← Book details Burinah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 39

Sashe 12

Burinah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kafin ta bashi amsa aka qwanqwasa Dakin
Dan haka tace yayanah Ina zuwa zan kiraka, tana kashe wayar itama tana turo Dakin tana shigowa
Ajiye wayar tayi, ta miqe tsaye, ta zuba mata ido, Riga da wando ne de ajikinta kamar kullum
Tana yatsina tace sannu ko
Amal data gama gane yarinyar batada mutunci Kai tsaye tace yauwa
Zaki futo ki gaisa da qwayena suna falo, tana gama fadar haka tafi ce,
Afili Amal tace yarinyar nan yar renin wayo ce
Dan kwalin ta ta yafa akanta tafice zuwa falon
Tana fita su nusy suka kwashe da dariya harda nunata da hannu
Kallan jikinta Amal tayi, tana neman makusa ajikinta
Sukuwa suka miqe suna cigaba da daria, shahida tace jiwata shiga Dan Allah yar qauyen qauyawa, kidahuma dake waike kinzo amatsayin matar yayanah ko
Nunata tayi da hannu tace Dan Allah kiduba kuga wadda takesan zama new first lady in bauchi state
Taqarasa maganar tare da dungure mata Kai, har Dan kwalinta yafadi
Hakan ne yayi Sanadin baiyanar dogon gashin kanta
Gaba dayansu suka hada wajan fadin attached?

Shahida tace au kina nufin da wannan abin zaki yaudari yayanah?

Nusy bani Reza
Aikuwa tana Bata ta nufi gashin Amal gadan gadan, ta riqe shi zata yanke, bige mata hannunta Amal din tayi
Amma ko gizau shahida batayiba
Ganin haka yasa Amal dukan hannun shahida, suma su nusy suna ganin haka suka rirriqe Amal
Shahida zata dora rezar akanta, Amal tafara ihun kuka, saboda sarkin yawa yafi sarkin qarfi
Ku qyaleni!
ku rabu Dani nace!
da karfinta take fadar haka
Shahida takama gashi ta riqe, Amal tana qoqarin qwatar kanta har suka yanketa a hannunta
kamar wasa yaji ihu aqasa
Kuma kamar fada ake
Tashi yayi, dagashi sai wando ajikinsa three quarter, baqi Sai Riga yar qarama data kama jikinsa, dantsan hannun sa sun futo sosai
Saboda yana hutawa ne
Dasauri yasakko qasa, cikin tsawa yace ke shahida!!!!

Dasauri suka saki Amal, tana kuka tana yarfe hannunta inda suka yanketa
Wani mugun kallo yamusu baice musu uffan ba, suka fice cikin sauri
Kallan sa yakai kanta, ahankali ya tsugunna dede inda take zaune tana kuka, yazubawa gashin kanta daya barbaje ido, dama wannan yarinyar gashin tane haka?

To Amma de duk yanda akai sudin ba Yan nigeria bane
Hannunta ta rufe da dankwalinta dede inda yake jinin
Cikin kuka tace masa Dan Allah na roqeka, idan Kaci zaben kasauwaqe min, inje in auri Yaya Shahid
Ni bazan iyaba
Kallanta yake shi har yanzu mamakin gashin kanta bai sake Shiba
Cikin ransa yace SHAHID
Mrs Usman ce
BURINAH
(A Romantic love story)
Writing by Amnah El yaqoub
Bismillahir-rahmanirraheem
Yanzu wannan yarinyar har tasan soyaiya?

Dududu ma nawa take?

Yar qarama da ita har tasan asaketa ta auri wani?

Waye wannan Yaron?

Waye shi?

