Sashe 25
Bani Nayi Kaina Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zaka sota kaman yanda kaso zakiyya ai itama baka sonta aka aura maka ita yanzu ba gashi kuna zamanku lafiya ba.
Abba..... Abba.... Abba dafa shi abban yayi yace yi shiru ridwan tashi kaje Allah yayi maka albarka ni zan dau dawainiyar komi tunda har ka amince na da yan sati uku ne bikin Allah ya muku albarka.
Mikewa yayi kanshi na wani irin sarawa da kyar ya kai kanshi side dinshi na gidan key din motanshi ya lalubo dan key din na jiki ya bude ya shiga.
Dakin duk yayi kura cikin kuran ya shiga ya hau gadon ya kwanta .
Meke shirin faruwa da rayuwansu shi da precious me yasa abba ke mishi haka sai kace shi kadai ne namiji a zuriyar innalillahi.
Ta ina zai fara fadawa precious wannan maganan gashi lokacin a kure the last thing he want shine daga mata hankali a condition din nan nata.
Bam ta banko kofar tare da juyo da yar uwarta me nake ji haka fadeela me kika aikata?
Wato ke baza ki taba barin rayuwar zakiyya ba ko me zakiyya ta miki ne haka ki rasa wanda zaki aura sai mijinta ta karasa tana hawaye.
Murmushin rainin hankali fadilan tayi tace lallai tambayata kike me zakiyya ta min ko yanda kike behaving kadai ya isa yasa in tsani zakiyya ke yar uwata ce ta haihuwa amma kin fifita zakiyya a kaina.
Yanzu akan zakiyya iyayena haushina suke ji duk saboda zakiyya.
Kina wani maganan zan aure mata miji naga dai dan uwana ne ita bare ma ta sameshi balle ni.
Girgiza kai fareeda tayi kawai ta furta Allah ya shiryeki a hankali ta fita.
Cikin daga sauti tace ameen in har zuci ne.
Bangarena ganin har 11:30 ba alamun yah rid ba wayarsa hankalina yayi mugun tashi sai lokacin na fara jin tsoron kiran da abban ya mishi.
Allah dai yasa lafiya dan nayi ta gwada number dinshi a kashe.
Tashi daya hadari ya hadu ruwa ya kece hankalina ya kuma tashi wayar mama na kira nace mata yah bai dawo ba har yanzu itama hankalinta a tashe ta nufi side din abba duk da ba ita bace da shi
Hango motanshi tayi hakan ya tabbatar mata yana gidan dakinshi ta nufa nan ta sameshi.
Tace haba sojana ba a san soja da ragwantaka ba kabi ka tadawa kanka hankali tare da matarka ka manta yanayin da take cikine.
A firgice ya mike yana duba lokaci ya kalli maman a sanyaye yace mama ban san me zance mata ba.
Kar kace mata komi gobe ka kawo min ita ni zan fahimtar da ita ai zakiyya yar albarka ce zaka sha mamakinta kai dai kayi kokarin danna damuwarka tashi ka tafi gidanka dare yayi hankalinta ya tashi.
A sukwane ya mike ya mata sallama ya fita.
SAWWAMA QAWWAMA
💖BANI NAYI KAINA BA💖
By Sawwama A.
42.
KU GAFARCENI NAJI NA SHIRU JIYA I WAS CARRIED AWAY BAN TASHI FARGAWA BA SAI WAJEN 12am.
Gudu yake ba kakkautawa ga ruwa da ake tsulawa titi yayi tsantsi hakan ya bawa tayoyin motan daman gogar titin kaman ana ja.
Ikon Allah ne kawai ya kai shi gida saboda irin gudun fitar hankalin da yake yi.
Horn yake dannawa kaman wanda aka koro a gigice sojojin suka bude mishi gate suna al-ajabin me ya fusata uban gidan nasu.
Yana karasowa bakin kofan palon na bude kofa a jike yake jagab dan fitowan da yayi daga car park zuwa kofar palon ne ya jike saboda ruwan da ake tsulawa.
Taranshi nayi ina tunanin me ke damun mijina haka.
Da karfi ya hade jikin mu ya min wani irin matsa da yasa ni zaro idanuna waje.
Dan patting bayanshi nayi duk da ban san meke damunshi ba hakan bai hanani lallashinshi ba.
Shhshh is okey cire kayan nan kar sanyi ya kama min kai na fadi hakan ina zamewa tare da balle botin din rigarsa.
