Sashe 26
Burinah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tace baba anty shahida ce qanwar Yaya daddy
Umma tace to Shahid Sai munga goron gayyata tunda abin ba sanarwa
Shahid Kasa magana yayi, yayi shiru
Umma tace oh kice Nima dana yakusa zama ango
Sai a sannan yace kai umma ni wasa takemin
Baba yace a a Amal kice gidan surukai zamuje
Dukansu sukasa daria, banda daddy dayayi murmushi kawai
Sosai Shahid yake gudu, har sukaje bauchi babu ma wanda ya lura da daddy
Suna Zuwa directly government house sukaje, sojojin dake bakin gate din gidan suna ganin motar suka Bude musu suka shiga
Tun kafin motar su ta tsaya, security suka qaraso aguje suka Bude musu murfin motar, yana futowa kuwa yacire abin fuskarsa, yafara miqawa mutanan dasuka mamaye wajan hannu suna gaisawa , sai kuma security dake tsare lafiyarsa dasuke tambayarsa Yaya yadawo?
Dole Sai tsayawa yayi su kuma su Amal sukai cikin gidan
Momy tana ganinsu tarasa inda zata sakasu Sai nan nan take dasu, sai yanzu baba yaqara tabbatar wa suna riqe Amal da gaskya
Abba yana gida, Bayan sun gaisa aka gabatar musu da abinci suka ci, sosai umma taji dadi
Babu Bata lokaci ba wajan qara jaddada godiyar su
Abba yace ai babu komai,
Shahid Sai waigawa yake ko zaiga shahida, Amma kuwa tana hankalce dashi, Dan haka tace momy Ina anty shahida ne?
Banganta ba
Momy tace shahida tana daki batajin dadi, ciwon ciki take wallahi, yau dashi tatashi
Bari naje natasota ku gaisa, umma tace a a hajiya barta, bari mu shiga mu dubata da kanmu
Adede lokacin daddy yashigo, suka tafi Dakin shahida gaba dayansu, banda, Shahid Sai sunkuyar dakai yake
Amal ta juya tayi masa hararar wasa
Haka itama hankali da tunanin daddy suka tattare awajanta
Tana kwance tana bacci acikin blanket fari qal dashi
Shahid yazuba mata ido, fuskar ta tayi fayau
Motsin dataji ne yasa ta farka, ahankali ta Bude idonta, dashi tafara tozali, Shahid a gidansu?
Dakinta?
Meza tace da Amal ita kuwa?
Su umma ne suka fara yimata ya jiki, taqayar ta motsa tana amsa musu, saboda ba qaramin ciwo marar ta takeba
Daddy ne ya kalli Abba yace Abba doctor yazo ne?
Abba yace eh munyi waya yace yana hanya
Baba hamani yace sannu kinji Allah yasawaqe
Amal ma tace anty shahida sannu da jiki, itama tace yauwa anty Amal
Raliya ce tayi sallama tashigo Dakin dauke da abinci, tace hajiya ga abincin yau bataci komai ba, shahida cikin shagwaba tace momy nide naqoshi bazanciba
Shahid daya Kasa yimata magana, baisan lokacin daya miqawa momy hannu ya karbi abincin ba, ya miqawa shahida yace ki daure kici
Gaba dayan yan Dakin saida yabasu daria, daddy da aka kirashi awaya yafita daga Dakin yana murmushi
Shiru shahida tayi, ganin haka yasa umma tace to Bari mukoma falo hajiya mubar ta tahuta, tana bacci mun tasheta
Aikuwa duka suka fice daga Dakin suna Zuwa falo Amal ta zauna ajikin umma, tana kallan daddy dayake kallan window yana amsa waya cikin aji
*** *** ***
Yana ganin futarsu yadawo kusa da ita ya zauna agefen gadon
Idanu yazuba mata, shi Sai yauma yaga wani irin mugun kyau data masa
Abincin ya ajiye, ahankali yakai hannun sa kan nata hannun
Kanta aqasa takasa dagowa ta kalleshi saboda wani mugun kwarjini daya mata
Zame hannun ta tafara yi, tasan bayaso tunda tayi kokarin riqe kafarsa a Indonesia yakusa sheqa mata mari, Dan haka ta janye hannun ta
Kallanta yake sosai yasake Kai hannu yariqe Hannunta dakyau, wani irin laushi yaji cikin hannun nata, abinka da wanda baya aikin wahala
Murya qasa yace kiyi hakuri
Shahida tayi shiru
Shahid yasake cewa kinji?