Hake yake fada cikin ransa, yayinda azahiri ya kafeta da idanunsa
Tashi yayi yabar ta awajan, yahaura sama
Tana ganin tashin sa tabishi da harara, tashige dakinta da gudu tafada kan gado tasaki wani malalacin kuka
Itada ko malami ne yadaketa a makaranta yayanta da mahaifinta basa zama Sai sun rama mata itace wata yarinya da aqalla Bata wuce sa'arta ba ta yanka da Reza
Yana shiga dakinsa yafada kan gado tareda hargitsa sumar kansa, shifa bayasan damuwa, gashi tun ba'a je ko'Inaba yarinyar nan tafara haddasa masa husuma
Tana daki tana bawa kanta hakuri tare da goge hawayen idonta, taji anbude kofa
Qin dagowa tayi bare ta kalleshi
Tsayawa yayi akanta, yana Kallanta, tayi rub da ciki, gashin kanta yabazu Akan gadon kamar wata aljana
Matsawa yayi dede inda take, yakai hannu zai tabata saiya fasa
Yasake Kai hannu akaro Nabiyu, Shima yafasa
Sai akaro na ukun ne yafizgi hannun nata da karfi
Batasan lokacin datasa qara ba wayyo baba wayyo Yaya Shahid
Ko kulata baiyi ba, ya tsugunna yafara treatment din hannun nata
Kanta ta sunkuyar saboda azabar datake ji, hakan datayi ne yabawa gashin kanta damar rufewa daddy fuska
Dago kansa yayi yana Kallanta, gashin ya zubawa ido, kamar bazai taba ba, saikuma yasa hannun yakawar dashi, yaci gaba da wanke mata wajan
Hannun ya kalla fari tas dashi, farcen ta gwanin sha'awa
Ahankali itama ta Dago da kanta, tana kallan yanda yake aikin
Ta shagala a kallansa, Sarai yasan kallansa take shiyasa yaqara tamke fuskar sa
Yana gamawa yasaki hannun, yafice yabar Dakin
Ita kuwa da idanu ta bishi, mayar da gashin ta baya tayi, ta kalli Dan yatsanta inda yaduba, ta kwanta awajan bacci me nauyi yadauketa
*** *** ***
Amma Lalle yarinyar nan, jibafa yar qarama da ita har tasan duniya, shahida tace shiyasa nace muku bansan zuwa gidan, Dan zuciya ta zafi take, zatasa inyi abinda banyi niyyaba
Nusy tace to kiyi hakuri Kawai ai akwai wani lokacin saimun nuna mata ita yar qaramin matsiyaci ce
Dahaka sukai sallama, tatafi gida
*** *** ***
Sai magrib na farka daga baccin danake, ahankali natashi nacire kayana, har banasan dungurar wajan da aka yanka ni, towel na daura nashiga toilet
Nayi wanka, sai dangale hannun nake, da hannu daya nashafa mai na janyo doguwar rigar material acikin kayana mai launin blue, tayi kyau sosai, nasaka, da hannu na mai ciwon nadanne Bayan rigar, marar ciwon kuma Naja zif narufe bayana
Ko falon ban komaba, Naja wayata nakira maisah, nabata labarin abinda qanwar daddy tayimin
Rumaisa tace subhanallah, Amma wannan yarinyar batada mutunci, kiyi hakuri Amal, komai lokaci ne
Maisah wallahi baba zan fadawa yazo yadaukeni ni bazan iyaba maisah, wannan jaraba har Ina,
A a Amal, kinsan halin baba, abinda zaiyi kowa ba zaiji dadi ba, kiyi hakuri, kiyiwa mijin ki biyaiya, ayanxu aljannarki kike nema awajansa, ita qanwar sa ba aurenta kikeba, shi kike aure
Nace hakane, nan nabata labarin anty mufy, maisah tace kinji ba, tunda kikaji yar'uwarsa tace haka yake, to kiyi masa uzuri, idan abin maganar yakamaki ke kiyi masa kece aqasan sa
Nace to maisah nagode
Nabawa Yaya sham latter ki Amal, yayi ta kuka, kamar ba namiji ba, ni har yabani kunya ma, nace Allah Sarki Yaya sham, yasoni maisah, tace hakane, Allah yasa hakane yafi alkhairi nace amin
*** *** ***
Momy cikina ciwo, subhanallah Wai shahida har yanzu baki dena wannan ciwon marar ba?

