Sashe 5
Dabia Ko Halitta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk yadda taso cire komai a ranta ta kasa, gashi ko yunwa bata ji rabon ta da abinci tun rana da sukaci tare da haleemah.
Wata jaka ta ɗauko ta fara duba abin da yake ciki, ganin kayan gyara ne a ciki ta buga tsaki ta tura shi gefe, cikin ranta tana cewa" dama ya lafiyar kura bare taci ɗan mutum hakan ma a rabu ƙalau, yadda kuka kawo haka za kuzo ku ɗauke shirmen KU.... "
Ganin bata da mafita sai kawai ta kunna karatun Al_Qur'ani a wayar ta tasa suratun baƙra Audio Ko Zata samu sassauci zata fara gwada shawarar ƴan uwan maman ta da su zakkiya ta gani dan a baya duk yadda taso da jin karatun ƙur'ani sai kasala da wani abu su rufe ta ko su mantar da ita, yau ko tana tuna hakan taji ta saka har tana saurara.
_Ajmal_
Wayar shi ce ta kama ringing da kamar baze duba me kiran ba sai ya duba yana ganin number ummah yayi ajiyar zuciya ya ɗaga da girmamawa, sai yaji muryar safna.
"hello yaya Ango mun dawo gida fa tun ɗazu waya ta ne babu kati, kuma ummha tace dan Allah ka samu kaci wani abu, ya sameer yace mata baka ci komai ba tun rana, kuma tace ka kula da ƴar mu........" be bari ta firta abin da zata ce ba yayi saurin tsai da ita.
" OK, Naji, sai da safe mai surutu"ya kashe wayar y fara kallon haɗaɗen gadon da aka saka a ɗakin da yake amsa sunan nashi, gashi gadon y sa me shi b a cikin nishaɗi da farin ciki ba, har ji yayi gara ɗakin shi da katifar shi so dubu da haɗaɗen ɗakin da yake ciki a yanzu.
Sosai ya fara tambayar kan shi me ya dace yayi a yanzu ne, sai y tuna da saƙon ummah, yace "dole na miki biyayya kin wuce Kice nayi abu naƙiyi indai har zan iya.
Falo ya koma ya fara duba ledar da su sameer suka ce sun ajiye mai, a dining area...
Wani irin faɗuwar gaba yaji a tare da shi, sakamakon ƙamshin turaren ta da ya kawo mai gulmar ta fito...
Ita ma jin maƙogaron ta ya bushe tace bari ko ruwa ne ta nema ta sha sai ta kwanta tunda kowannen su yasan haɗa su akayi babu wanda ya taɓa ganin kowa dan haka basuyi mamakin rashin gaɗuwar su ba, ta fito daga gefen dining ɗin tana rufe fridge, shi Kuma ya ɗau ledar ze buɗe suka kusan cin karo da juna, atake wani mugun magana ɗisun saƙo ya ziyarci kowannen su, shi kam sai da ya runtse idon shi ma, itama ƙafar ta sai da ta mata nauyi....
Ajmal besan lokacin da ya miƙa mata ladar da take hanun shi ba ba tare da ya buɗe ba, burin shi ta wuce ta bar kusan tar shi, itama da sauri ta karɓa tayi gama kamar wacce taga wani mugun abu, yana jin ta rufo ɗakin yayi kyakyawan ajiyar zuciya, ya bude ledar yaga ashe Leda biyu sameer yayi kowacce Leda kaza da lemu ne acikin kamar yasan za'ayi haka.
Yana ɗauka ya koma ɗaki ya murza ki itama ta murza key,ta koma tana ta ajiyar zuciya, ta bude ledar taga lemu da kaza bayan tasha ruwan ta ɗan sha lemun ta ajiye ta koma bathroom ta watsa ruwa ta zo ta canja kaya ta haye gado tayi addu'a, tana ta sauraron karatun har bacci ya ɗauke ta.
Ajmal ma ganin babu abin da zeci a gidan da yake ji kamar ba nashi ba ya samu ya ɗan ci kazar yana turawa kamar magani, ya haɗa da lemun badan yana jin daɗin su ba ya haye gado yana ta murƙususu.......
_Hajiyar shagali_
"suhail wallahi idan ka sake kaje gidan Jumana wallahi sai ka haɗu da ɓacin rai na, dan naga baka da hankali, kuma jibi zaka bar garin nan ka komai Abuja, ban yadda ka sake zuwa ba sai da izinina" hajiya Uwar Amarya ta firta ga tilon ɗan da ta haifa.
