanyin murya yace
"Kiyi hakuri my Ayusher kinji? Ni abunda banaso missd col ya wuce 1, idan da kin kira so d'aya ban d'aukaba idan kika jirani zan kiraki back ne, zancen ziyara kuma naji, yanzu so nawa kikeso ki ganni a sati?" Share hawayen ta tae
"Nagode sosai pure heart ni idan da wannan kalaman masu dad'i kurin ka barni zan gode maka" Murmushi yae
"Gayamun mana so nawa kikeso ki ganni a sati?"
"Niko sa d'aya ne ma kaji" murmushi yae
"Nacire kwana uku kacal a sati, zaki ganni so 4, inshaa Allah muddin ina garin nan, kira waya kuma zanna riqa kiranki kullum safe da dare wannan fa ta miki?" Ya k'arashe maganar cikin sakin fuska sosai
"Nagode pure heart" murmushi yae
"Da driver kikazo?"
"Da kaina nazo" mik'ewa yae
"Muje gidan mom nayi wanka semuje yawon yamma" murmushi tae itama ta mik'e
"Zaka sanya mom tace bana zuwar mata se idan kai ka kawoni ko" mirmushi yae
"Idan bazakiba sena tafi abuna" Rike baki tai tana murmushi
"Nina isa nace bazani ba? Aiban isaba ko pure heart?" Murmushi yae suka fita.
Aqilu ya wurgawa key na motar Ayusher ya cafe yace
"Ka kai motar gidan Su Ayusher ka baiwa gate man na gidan kace injita ya ajiye agunsa harta dawo" cikin girmamawa yace
"To yallab'ai" Takardar dubu d'aya ya zaro ya mik'a masa
"Kayi tranport zuwa gida daga nan" nanma godiya yae ya juya.
**********
A b'angaren Lawuri kuwa yau duk kuka ta wuni yi, ta samu Barbo ta cire mata glass d'in amma sun duba a garden d'in babu wani ganye daze iya tsayar da jinin da k'afar keyi,wajen gidan Barbo taje ta duba ko akwai ganyaye irin na garinsu....... Zaman dirshan tae a bakin gate d'in tana jiran isowar Barbo sabida yanda jinin ke zuba, ga yau banda masu gadin gidan duka sojojin sun kama gabansu,Shigowar barbo yayi daidai da dosowar motar Abu sufyan gidan, parking yae ya fito daga motar ya bita da kallon mamaki kafin ya k'ara wurinta cikin azama, durqusawa yae ya tallafi k'afar ba laifi tasha faso da kirci na rayuwar jeji
"Meya samu k'afar haka ne?" Amaimakon ta bashi ansa se kurun ta shiga rera masa kuka wiwi..... Nuni ya mata da hannu alamun ta mik'e a hankali ta tashi ta doma d'ingisawa tabi bayanshi zuwa ciki, Hanifer ya soma k'wallawa kira yama manta da wata Ayusher dasuka zo tare, da sauri ta sakko daga saman
"Zoki treating wound na yarinyar nan, bansan meya same taba" tab'e baki tae
"Yaa sufyan kofin dad ta d'akko na shan ruwa, shine kuma ta fasa shi garin gidadanci ta taka glass nisam nama manta mom tace na duba mata gun" Haukace mata yae da masifa, ita kuwa Ayusher tayi sororo tana jiyo su, haka ya dinga masifa har sanda ta shiga taitayinta, ya haura saman mom itama
"Mom yanzu daidai ne dan Allah, yarin yarnan fa mom mutum ce fa? Amma ace kun barta da miki haka tun safe kuma akan glass cup ace hadda duka, Hanny ta gayamun kin dake ta kuma nima na gani duk jikinta ya fashe" Mik'e wa tae daga zaman datake
"To ubana seka daken ai, nace seka daken, ni yanzu Sufyan ni kakewa magana irin haka acen wancen banzar, yaushe ta juyar mun da kanka har haka? Yaushe ma kai ka isa ka gayamun abinda ya dace ya wanda be dace ba?" Saukar da kanshi yae k'asa
"Mom kiyi hakuri kurun naga an qyale tane acikin jini tun safe shiyasa" tsaki taja tafice daga d'akin gaba daya.