Kai ta daga mata alamar eh
To sannu bari Akira likita, Bayan takira doctor yazo yadubata yabata magani tasha, yace hajiya idan bataji Dan sauqi ba atafi da ita hospital
Godia momy juwairah tayi masa yajuya yatafi
Kamar wasa taji sauqi, harma tafara hada kayanta, saboda gobe takesan komawa, momy tace haba shahida kibari kiji sauqi mana, saiki koma ko zuwa next week ne
Lalle momy Ina zan iya zama banje Naga shahid ba,
Afili kuwa saitace momy karki damu, ai naji sauqi
Momy tace Toshiknn
Kalau suka kwanta, tanata murna gobe zataje taga Shahid
1:00am ciwon nata yadawo, marar ta ta riqe har batasan tayi motsi
Haka tahanasu bacci Babu yanda momy ta'iya dole Sai asbiti suka tafi
Kamar wasa yana kwance yana bacci momy ta kirashi tafada masa halin dasuke ciki
Dasauri yasa jallabiyarsa, yahau Mota yafita, yana zuwa asbitin alokacin harta Samu bacci Bayan alluran datasha
Momy yajikin nata?

Da sauqi daddy, Abba ku yafita dazu shiyasa nakiraka, bari in shiga toilet zanyi sallah
Yace to momy
Gadon ya qarasa yana Kallanta, aransa yace marar ji kawai
Yana kallan Dakin dasuke kamar wasa yaji tana cewa Shahid...

Shahid...

Idanunta arufe da alama nafarki take, Kallanta yasake yi
Aransa yace SHAHID again?
*** *** ***
After 2 week's
Haka Zaman su Amal yakasan ce, daddy baya nemanta, itama haka
Babu wanda yake shiga sabgar dan'uwansa
Shi kullum babu fara'ah fuska a daure
Bata kula shi, ko taji motsinsa banza take dashi, saide abinda takasa ganewa shine, kullum saiya shiga Dakin dayake kusa danata
Tarasa me yake yi adakin tunda shide dakinsa asama yake
A bangaren daddy kuwa shi shaf ma yamanta da ita
Siyasar datake qara matsowa itace aransa
*** *** ***
Kwalliya akeci tagani tafada, jamcy tace qawata Sai Ina haka?

Fari tayi da idonta tace Sai wajan Shahid na shahida
Zanje mufita ko shan ice cream ne
Kallan agogo tayi tace Amma shahida yanzu karfe tara fa, kina ganin zaki iya Jan hankalin sa har kuje tare?

Karki damu jamcy, tana fadar haka tadau Jakarta tafi ce
Bata zarce ko Inaba Sai gidansu Shahid
Suna falo suna kallo dukansu, tayi sallama tare da shiga falon, Nazy da okasha suka tashi suka bar musu wajan
Cikin ransa yace wannan yarinyar badai naci ba
Akusa dashi ta zauna tace um Shahid nace Dan Allah ko zaka shirya muje musha ice cream?

Kallanta yayi da mamaki baisan lokacin dayace
"shahida yaushe nafara magana dake mai tsawo dahar zan debi kafa nafita tare dake?

"
Maimakon tayi fishi saitayi murmushi tace Shahid yau wacce Rana kakira sunana?

Tafe kansa yayi da hannun sa, yace Dan Allah kifita daga gidan nan, bazaki gane yanda zuciyata take zafi ba idan naganki, banasanki shahida
Akwai wadda nakeso
Hawaye ne suka wanke mata fuska, cikin kuka ta tsugunna qasa tace Shahid Ina sanka
Cikin zafi yace nikuma Bana sanki
Kafafunsa takama ta riqe, yafizge kafarsa, tareda Kai hannu zai dauketa da mari
Okasha ne yafuto Dasauri, wanda yaji suna rikici cikin daga murya, hakanne yasashi futowa
Yace haba Shahid?

Dukan mace?

Yadubi shahida yace shahida tashi ki tafi, insha Allah komai zaiyi normal kinji?

Kai ta daga masa tana goge hawayen idonta
Tana fita okasha yace abokina meyayi zafi haka?

Yarinyar nan tana sanka, koyayane kadinga kulata zataji dadi, be kamata irin haka yadinga shiga tsakanin Kuba
Okasha nafada mata banasanta, Bana Santa okasha, Yaya take so namata?

Har wannan yarinyar ce zatasa hannu tace zata riqeni?

Nawa ma take, Amma har tasan tana taba Jikin maza
Ahakan zan sota in aure ta?

Okasha ya kalleshi yace Amma na tabbatar ayanda kake bamu labarin Amal, abinda yafi riqewa ma kayi mata, shin ita Amal din muharramarka ce?

Amal da shahida duk daya suke awajanka, zaka iya auren kowa acikinsu
Amma Okasha...
Chapter 12 · 0% Book details