"yanzu mum kina nufin ko na gama karatu wai acan zan cigaba da zama?" suhail y tambaya
"eh haka nake nufi" ta firta mai.
"to saboda me ba akan kula jumana bane ko tausayin ta da nake yi kika ɗauke ni daga gidan ba ko Ince garin ma gaba ɗaya, to ai tabar gidan kuma na kusa kammala karatu na" y bata amsa.
Sosai tayi mamakin kalaman shi Bata taɓa tunanin ze iya firta Mata yasan gudun da take yi ba, ashe yana ankare da komai? Lalai suhail ya fara girma, Amman a fili sai ta kawai da mamakin tace "ni bance maka haka ba in kuma titsiye ni kage to naji duka Sai na amsa maka, kuma haka na baka umarni ka ci gaba da zama a can, ana maka gata baka gani, ga Abuja, wayake ta wani kano?"
"a hakan nake son Kano ai gari ba Kano ba dajin Allah ga mahaifa ta wayake ta kalan dangi" ya bata amsa ya tashi ya tafi fuuuuu.
Tana ta kiran shi be ko saurare ta ba, anan ta fara tunanin lalai suhail ya balaga ya balage tasan me zatayi Kafin yafi ƙarfin ta dan bazata zuba mai ido ba.
_mommah da ummah_
"Hassan ya kuka ga yadda yayan ku ya ƙarɓi Amaryar sa, kuna ganin baze bani matsala ba?"
Mommah ta jefo ma su hussy tambayar da basu tsamace ta ba, dake suna da wayo, kuma basu san abin da ze ba yayan su matsala da sauri hassana tace "ai lafiya lau muka ɓaro shi har abokai suka kawo shi aka watse aka barsu, ya rako mu har mota ma, da alamun fa in sha Allahu....."
"ya isa haka...." mommah ta dakatar da ita a hassale kamar ba ita taso taji yada akayi ba. Wani kallo hussy da hassy suka ma junan su, suka sulale suka gudu ɗaki suna ma yayan su addu'a samun sauƙi a wajen mommah.
09064271655
[08/12, 7:51 am] Maman shaheed😍🥰: *ƊABI'A KO HALITTA*
Free book...
Shafi Na 5
Maman shaheed (Fatima Abubakar)
_Ajmal & jumana_
Washe gari ango da Amarya kowa ya tashi ya gabatar da sallah a makare kowanne ya tashi, dan shi Ajmal rasa maka ma yayi dan besan inda masallaci yake bane da a masallaci zeje yayi sallah, Amman yace dole anjima ya fita ya duba yanayin unguwar.
Jumana ma amakaran ta tashi tayi sallah, ta shiga aikin tunanin makomar Auren ta da irin rayuwar da zasuyi da wanan bawan Allah da suka kasa kallon juna.
Bayan Ajmal y fito daga wanka ya shirya, ya cigaba da zaman ɗaki, da yaji alamun yunwa ya ɗauko ragowar kazar shi ya cinye ya kora da ruwa da lemu dan yasan babu t inda ze samu abin kari.
Jumana ma hakan take, a tunanin ta inta sarrafa wani abun ma ba lalai yaci ba kuma ita dan dai cikin ta ko haka zata iya zama, sai d taji azabar ƙugin da cikin ta yake ta rasa yadda zatayi gashi da abu mai zafi ta saba karyawa irin su tea Ko kunu first Kafin taci Komai, ledar kazar ta ɗauko ta bude taga bazata iya ci ba dama da zafi ne, sai ta ajiye ta koma ta kwanta tana ta lissafin dokin Rano, Ganin yunwar ba ƙanwar uwata bace basu haɗa dangi na kusa ko na nesa ba gashi yunwa bata san taurin kai ba dole ta sakko ta fara shirin leƙa falo don ta lalubo kitchen taga me Zata iya sarafawa.
Da sanɗa ta buɗe ƙofar, yaji buɗe ƙofar ta Sai yayi wani guntun tsakanin yana ganin duk an cuce su ita a takure shima a takure.
Ko da ta fara dube dube ta hango kitchen a gefen dining da saɗan ta tafi ta ɓuɗe ta shiga tana sauke ajiyar zuciya kamar mara gaskia.