Seda aka bata anti tetanus sannan akae dressing na gun se kuka take, lokacin ne barbo ta tallafeta zuwa d'akin su.
Sun baiwa Ayusher tausayi sosai bako na wasa ba, bataso taga ana cutar da mutane ita kam,amma haka ta gaisa da mutane gidan ta zauna a darare har ya kimtsa suka fita, fitar ba dadi sabida fuskar babu wata walwala haka suka yishi.
[11/20, 3:01 PM] Maamah twins💕❤: 🏇🏇DOGUWAR HANYA....🏇🏇*
*Billy Galadanchi*
*Haske writer's Association(home of expert and perfect writer's)*
*please book nawa na siyarwa ne, idan kinaso ki karanta ki biya kud'in ki a sakaki a group, 07084161619*
15
K'uru zirga zirga yakeyi cikin tsananin tashin hankali, duk tsafin daya dace ya sanya ayi ya saka anyi amma har yanzun Lawurin sa bata dawo gida ba, anje garin kusa dasu ma amma shiru kakeji, tunda yae sa'a wani acikin bayinsa ya tsallaka ruwa ya samu sacrifice yake cikin murna sedai tashin hankalin rashin Lawuri, dole seya nemota amma besan akwai wata duniya ba bayan tasu data mutanen dake tsallako ruwa suzo, mutanen daya gani da wannan abun kashe mutum abun ya tsorata shi, ga K'uruwa ma ta dena cin abinci kullum zancen kenan Lawuri.
"So nakeyi aje nemanta har waccen duniyar dabansan ya ake zuwa ba, ina buk'atar yarinyar nan ta dawo ko anaso ko ba'aso" Kallonsa Barden garin yar
"Zamuje mu nemota, koda xamu mutu ne K'uru sarkin adalci ka kwanta kayi bacci dole zata dawo" haka suka shirya sunkai su 20 aka soma nausar jeji.
*************
Rik'e take da book a hannunta ta k'urawa rubutun ido kurun amma sam bata gane komai, bazata iya rubutu ba ko karatu tasani har abada amma hausar dai tanaso ta koya, so take ta iya yaren Aboo Wurairai (In Lawuri's voice), ta rik'ayin hira dashi kafin ta koma garin su, kife littafin tae ta mik'e zuwa cikin gidan sabida tanaso tasha ruwa, zuwa yanzu tasoma sabawa da d'and'anon ruwansu me sanyaya zuciya, kai tsaye ciki tashiga bayan tayi sallama ba kowa a parlor d'in, kitchen ta wuce ta bud'a fridge ta d'akko robar ruwa d'aya ta shiga dudduba kofi, sedaga cen ta samu tana fitowa sukai karo da Hanifer cup d'in ya sub'uce mata dama na glass ne lokaci d'aya ya tarwatse, cikin tsoro taja da baya bata tab'a tsammanin abun yana tarwatsewa har haka ba
"Hanty Anny hakuri kinji?" Ta furta muryanta yana rawa, tsaki hanifer tae
"Dama mana Arniyar jeji, yaya zaki yi abu cikin nutsuwa wama ya baki damar d'akko cup na daddy kizo harki fasa? Wlhy yau keda mommy ne, zuwa zan na fad'a mata abinda kikayi idan akwai wanda kika tab'a ganin ya d'akko cup d'in daddy yana amfani dashi" ta gano masifar takeyi dukda bajin me takecewa duka take ba,jin ta ambaci momy ma ya k'ara firgitar da ita tasani kashinta ya bushe, kuka ta hauyi tana rok'onta amma da gudu ta juya saman, segata sun dawo tare da mom har lokacin kuwa Lawuri tana nan tsaye tana sharar k'walla, salati mom ta hauyi tana tafa hannu
"Hanifer d'akkomun dorinan danake zane su Nu'aiym shida Khabbab kizo ki sameni a garden tare da ita zakizo" haka Ta wuce garden Hanifer kuwa ta wuce saman ta d'akko dorina ta kuma zo taja hannun Lawuri garin tsallakawa qatoton glass ya cake ta, k'ara ta kwalla yayinda hanifer ta tizgeta zuwa garden d'in cikeda fushi, d'ingishi ta somayi tana kuka amma ko kallonta hanifer batayi ba taci gaba da janta har garden, mom zama tae akan kujera hanifer ma haka
