← Book details Burinah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 39

Sashe 36

Burinah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kuka take tasake qanqameshi, Shima kansa kuka zuci yake, Yama rasa wacce kalmar zaiyi amfani da ita wajan rarrashin ta
Kamota yayi suka futo falon, yace Dan Allah baby kiyimin alqawarin zaki kulamin da kanki da baby na, kidinga cin abinci sosai, karkibar babynmu da yunwa
Duk abinda kike buqata kifadawa doctor's dinnan zasuyi miki, akwai me aiki dazata fara zuwa anjima
Ban yarda ki dauke ko tsinke ba
Duk abinda baiyi miki ba
Kawai kisanar Dani tawaya
Yana fadar haka wani irin kuka yazo masa kusa, wani qullulun baqin ciki ya tokare masa wuya
Cikin sauri yajuya yabar falon yana goge hawayen idonsa yafita harabar gidan yashiga Mota suka wuce airport
Kan kujera tafada tasaki wani irin kuka mai ciwo, sai yau taji ta tsani mulki a rayuwar ta
Gashi asadinsa anrabata da daddynta
Kuka take sosai, cikin sauri daya daga cikin doctor me kula da ita tafuto daga Dakin dayake kusa dana Amal ta janyo ta jikinta tana aikin rarrashin ta, cikin harshan turanci
*** **** ***
Tunda daddy yatafi tazama wata irin shiru shiru, Bata magana sosai, kullum cikin tunanin sa take, abinda yake hanata shiga damuwa daya ne yanda zai Bata tsawon lokaci yakirata awaya suyi ta waya yana sakata daria
Saikuma video call a computer daya zama qa'ida kowanne dare, harta saba kullum yakira waya saita dage rigar ta ta nuna masa cikin yagani, banda ruwan pictures datakeyi tana tura masa
Gaba daya ta kumbura, cikin jikinta daya cika wata biyar yayi wani irin girma, abin har tsoro yake Bata, saboda ba haka take ganin na sauran mata masu ciki ba
Duk ranar Allah Sai doctor ta matsa mata kafarta saboda yanda suka kumbura
Haka doctor zata Sata agaba suyi ta zagaye gidan, saita gaji ne sannan zasu dawo ciki
Batta da aiki Sai shan fruit, kullum shine take wuni tanaci, batada damuwar komai banda rashin ganin mijinta
Idan ta zauna afalo anan take wuni, saboda cikin nauyin sa yafi karfin ta, wani lokacin tayi sallah a zaune, wataran kuma idan tanajin dama dama tayi yanda tasaba
Taqara wani irin kyau jikinta yayi bulbul ta murje, Taqara zama yar hutu kamar ka latsa jikinta jini yafuto
A bangaren daddy kuwa yafita zumudin San ganinta, so yake kawai Rana daya yayi Mata zuwan bazata, ayyukan gabansa yake burin yaga yayi sosai, yanda dazaran ya ware wajan babynsa babu me nemansa
Mrs Usman ce
BURINAH
(A Romantic love story)
Writing by Amnah El yaqoub
Bismillahir-rahmanirraheem
Second to the last page
Fiancee banga perfume din danake using dashi ba Ina kika sakamin shi?

Dawowa tayi kusa dashi tace wallahi yana cikin kayana fiance, qamshin nakeso, shiyasa na sakashi cikin kayana Dan su dinga yin qamshin turaren
cikin rashin damuwa yace ok bari nayi amfani da wannan
Yasa hannu yadauki wani yana fesawa
Haka ya budawa jikinsa turare kamar sabon ango
Cikin dauria ta to she hancinta, tana turashi gaba
Da mamaki ya kalleta yace lafiya?

Cikin to she hanci tace bansan wannan qamshin turaren fice daga Dakin nan
Jikinsa ne yayi sanyi yazuba mata kyawawan idonsa yana Kallanta
Cikin sauri ya matso kusa da ita yace lafiya kike kuwa?