Gas ta fara kunawa taga Anyi refilling ɗin Shi ajiyar zuciya ta sauke, ta samo bottle Wata ta kunna gas ɗin ta juye a ƙaramar nonstick pot ta ɗora a wuta ta nemo kofi tana jira yayi zafi ta juye, sai ta hango oven tayi tunanin gasa kazar ta, ta tafi ta ɗauko ta zo ta kunna tasa kazar dan ta dumama, sosai kitchen ɗin ta ƴa haɗu Amman ba shine a gaban ta ba ko bi ta kayan da aka loda a kitchen ɗin batayi ba burin ta ma ta bar kitchen ɗin.
Bayan ta juye ruwan zafin a cup Sai ta fara zare ido tana neman kayan shayi kamar ta ajiye, ta dinga lalube bata gani ba ranta kawai sai taji ya ɓaci, har ta haƙura ta ɗauki kazar Zata tafi, sai taga Leda da abu aciki akan dining, Sai taji zuciyar ta na mata umarnin ta ɓuɗe daga meye aciki, har zata ƙi bin umarnin zuciyar Sai da ta buɗe, tana buɗewa tayi e eyes da gwangwanin millo batasan lokacin da murmushin ganin mutumin ya kubce Mata ba, ba tare da ta sani ba, dan tun da aka fara bikin ta shine murmushin ta na farko ganin kayan shayi, bata tsaya wata wata ba ta suri ledar kamar Tata takai ɗaki ta ajiye da kazar hanun ta, ta dawo ta sake ɗaukan ruwan zafin ta, ta fice a kitchen, ta tafi ɗaki ta murza key ta baje a ƙasa ta fara haɗa tea Jikin ta Har rawa yake dake tana da Ulcer, dan sai da ta fara Afa madarar ma tunda Bata da magani a kusa dan kamar Ulcer nason tashi ma dan taji yunwa ba kaɗan ba.
Ajmal Najin ta koma shima ya fito, ya ɗauki ruwa har ce wuce ya leƙa kitchen Yana tunanin Uwar me zeyi ma a kitchen ɗin, makulin Gidan ya ɗauka da Sameer ya bashi dama a falo ya ajiye bayan y kulle gidan jiya, fita yayi y buɗe yace bari ya zaga yaga inda masalin unguwar yake ko ze samu sanyi ya ratsa shi in y bar gidan ma.
Jumana kuwa sai da ta ƙoshi sanan ta maida kayan gefe, ta koma kogin tunani kuma, tana cikin haka taji saƙo ya shigo wayar ta, da kamar bazata kula ba sai ta ɗauko, ta duba taga haly ce ta turo mata da saƙon
Wata jaka ta ɗauko ta fara duba abin da yake ciki, ganin kayan gyara ne a ciki ta buga tsaki ta tura shi gefe, cikin ranta tana cewa" dama ya lafiyar kura bare taci ɗan mutum hakan ma a rabu ƙalau, yadda kuka kawo haka za kuzo ku ɗauke shirmen KU.... "
Ganin bata da mafita sai kawai ta kunna karatun Al_Qur'ani a wayar ta tasa suratun baƙra Audio Ko Zata samu sassauci zata fara gwada shawarar ƴan uwan maman ta da su zakkiya ta gani dan a baya duk yadda taso da jin karatun ƙur'ani sai kasala da wani abu su rufe ta ko su mantar da ita, yau ko tana tuna hakan taji ta saka har tana saurara.
_Ajmal_
Wayar shi ce ta kama ringing da kamar baze duba me kiran ba sai ya duba yana ganin number ummah yayi ajiyar zuciya ya ɗaga da girmamawa, sai yaji muryar safna.
"hello yaya Ango mun dawo gida fa tun ɗazu waya ta ne babu kati, kuma ummha tace dan Allah ka samu kaci wani abu, ya sameer yace mata baka ci komai ba tun rana, kuma tace ka kula da ƴar mu........" be bari ta firta abin da zata ce ba yayi saurin tsai da ita.
" OK, Naji, sai da safe mai surutu"ya kashe wayar y fara kallon haɗaɗen gadon da aka saka a ɗakin da yake amsa sunan nashi, gashi gadon y sa me shi b a cikin nishaɗi da farin ciki ba, har ji yayi gara ɗakin shi da katifar shi so dubu da haɗaɗen ɗakin da yake ciki a yanzu.
Sosai ya fara tambayar kan shi me ya dace yayi a yanzu ne, sai y tuna da saƙon ummah, yace "dole na miki biyayya kin wuce Kice nayi abu naƙiyi indai har zan iya.
Falo ya koma ya fara duba ledar da su sameer suka ce sun ajiye mai, a dining area...
Wani irin faɗuwar gaba yaji a tare da shi, sakamakon ƙamshin turaren ta da ya kawo mai gulmar ta fito...