"Hanifer tashi ki nuna mata yanda zatayi kneeldown" mik'ewa tae tayi kneel down agabanta tana nuna mata da hannu akan itama tayi, ba musu tayi harda d'age hannayenta sama yanda hanny tae, tana ganin tayi ta mike itama ta mik'e wanka mata mari hanny tae
"Danla ki koma wayace ki mik'e?" Bata gane abinda take nufi ba ga glass a qafanta se kuka take tana ambatar kalmar ki Akuri da k'yar, duka sosai mom ta mata da dorina ta kira Dawood a waya
"Ga wannan mejin yarbancin Arniyar yarinyar dakuka kawomun agida na, ka sanar mata glass cup data d'auka tasha ruwa harta fasa na daddy ne nxt time idan taga abu ta rink'a bincikawa danni ba lamuni zan mata ba" tana kaiwa nan ta kara wayar a kunnen Lawuri daga cen yayi Lawurin bayani akan shine ga abinda akace tayi ta rik'a kiyaye, tana kuka ta ansashi da ta dena zata nasu hak'uri amma a mayar da ita garin su
"Zamuyi magana idan nazo Lawuri kinji, yanzu kiyi hak'uri" godiya ta masa sannan suka karb'i wayar dukai hanyar ciki ita duka barta nan
"Allah Hanifer banajin dad'in yanda nakewa yarinyar nan, kurun dai na tsane ta ne so nake wuya tasa tabar gidan ba komai ba" jinjina kai hanifer tae
"To mom harga Allah aibaki da laifi, tunda laifi tae kika hukuntata" Jinjina kai mom tae alamar gamsu kafin tace
"Amma naga kaman Glass yashiga k'afanta kidubata da kanki" Jinjina kai Hanifer tae
"To mom zan duba ta inshaa Allah" Barbo ce ta tattare kwalban ita kuwa hanifer tunda ta shiga hidimar girkin daza'aci na dare bata k'ara tunawa da wata Lawuri ba...
**************
Tunda ta sanya kiran wayansa agaba be d'aga ba take cikin yamutsi, ta cab'a ado iya ado sedai babu walwalar zuci, mesa ne ita Pure heart yake mata haka? Meta masa ina laifin masoyinka? Shirin zuwa gun k'awarta tafito da amma se kurun ta karkata akalar motarta zuwa Tile making company nasu ta tabbatar yana cen yanzu.
Kai tsaye office nashi ta nufa, akai mata iso ta shiga, fuskar nan babu walwala ya tarbeta
"Me kika zo kimun anan?" Kallon sa tae har idanta sun sauya sunyi ja
"Meye laifi na sufyan? Mena maka hakane wai? Na dinga kiranka kenan a waya baka d'agawa? Sannan kuma baka kirana, baka zuwa inda nake ni idan nazo seya zama laifi? Yaya kakeso nayi da rayuwata ne wai?" Hannunshi ya ssanya ya shafi sumar kansa
"Na sanar dake ai banaso kike yawaita kirana a waya ko? Nakuma sanar dake ba girmanki bane ba ace kina kawomun ziyara da kanki" cikin damuwa ta furta
"Amma idan nakira baka d'auka bafa? Kokuma idan na kira baka kirani back ba fa? Idan inaso na ganka amma bakazo bafa ya zanyi ehm Abu sufyan?" Ta k'arashe maganar cikin tausayawa kanta har tana zubar da hawaye, tausayi sosai ta bashi ya tashi daga kan kujerar da take yazo ya zauna kujerar dake fuskantar nata, cikin sanyin murya yace
"Kiyi hakuri my Ayusher kinji? Ni abunda banaso missd col ya wuce 1, idan da kin kira so d'aya ban d'aukaba idan kika jirani zan kiraki back ne, zancen ziyara kuma naji, yanzu so nawa kikeso ki ganni a sati?" Share hawayen ta tae
"Nagode sosai pure heart ni idan da wannan kalaman masu dad'i kurin ka barni zan gode maka" Murmushi yae
"Gayamun mana so nawa kikeso ki ganni a sati?"