Daga masa Kai tayi ahankali
Yace Dan Allah Koda wasa karki rage Koda digo dayake acikin soyaiyar dakikemin, nayi alqawarin zan nuna miki soyaiya fiye da wadda kikemin
Hannun ta dayake cikin nasa yakai setin bakinsa yayi kissing Bayan hannun
Shahida mamaki yakashe ta a zaune, mutumin dayake fada da sababi Akan zata riqe shi, shine yau harda kissing hannun ta?
Anya Shahid din data sani abaya ne kuwa?
Abincin yadauko yadebo a spoon yayi Bakinta dashi yace to Bude bakin nabaki
Aikuwa shahida babu musu, ta Bude baki, yadinga Bata abincin, sai gashi takusa cinyewa
Yadebo zai Kai Bakinta ne su Momy Abba, umma da baba da daddy da Amal tare da doctor suka turo kofar Dakin suka shigo
Kana ganin Zaman su kasan irin wannan Zaman Sai masoya
Dasauri ya ajiye spoon din yana matsawa baya cikin sauri, shahida kanta saida yabata daria, to ai sun Riga dasun gansu
Doctor ne yaduba ta, yajuyo yacewa Abba alhaji wannan ciwon cikinfa bazata denaba saide in aure za'ai mata
Amma inba hakaba duk wata ta dinga yinsa kenan
Shahid da baisan Akan wanne irin ciwon ciki ake maganaba cikin tsananin tausayin ta yayi caraf yace to Abba ayi mata auren mana, Amma ace ciwo duk wata?
Gaba daya yan Dakin ne suka zuba masa ido
Shikuma yaji sunyi shiru, yadago kansa kenan kawai yaga dukansu shi suke kallo
Ashefa shine wanda shahidan take so
Wayyo Allah qasa tsage shahida yashige saboda wata muguwar kunya dayaji takamashi, ai cikin sauri yafice daga Dakin yayi falo
Doctor ne yabata magani, su umma da momy dasuke dariyar Shahid suma suka futo gaba dayansu
Ana zaune afalo nan take kuwa baba hamani yace yana nemawa dansa auren yarsa shahida
Abba ma cikin farin ciki yace anbaku Malam
Babu Bata lokaci Abba yakira waya yace kawo musu goro, sannan yakira abokansa biyu, a take aka saka ranar aure nan da sati biyu
Inda daddy yace yadau nauyin komai na ango da amarya
Comments please
Mrs Usman ce
BURINAH
(A Romantic love story)
Writing by Amnah El yaqoub
Bismillahir-rahmanirraheem
Godia iyayen duka suka yiwa daddy, Abba yace to Nima de baza'a barni abaya ba, yadubi Shahid yace dana Shahid ka aikomin da takardun karatun ka Bayan biki insha Allah saika fara aiki
Sannan katuromin da account number ka zansama ko miliyan goma ne ka sake rage wata hidimar, kafin muga abinda Allah zaiyi, kayi hakuri babu yawa
Mamaki ne yakama Amal, kyautar miliyan goma Amma ko ajikinsa kamar yayi kyautar dubu goma
Haka su umma sukaita godia, kowa de yana cikin farin ciki, saida suka Dan jima kafin suka fara haramar tafiya gida, daddy yasa adaukesu amaidasu
Amal ta riqe ummanta, tace umma ni wallahi banaso ku tafi, kamar ku kwana anan, umma tace Amal abinda nakeso dake shine, ki riqe mijin ki da iyayen mijin ki Amana Dan Allah, kinga de irin karamcin dasuka mana, Dan Allah karki bari wata matsala ta faru tsakanin ku
Yi nayi bari nabari, kidena barinsa da yunwa, Dan nasan halinki
Amal tace to umma insha Allah