Ita ma jin maƙogaron ta ya bushe tace bari ko ruwa ne ta nema ta sha sai ta kwanta tunda kowannen su yasan haɗa su akayi babu wanda ya taɓa ganin kowa dan haka basuyi mamakin rashin gaɗuwar su ba, ta fito daga gefen dining ɗin tana rufe fridge, shi Kuma ya ɗau ledar ze buɗe suka kusan cin karo da juna, atake wani mugun magana ɗisun saƙo ya ziyarci kowannen su, shi kam sai da ya runtse idon shi ma, itama ƙafar ta sai da ta mata nauyi....
Ajmal besan lokacin da ya miƙa mata ladar da take hanun shi ba ba tare da ya buɗe ba, burin shi ta wuce ta bar kusan tar shi, itama da sauri ta karɓa tayi gama kamar wacce taga wani mugun abu, yana jin ta rufo ɗakin yayi kyakyawan ajiyar zuciya, ya bude ledar yaga ashe Leda biyu sameer yayi kowacce Leda kaza da lemu ne acikin kamar yasan za'ayi haka.
Yana ɗauka ya koma ɗaki ya murza ki itama ta murza key,ta koma tana ta ajiyar zuciya, ta bude ledar taga lemu da kaza bayan tasha ruwan ta ɗan sha lemun ta ajiye ta koma bathroom ta watsa ruwa ta zo ta canja kaya ta haye gado tayi addu'a, tana ta sauraron karatun har bacci ya ɗauke ta.
Ajmal ma ganin babu abin da zeci a gidan da yake ji kamar ba nashi ba ya samu ya ɗan ci kazar yana turawa kamar magani, ya haɗa da lemun badan yana jin daɗin su ba ya haye gado yana ta murƙususu.......
_Hajiyar shagali_
"suhail wallahi idan ka sake kaje gidan Jumana wallahi sai ka haɗu da ɓacin rai na, dan naga baka da hankali, kuma jibi zaka bar garin nan ka komai Abuja, ban yadda ka sake zuwa ba sai da izinina" hajiya Uwar Amarya ta firta ga tilon ɗan da ta haifa.
"yanzu mum kina nufin ko na gama karatu wai acan zan cigaba da zama?" suhail y tambaya
"eh haka nake nufi" ta firta mai.
"to saboda me ba akan kula jumana bane ko tausayin ta da nake yi kika ɗauke ni daga gidan ba ko Ince garin ma gaba ɗaya, to ai tabar gidan kuma na kusa kammala karatu na" y bata amsa.
Sosai tayi mamakin kalaman shi Bata taɓa tunanin ze iya firta Mata yasan gudun da take yi ba, ashe yana ankare da komai? Lalai suhail ya fara girma, Amman a fili sai ta kawai da mamakin tace "ni bance maka haka ba in kuma titsiye ni kage to naji duka Sai na amsa maka, kuma haka na baka umarni ka ci gaba da zama a can, ana maka gata baka gani, ga Abuja, wayake ta wani kano?"
"a hakan nake son Kano ai gari ba Kano ba dajin Allah ga mahaifa ta wayake ta kalan dangi" ya bata amsa ya tashi ya tafi fuuuuu.
Tana ta kiran shi be ko saurare ta ba, anan ta fara tunanin lalai suhail ya balaga ya balage tasan me zatayi Kafin yafi ƙarfin ta dan bazata zuba mai ido ba.
_mommah da ummah_
"Hassan ya kuka ga yadda yayan ku ya ƙarɓi Amaryar sa, kuna ganin baze bani matsala ba?"
Mommah ta jefo ma su hussy tambayar da basu tsamace ta ba, dake suna da wayo, kuma basu san abin da ze ba yayan su matsala da sauri hassana tace "ai lafiya lau muka ɓaro shi har abokai suka kawo shi aka watse aka barsu, ya rako mu har mota ma, da alamun fa in sha Allahu....."
"ya isa haka...." mommah ta dakatar da ita a hassale kamar ba ita taso taji yada akayi ba. Wani kallo hussy da hassy suka ma junan su, suka sulale suka gudu ɗaki suna ma yayan su addu'a samun sauƙi a wajen mommah.
09064271655
[08/12, 7:51 am] Maman shaheed😍🥰: *ƊABI'A KO HALITTA*
Free book...