"Niko sa d'aya ne ma kaji" murmushi yae
"Nacire kwana uku kacal a sati, zaki ganni so 4, inshaa Allah muddin ina garin nan, kira waya kuma zanna riqa kiranki kullum safe da dare wannan fa ta miki?" Ya k'arashe maganar cikin sakin fuska sosai
"Nagode pure heart" murmushi yae
"Da driver kikazo?"
"Da kaina nazo" mik'ewa yae
"Muje gidan mom nayi wanka semuje yawon yamma" murmushi tae itama ta mik'e
"Zaka sanya mom tace bana zuwar mata se idan kai ka kawoni ko" mirmushi yae
"Idan bazakiba sena tafi abuna" Rike baki tai tana murmushi
"Nina isa nace bazani ba? Aiban isaba ko pure heart?" Murmushi yae suka fita.
Aqilu ya wurgawa key na motar Ayusher ya cafe yace
"Ka kai motar gidan Su Ayusher ka baiwa gate man na gidan kace injita ya ajiye agunsa harta dawo" cikin girmamawa yace
"To yallab'ai" Takardar dubu d'aya ya zaro ya mik'a masa
"Kayi tranport zuwa gida daga nan" nanma godiya yae ya juya.
**********
A b'angaren Lawuri kuwa yau duk kuka ta wuni yi, ta samu Barbo ta cire mata glass d'in amma sun duba a garden d'in babu wani ganye daze iya tsayar da jinin da k'afar keyi,wajen gidan Barbo taje ta duba ko akwai ganyaye irin na garinsu....... Zaman dirshan tae a bakin gate d'in tana jiran isowar Barbo sabida yanda jinin ke zuba, ga yau banda masu gadin gidan duka sojojin sun kama gabansu,Shigowar barbo yayi daidai da dosowar motar Abu sufyan gidan, parking yae ya fito daga motar ya bita da kallon mamaki kafin ya k'ara wurinta cikin azama, durqusawa yae ya tallafi k'afar ba laifi tasha faso da kirci na rayuwar jeji
"Meya samu k'afar haka ne?" Amaimakon ta bashi ansa se kurun ta shiga rera masa kuka wiwi..... Nuni ya mata da hannu alamun ta mik'e a hankali ta tashi ta doma d'ingisawa tabi bayanshi zuwa ciki, Hanifer ya soma k'wallawa kira yama manta da wata Ayusher dasuka zo tare, da sauri ta sakko daga saman
"Zoki treating wound na yarinyar nan, bansan meya same taba" tab'e baki tae
"Yaa sufyan kofin dad ta d'akko na shan ruwa, shine kuma ta fasa shi garin gidadanci ta taka glass nisam nama manta mom tace na duba mata gun" Haukace mata yae da masifa, ita kuwa Ayusher tayi sororo tana jiyo su, haka ya dinga masifa har sanda ta shiga taitayinta, ya haura saman mom itama
"Mom yanzu daidai ne dan Allah, yarin yarnan fa mom mutum ce fa? Amma ace kun barta da miki haka tun safe kuma akan glass cup ace hadda duka, Hanny ta gayamun kin dake ta kuma nima na gani duk jikinta ya fashe" Mik'e wa tae daga zaman datake
"To ubana seka daken ai, nace seka daken, ni yanzu Sufyan ni kakewa magana irin haka acen wancen banzar, yaushe ta juyar mun da kanka har haka? Yaushe ma kai ka isa ka gayamun abinda ya dace ya wanda be dace ba?" Saukar da kanshi yae k'asa
"Mom kiyi hakuri kurun naga an qyale tane acikin jini tun safe shiyasa" tsaki taja tafice daga d'akin gaba daya.
Seda aka bata anti tetanus sannan akae dressing na gun se kuka take, lokacin ne barbo ta tallafeta zuwa d'akin su.
Sun baiwa Ayusher tausayi sosai bako na wasa ba, bataso taga ana cutar da mutane ita kam,amma haka ta gaisa da mutane gidan ta zauna a darare har ya kimtsa suka fita, fitar ba dadi sabida fuskar babu wata walwala haka suka yishi.