Jin qamshin akusa da ita ne yasa cikin azama ta tureshi tayi cikin toilet da gudu tana kwara Amai
Bin jikinsa yayi da kallo yana janyo rigar jikinsa yana shaqar qamshin turaren
Yarasa me taji dahar zaisa ta yin Amai
Ahankali ya zare rigar daga jikinsa yakasan ce dagashi sai dogon wando da farar vest ajikin farar fatar sa
Toilet din yabita, yakamata ya riqeta saida ta gama sannan ya wanke mata Bakinta da fuskar ta, yariqota yanayi mata sannu suka dawo Cikin Dakin
Ajiyar zuciya take ita kadai?

Shahid yace sannu
Bata iya bashi amsaba illa daga masa Kai datayi
Yace meyake damun kine?

Tace babu komai fiance
Yace no, tashi muje asbiti
Tace da gaske nake, Babu abinda nakeji, kawai qamshin wannan turaren daka fesa ne banaso
Kin tabbatar babu abinda yake damunki?

Babu komai fiance
Yace ok
Tashi yayi yacire wandon Jikin nasa yasauya wasu kayan, zuwa kalar brown manyan kaya, yabude cikin kayanta yadauko turaren data dauke
Yafesa sannan yaje kusa da ita yace wannan yayi ko?

Ahankali ta tashi ta rungume shi, tana shaqar qamshin turaren
Shide Shahid yana tsaye mamaki yana neman kashe shi
Ahankali yasa hannu ya rungume ta, suna tsaye ahaka har tsawon wani lokaci sannan yajata zuwa gadon yace ki kwanta ki huta to Nima zanje office
Riqeshi tayi tace ni inasan wannan qamshin please karka tafi
Babu yanda ya iya haka ya zauna agefenta, yana shafa Fuskarta
Ahankali bacci me nauyi yadauke ta
Tashi yayi ya kunna mata esi ya rufeta da blanket sannan yafice zuwa wajan aiki
*** *** ***
Yau tunda safe tatashi tashirya, da kanta tashirya Dakinta, taci kwalliyar ta cikin doguwar Riga ta atamfa
Bawani daurin wahala tayi akanta ba, me sauqi tayi
Ta feshe jikinta da turare
Tafuto falo ta ganshi tsaf agyare
Abinci tazuba me mugun yawa, ta cinye shi tsaf
Zuwa yanzu harta saba da mugun cin abinci kamar yan kwallo
Kuma hakan bazai Hana anjima taci wani abincin ba
Tana gamawa ta dauki Wayarta zata kira daddy kawai kuma saita fasa
Takira maisah
Tana shiga maisah ta daga Kiran daga bangaren ta
Tace Allah Sarki yar'uwata yanzu nake cewa bari inkira me cikin nan inji Yaya take da cikin jikinta
Amal tace kede bari maisah wallahi nagaji da wannan Zaman
Jira nake wani yazo daga gida wallahi kafata kafarsa zan biyoshi mutaho gida
Nagaji
Maisah tace haba me ciki kwana nawa nema yarage
Cikin sauri Amal tace kede bazaki dena fadamin wannan sunan ba, kedinma kwana nawane kin samu naki
Ajiyar zuciya maisah tayi tace albishirinki, ai yanzu ma inada abina harna wata daya
Gani ya sham dina yana tattalina dana babynsa
Amal tace Karde ki fadamin magana wallahi, kinsan cewa Badan matsalar dana samu kwanaki Akan cikina ba, Babu abinda zai rabani da daddy nah
Kuma yanzu ma jira nake yazo, wallahi Dani zai koma
Maisah tace kinga ni wasa nake miki, garama de ki biyo abinki kudawo gida adora daga inda aka tsaya
Daria Amal Tasa tace kinga ni Sai anjima tun kafin ki fara shaqiyancin naki, Allah yarabamu da wannan abin lafiya, maisah tace to amin
*** *** ***
Tun dazu yake tsaye a kofar kitchen din yana Kallanta tana aikinta cikin nutsuwa
Juyowar dazatai Sai ganin mutum tayi
Dasauri ta dora Hannunta Akan Kirjinta, tace oh wallahi harka tsorata ni
Shigowa cikin kitchen din yayi yana rungumota jikinsa yace sorry fiancee
Jug ta meqo masa cike kunun madara da kwakwa tace ungo kaimin wannan dining
Babu musu ya karba yakai, yadawo kitchen din yace Dame zan tayaki?