Haka suka dunguma suka raka su wajan Mota, sannan suka dawo ciki
Suna dawowa momy ta dubi Amal tace kira mufeeda ki fada Mata zancan saka ranar
Amal tana farin ciki tace to momy
Bayan sun gaisa da anty mufy ne Amal take fada Mata zancan saka ranar, aikuwa tace to tana Nan zuwa jibi insha Allah domin afara shirin biki
Da daddare dukansu suna yin dinner, shahida Sai tsari take kamar ba majinyaciya ba, Amal nacin abincin ta anutse kanta aqasa, shikuwa gaba daya tension dinsa yana kanta, shahida ta qyalla ido taga yanda Yaya daddy yazubawa Amal ido aranta tace um masoya, har agaban su abban ma babu Kara
Tana dago Kai suka hada ido da daddy aikuwa saita qware
Tari tafara, momy tace subhanallah ungo ruwa Sha yata
Tafadi hakan tana bubbuga bayanta
Ruwan ta karba tasha kadan, momy tace sannu, ai dole ki qware irin wannan kallo haka, ninarasa inda kaje ka koyo wannan kallo wallahi, Kai bakaci abincin ba, ita baka barta taciba
Ahankali shahida Tasa daria, Amma Bata bari gogan yaganta ba
Abba ma murmushi yayi kawai, shikuwa daddy dayasan dashi ake kawai saiya sunkuyar dakai yana shafa Sumar kansa
Suna gama cin abinci, tayi Dakinta tayi wanka, ta kulle kofarta saboda tasan Sarai zai iya zuwa
Aikuwa Bata dade da kwanciya ba, taji alamun Bude kofar, but tariga data kulle
Haka ya hakura yakoma dakinsa, shidama ba komai zai mataba kawai de zaiyi mata saida safe ne
*** *** ***
Washe gari tunda sassafe yashirya yafuto falon, yayi masifar kyau cikin manyan kaya, shi kadai yanata zagaye yana jira tafuto, Amma Bata futo ba, bayasan yafita office batare daya ganta ba, idan yajema tunanin ta zaiyi tayi, bazaiyi aikin kirki ba, yarasa meyasa take masa haka yanzu, Bayan itace tajashi ajikinta harya sake da ita, Amma to meyasa yanzu ta dena?
Yana Nan atsaye shahida ta futo daga Dakinta tayi Dakin Amal din
Har qasa ta tsugunna ta gaidashi ya amsa, yabita da kallo
Tana zuwa Dakin tace anty Amal Bude nazo
Aikuwa yaga anbude kofa, kenan de har yanzu Bata huce ba, shidin ne batasan gani
Kai tsaye Shima yayi cikin Dakin tare da sallama, suna zaune agefen gado
Bema kula su ba ya wuce wajan drawer yafara dube dube
Da kallan mamaki tabishi, meya ajiye mata da zai dauka?
Kamar yasan abinda take tunani kuwa yadubeta yace akwai wasu takardu dana ajiye anan Ina kika maidasu?
Cikin mamaki tace takardu kuma?
Shahida na ganin haka tace anty Amal bari naje nadawo, tafice
Bayanta yabi tareda rufe Dakin, yadawo kusa da ita har jikinsu na gugar juna yace, meyasa kike gudunane?
Kanta ta sunkuyar qasa tace babu komai
Amma Aina baki hakuri ko?
Nace nadena, kuma ni magana Akan Shahid dinma nadena, ai dan'uwana ne
Hannayenta yakama yasauko daga gadon yace kiyi hakuri baby bazan sakeba yasake yin qasa da murya yace please
Runtse idanuwanta tayi, zuciyar ta tacigaba da bata shawarar Amal, kinga tun yana bin kanki Kar yazo yadena, mutum mai aji da kudi da kyau dakuma uwa uba miskilanci shine a tsugunne agabanta
Kamar me rada yace kin hakura?