Shafi Na 5
Maman shaheed (Fatima Abubakar)
_Ajmal & jumana_
Washe gari ango da Amarya kowa ya tashi ya gabatar da sallah a makare kowanne ya tashi, dan shi Ajmal rasa maka ma yayi dan besan inda masallaci yake bane da a masallaci zeje yayi sallah, Amman yace dole anjima ya fita ya duba yanayin unguwar.
Jumana ma amakaran ta tashi tayi sallah, ta shiga aikin tunanin makomar Auren ta da irin rayuwar da zasuyi da wanan bawan Allah da suka kasa kallon juna.
Bayan Ajmal y fito daga wanka ya shirya, ya cigaba da zaman ɗaki, da yaji alamun yunwa ya ɗauko ragowar kazar shi ya cinye ya kora da ruwa da lemu dan yasan babu t inda ze samu abin kari.
Jumana ma hakan take, a tunanin ta inta sarrafa wani abun ma ba lalai yaci ba kuma ita dan dai cikin ta ko haka zata iya zama, sai d taji azabar ƙugin da cikin ta yake ta rasa yadda zatayi gashi da abu mai zafi ta saba karyawa irin su tea Ko kunu first Kafin taci Komai, ledar kazar ta ɗauko ta bude taga bazata iya ci ba dama da zafi ne, sai ta ajiye ta koma ta kwanta tana ta lissafin dokin Rano, Ganin yunwar ba ƙanwar uwata bace basu haɗa dangi na kusa ko na nesa ba gashi yunwa bata san taurin kai ba dole ta sakko ta fara shirin leƙa falo don ta lalubo kitchen taga me Zata iya sarafawa.
Da sanɗa ta buɗe ƙofar, yaji buɗe ƙofar ta Sai yayi wani guntun tsakanin yana ganin duk an cuce su ita a takure shima a takure.
Ko da ta fara dube dube ta hango kitchen a gefen dining da saɗan ta tafi ta ɓuɗe ta shiga tana sauke ajiyar zuciya kamar mara gaskia.
Gas ta fara kunawa taga Anyi refilling ɗin Shi ajiyar zuciya ta sauke, ta samo bottle Wata ta kunna gas ɗin ta juye a ƙaramar nonstick pot ta ɗora a wuta ta nemo kofi tana jira yayi zafi ta juye, sai ta hango oven tayi tunanin gasa kazar ta, ta tafi ta ɗauko ta zo ta kunna tasa kazar dan ta dumama, sosai kitchen ɗin ta ƴa haɗu Amman ba shine a gaban ta ba ko bi ta kayan da aka loda a kitchen ɗin batayi ba burin ta ma ta bar kitchen ɗin.
Bayan ta juye ruwan zafin a cup Sai ta fara zare ido tana neman kayan shayi kamar ta ajiye, ta dinga lalube bata gani ba ranta kawai sai taji ya ɓaci, har ta haƙura ta ɗauki kazar Zata tafi, sai taga Leda da abu aciki akan dining, Sai taji zuciyar ta na mata umarnin ta ɓuɗe daga meye aciki, har zata ƙi bin umarnin zuciyar Sai da ta buɗe, tana buɗewa tayi e eyes da gwangwanin millo batasan lokacin da murmushin ganin mutumin ya kubce Mata ba, ba tare da ta sani ba, dan tun da aka fara bikin ta shine murmushin ta na farko ganin kayan shayi, bata tsaya wata wata ba ta suri ledar kamar Tata takai ɗaki ta ajiye da kazar hanun ta, ta dawo ta sake ɗaukan ruwan zafin ta, ta fice a kitchen, ta tafi ɗaki ta murza key ta baje a ƙasa ta fara haɗa tea Jikin ta Har rawa yake dake tana da Ulcer, dan sai da ta fara Afa madarar ma tunda Bata da magani a kusa dan kamar Ulcer nason tashi ma dan taji yunwa ba kaɗan ba.
Ajmal Najin ta koma shima ya fito, ya ɗauki ruwa har ce wuce ya leƙa kitchen Yana tunanin Uwar me zeyi ma a kitchen ɗin, makulin Gidan ya ɗauka da Sameer ya bashi dama a falo ya ajiye bayan y kulle gidan jiya, fita yayi y buɗe yace bari ya zaga yaga inda masalin unguwar yake ko ze samu sanyi ya ratsa shi in y bar gidan ma.
Jumana kuwa sai da ta ƙoshi sanan ta maida kayan gefe, ta koma kogin tunani kuma, tana cikin haka taji saƙo ya shigo wayar ta, da kamar bazata kula ba sai ta ɗauko, ta duba taga haly ce ta turo mata da saƙon