Albasa ta bashi da wuqa tace ungo yankamin wannan qanana
Karba yayi yafara yankawa, yanayi Idanu yana cikowa da hawaye
Qanshin albasar dataji ne yasa nan take wani irin Amai yataso mata, cikin sauri tayi waje da gudu
Kallan mamaki yabita dashi, sannan ya ajiye wuqar hannun sa ya wanke hannun yabi bayanta
Lokacin daya shiga Dakin harta gama tafuto daga toilet tana goge Fuskarta da towel
Baice mata komai ba, yadauko mata after dress ta dora Akan kayan jikinta yabata dankwalin abayar tayi rolling, suka kama hanyar fita waje
Suna Zuwa harabar gidan, yayi saurin Bude mata gaban motar tashiga, yazagayo yashiga yajasu Sai hospital
*** *** ***
To babana harka shirya ne haka da wuri?karfe takwas fa yanzu
Kansa ya Sosa, yayi masifar kyau cikin farin yadin da aka yiwa ado da ash din zare
Babbar rigar ta karbi jikinsa
Hular kansa kala daya da takalmin kafarsa, sai tashin qamshi yake kamar wanda zaije wajan daurin aurensa
Yace momy ai gara inbi flight din dazai tashi da wuri
Tace to ai ka tsaya kayi break ko
Agogon dake daure a tsintsiyar hannun sa ya kalla
Yace ai momy babu damuwa idan naje can sainaci
Kallan mamaki momy tayi masa tace, kace baka sanar da ita zakaje ba, tayaya zakayi maganar zakaci abinci idan kaje
Kaga muje Kaci abinci saika wuce
Babu yanda ya iya haka ya wuce dining yaci abincin kadan, momy tatashi ta dauko masa wata Leda tace gashi to saika Kai mata
Ai bazaku wuce sati biyu ba zaku dawo gaba dayanku ko?

Fuskar sa yashafa yace eto gamu nande momy, da inaso mu wuce Saudia ne daga can
Momy tace banasan shirme daddy, yarinyar da tsohon ciki zaka Diba kuyita tafiya yawo?

Kabari idan Allah yadauke ta lafiya saikuje
Yace to momy saikun ganmu, kifadawa Abba idan yafuto nawuce
Cikin ranta tace yauga zumudi lale
Afili tace to zaiji, Allah yakaiku lafiya
*** *** ***
Doctor ya dubesu yace inajin ku meke tafe daku?

Shahid yace wallahi narasa gane kanta ne doctor, yau tace batasan qamshin wannan Abu, gobe tace batasan qamshin wannan
Hartakai yau Albasa wannan da ake abinci da ita dagajin qamshin ta tafara Amai
Nace mata muje asbiti tace a a lafiya kalau take, shine nace yau de bari nakawo ta aduba ta agani ko batada lafiya ne?

Murmushi doctor din yayi yace Toshiknn bari Akira nurse tazo suje ayi mata text
Babu Bata lokaci nurse din tazo, sukaje akayi mata gwajin fitsari dana jini
Basufi minti talatin ba, likita ya baiyana musu cewa tana dauke da ciki tsawon wata biyu
Nan take farin ciki yakamasu gaba dayansu
Shahid yadaga hannu sama yana zubawa Allah godia
Haka suka taho gida cikin tsananin murna
Suna qarasawa gida shahida tayi hanyar kitchen, cikin sauri yace fiancee me zakiyi?
Chapter 36 · 0% Book details