Umma tace to Shahid Sai munga goron gayyata tunda abin ba sanarwa
Shahid Kasa magana yayi, yayi shiru
Umma tace oh kice Nima dana yakusa zama ango
Sai a sannan yace kai umma ni wasa takemin
Baba yace a a Amal kice gidan surukai zamuje
Dukansu sukasa daria, banda daddy dayayi murmushi kawai
Sosai Shahid yake gudu, har sukaje bauchi babu ma wanda ya lura da daddy
Suna Zuwa directly government house sukaje, sojojin dake bakin gate din gidan suna ganin motar suka Bude musu suka shiga
Tun kafin motar su ta tsaya, security suka qaraso aguje suka Bude musu murfin motar, yana futowa kuwa yacire abin fuskarsa, yafara miqawa mutanan dasuka mamaye wajan hannu suna gaisawa , sai kuma security dake tsare lafiyarsa dasuke tambayarsa Yaya yadawo?
Dole Sai tsayawa yayi su kuma su Amal sukai cikin gidan
Momy tana ganinsu tarasa inda zata sakasu Sai nan nan take dasu, sai yanzu baba yaqara tabbatar wa suna riqe Amal da gaskya
Abba yana gida, Bayan sun gaisa aka gabatar musu da abinci suka ci, sosai umma taji dadi
Babu Bata lokaci ba wajan qara jaddada godiyar su
Abba yace ai babu komai,
Shahid Sai waigawa yake ko zaiga shahida, Amma kuwa tana hankalce dashi, Dan haka tace momy Ina anty shahida ne?
Banganta ba
Momy tace shahida tana daki batajin dadi, ciwon ciki take wallahi, yau dashi tatashi
Bari naje natasota ku gaisa, umma tace a a hajiya barta, bari mu shiga mu dubata da kanmu
Adede lokacin daddy yashigo, suka tafi Dakin shahida gaba dayansu, banda, Shahid Sai sunkuyar dakai yake
Amal ta juya tayi masa hararar wasa
Haka itama hankali da tunanin daddy suka tattare awajanta
Tana kwance tana bacci acikin blanket fari qal dashi
Shahid yazuba mata ido, fuskar ta tayi fayau
Motsin dataji ne yasa ta farka, ahankali ta Bude idonta, dashi tafara tozali, Shahid a gidansu?
Dakinta?
Meza tace da Amal ita kuwa?
Su umma ne suka fara yimata ya jiki, taqayar ta motsa tana amsa musu, saboda ba qaramin ciwo marar ta takeba
Daddy ne ya kalli Abba yace Abba doctor yazo ne?
Abba yace eh munyi waya yace yana hanya
Baba hamani yace sannu kinji Allah yasawaqe
Amal ma tace anty shahida sannu da jiki, itama tace yauwa anty Amal
Raliya ce tayi sallama tashigo Dakin dauke da abinci, tace hajiya ga abincin yau bataci komai ba, shahida cikin shagwaba tace momy nide naqoshi bazanciba
Shahid daya Kasa yimata magana, baisan lokacin daya miqawa momy hannu ya karbi abincin ba, ya miqawa shahida yace ki daure kici
Gaba dayan yan Dakin saida yabasu daria, daddy da aka kirashi awaya yafita daga Dakin yana murmushi
Shiru shahida tayi, ganin haka yasa umma tace to Bari mukoma falo hajiya mubar ta tahuta, tana bacci mun tasheta
Aikuwa duka suka fice daga Dakin suna Zuwa falo Amal ta zauna ajikin umma, tana kallan daddy dayake kallan window yana amsa waya cikin aji
*** *** ***
Yana ganin futarsu yadawo kusa da ita ya zauna agefen gadon
Idanu yazuba mata, shi Sai yauma yaga wani irin mugun kyau data masa
Abincin ya ajiye, ahankali yakai hannun sa kan nata hannun
Kanta aqasa takasa dagowa ta kalleshi saboda wani mugun kwarjini daya mata
Zame hannun ta tafara yi, tasan bayaso tunda tayi kokarin riqe kafarsa a Indonesia yakusa sheqa mata mari, Dan haka ta janye hannun ta
Kallanta yake sosai yasake Kai hannu yariqe Hannunta dakyau, wani irin laushi yaji cikin hannun nata, abinka da wanda baya aikin wahala
Murya qasa yace kiyi hakuri
Shahida tayi shiru
Shahid yasake cewa kinji?
Daga masa Kai tayi ahankali
Yace Dan Allah Koda wasa karki rage Koda digo dayake acikin soyaiyar dakikemin, nayi alqawarin zan nuna miki soyaiya fiye da wadda kikemin
Hannun ta dayake cikin nasa yakai setin bakinsa yayi kissing Bayan hannun
Shahida mamaki yakashe ta a zaune, mutumin dayake fada da sababi Akan zata riqe shi, shine yau harda kissing hannun ta?
Anya Shahid din data sani abaya ne kuwa?
Abincin yadauko yadebo a spoon yayi Bakinta dashi yace to Bude bakin nabaki
Aikuwa shahida babu musu, ta Bude baki, yadinga Bata abincin, sai gashi takusa cinyewa
Yadebo zai Kai Bakinta ne su Momy Abba, umma da baba da daddy da Amal tare da doctor suka turo kofar Dakin suka shigo
Kana ganin Zaman su kasan irin wannan Zaman Sai masoya
Dasauri ya ajiye spoon din yana matsawa baya cikin sauri, shahida kanta saida yabata daria, to ai sun Riga dasun gansu
Doctor ne yaduba ta, yajuyo yacewa Abba alhaji wannan ciwon cikinfa bazata denaba saide in aure za'ai mata
Amma inba hakaba duk wata ta dinga yinsa kenan
Shahid da baisan Akan wanne irin ciwon ciki ake maganaba cikin tsananin tausayin ta yayi caraf yace to Abba ayi mata auren mana, Amma ace ciwo duk wata?
Gaba daya yan Dakin ne suka zuba masa ido
Shikuma yaji sunyi shiru, yadago kansa kenan kawai yaga dukansu shi suke kallo
Ashefa shine wanda shahidan take so
Wayyo Allah qasa tsage shahida yashige saboda wata muguwar kunya dayaji takamashi, ai cikin sauri yafice daga Dakin yayi falo
Doctor ne yabata magani, su umma da momy dasuke dariyar Shahid suma suka futo gaba dayansu
Ana zaune afalo nan take kuwa baba hamani yace yana nemawa dansa auren yarsa shahida
Abba ma cikin farin ciki yace anbaku Malam
Babu Bata lokaci Abba yakira waya yace kawo musu goro, sannan yakira abokansa biyu, a take aka saka ranar aure nan da sati biyu
Inda daddy yace yadau nauyin komai na ango da amarya
Comments please
Mrs Usman ce
BURINAH
(A Romantic love story)
Writing by Amnah El yaqoub
Bismillahir-rahmanirraheem
Godia iyayen duka suka yiwa daddy, Abba yace to Nima de baza'a barni abaya ba, yadubi Shahid yace dana Shahid ka aikomin da takardun karatun ka Bayan biki insha Allah saika fara aiki
Sannan katuromin da account number ka zansama ko miliyan goma ne ka sake rage wata hidimar, kafin muga abinda Allah zaiyi, kayi hakuri babu yawa
Mamaki ne yakama Amal, kyautar miliyan goma Amma ko ajikinsa kamar yayi kyautar dubu goma
Haka su umma sukaita godia, kowa de yana cikin farin ciki, saida suka Dan jima kafin suka fara haramar tafiya gida, daddy yasa adaukesu amaidasu
Amal ta riqe ummanta, tace umma ni wallahi banaso ku tafi, kamar ku kwana anan, umma tace Amal abinda nakeso dake shine, ki riqe mijin ki da iyayen mijin ki Amana Dan Allah, kinga de irin karamcin dasuka mana, Dan Allah karki bari wata matsala ta faru tsakanin ku
Yi nayi bari nabari, kidena barinsa da yunwa, Dan nasan halinki
Amal tace to umma insha Allah
Haka suka dunguma suka raka su wajan Mota, sannan suka dawo ciki
Suna dawowa momy ta dubi Amal tace kira mufeeda ki fada Mata zancan saka ranar
Amal tana farin ciki tace to momy
Bayan sun gaisa da anty mufy ne Amal take fada Mata zancan saka ranar, aikuwa tace to tana Nan zuwa jibi insha Allah domin afara shirin biki
Da daddare dukansu suna yin dinner, shahida Sai tsari take kamar ba majinyaciya ba, Amal nacin abincin ta anutse kanta aqasa, shikuwa gaba daya tension dinsa yana kanta, shahida ta qyalla ido taga yanda Yaya daddy yazubawa Amal ido aranta tace um masoya, har agaban su abban ma babu Kara
Tana dago Kai suka hada ido da daddy aikuwa saita qware
Tari tafara, momy tace subhanallah ungo ruwa Sha yata
Tafadi hakan tana bubbuga bayanta
Ruwan ta karba tasha kadan, momy tace sannu, ai dole ki qware irin wannan kallo haka, ninarasa inda kaje ka koyo wannan kallo wallahi, Kai bakaci abincin ba, ita baka barta taciba
Ahankali shahida Tasa daria, Amma Bata bari gogan yaganta ba
Abba ma murmushi yayi kawai, shikuwa daddy dayasan dashi ake kawai saiya sunkuyar dakai yana shafa Sumar kansa
Suna gama cin abinci, tayi Dakinta tayi wanka, ta kulle kofarta saboda tasan Sarai zai iya zuwa
Aikuwa Bata dade da kwanciya ba, taji alamun Bude kofar, but tariga data kulle
Haka ya hakura yakoma dakinsa, shidama ba komai zai mataba kawai de zaiyi mata saida safe ne
*** *** ***
Washe gari tunda sassafe yashirya yafuto falon, yayi masifar kyau cikin manyan kaya, shi kadai yanata zagaye yana jira tafuto, Amma Bata futo ba, bayasan yafita office batare daya ganta ba, idan yajema tunanin ta zaiyi tayi, bazaiyi aikin kirki ba, yarasa meyasa take masa haka yanzu, Bayan itace tajashi ajikinta harya sake da ita, Amma to meyasa yanzu ta dena?
Yana Nan atsaye shahida ta futo daga Dakinta tayi Dakin Amal din
Har qasa ta tsugunna ta gaidashi ya amsa, yabita da kallo
Tana zuwa Dakin tace anty Amal Bude nazo
Aikuwa yaga anbude kofa, kenan de har yanzu Bata huce ba, shidin ne batasan gani
Kai tsaye Shima yayi cikin Dakin tare da sallama, suna zaune agefen gado
Bema kula su ba ya wuce wajan drawer yafara dube dube
Da kallan mamaki tabishi, meya ajiye mata da zai dauka?
Kamar yasan abinda take tunani kuwa yadubeta yace akwai wasu takardu dana ajiye anan Ina kika maidasu?
Cikin mamaki tace takardu kuma?
Shahida na ganin haka tace anty Amal bari naje nadawo, tafice
Bayanta yabi tareda rufe Dakin, yadawo kusa da ita har jikinsu na gugar juna yace, meyasa kike gudunane?
Kanta ta sunkuyar qasa tace babu komai
Amma Aina baki hakuri ko?
Nace nadena, kuma ni magana Akan Shahid dinma nadena, ai dan'uwana ne
Hannayenta yakama yasauko daga gadon yace kiyi hakuri baby bazan sakeba yasake yin qasa da murya yace please
Runtse idanuwanta tayi, zuciyar ta tacigaba da bata shawarar Amal, kinga tun yana bin kanki Kar yazo yadena, mutum mai aji da kudi da kyau dakuma uwa uba miskilanci shine a tsugunne agabanta
Kamar me rada yace kin hakura?