A nan na cire mishi kayan ya rage i sai boxers janshi nayi zuwa dakinshi muka wuce toilet.
Taimaka mishi nayi yayi wanka na dakko abinci na feeding dinshi kaman yaro.
Shi kam ba abinda yake in ba kallonta ba,suna zamansu cikin aminci ana neman kawo musu fitina.
Bathroom na kuma kaishi muka yi brush ban matsa mishi da son jin meke damunshi ba tunda dai na san mahaifinshi ya kirashi kuma ba zai cutar dashi ba beside tsakanin da da mahaifi sai Allah ni yar kallo ce duk lokacin da yaso in san matsalar shi zai fada min.
Precious....
Dago kai nayi ina kallonshi da murmushi a fuskata nace na'am mijin precious.
Shima murmushin yayi yace na gode.
Gira daya na daga nace da akayi me.
Na gode da kulawarki a gareni Allah ya miki albarka.
Amin na ansa.
Precious, nace hummm.
Ki yafe min zan miki babban laifi wanda ko a mafarki ban taba tunanin zan aikata miki haka ba.
Da sauri na dago kaina nace me kake fada yah rid wani irin laifi kuma.
Rintse ido yayi yace ba zan iya yi miki shiru in barki a duhu ba har sai gobe precious abba na so in auri fadeela nan da sati uku.
Ido na kura mishi ba tare da ina gane me nake kallo ba dan Wani duhu duhu na fara gani kaina na wani jujjuyawa me nake ji ko dai mafarki nake yi.
Dan jijigata yayi yace babe dawo hankalin ki wallahi bana sonta ban son auranta ban san me zanyi ba ina cikin tashin hankali.
Hannu yasa ya riko fuskata ban san lokacin da na buge hannun ba idona yayi ja dan wani irin tukuki zuciyata yake yi.
Ya Allahu pls kar ki min haka ki fahimceni ke kadai zuciyata ke so da ke kadai nake burin kammala rayuwata ya kara kokarin kai hannu jikina.
Wani karfine ya zo min na dira daga kan gadon nace kar ka kara gigin tabani hmmm nayi murmushi nace zaka auri yar uwarka kake fada min ko na girgiza kai kwalla na cika idona dan na rasa da wata kalma zanyi amfani dan ina iya fadan mara kyau.
A hankali na furta me yasa suka aura maka ni tunda ga farko sun san zasu aura maka yar uwarka.
Me yasa basu bari na auri wani cikin dimbin masoya na ba suka aura maka ni alhalin sun san zasu baka yarsu girgiza kai na kuma yi hawayen dake mamale a idona ya zubo.
Right ni banda gata bani da zabi saboda mu ba wasu bane tallafawa rayuwata aka yi.
Da farko an daurawa wanda baya sona aure dani na ci wuyarsa sai yanzu da na samu soyayyarsa nake ganin zan samu kulawarsa nafi ko wace mace sa'a a dai dai wannan gaban ne za a aura masa wata.
Kallonta kawai yake dan bai taba ganinta a cikin wannan yanayin ba katse mishi tunani tayi da fadin wai kai baka da zabi ne a rayuwarka especially rayuwarka ta aure sai yanda aka tsara maka?
Biyota yace zakiyya kar kishi da bacin rai ya saki furta abinda zakiyi da na sani ki fahimceni ki fahimci iyayyenmu basu taba kinki ba asalima sun san da fadeelan suka yi kwadayin hadamu aure fadila ce kawai da fitina ta taso da wannan maganan a yanzu.
Right fadeela ta sha cewan ban dace da rayuwarka ba ko mai yasa oho kaima ka san ban dace da rayuwarka ba ko.
Tausayi ta bashi sosai ganin yanda take kaman sabuwar kamu duk maganganun da take a nutse take yi sai da yayi kokarin kusanto kanshi da ita a lokacin ne ta bude murya tana fadin nace kar ka matso kusa dani.
Ture bedside lamp din nayi lokaci daya na dire guiwowina akasa ina wani irin kuka me cin rai dan tabbas an gama da rayuwata.
Matsowa yayi ahankali ya rumgumeni tun ina turje turje har na hakura saboda irin rikon da ya min.
Kuka nake sosai ina surututai da ni kaina ban san mai nake fada ba a takaice daren ranan ba wanda ya runtsa a cikinmu.
Da safe ko kallo bai isheni ba dan gani nake shima munafuki ne ai bai nuna kin auran kaman yanda ya nuna kin aurena ba ko dan ita yar uwarshi ce oho.
A daddare yace mata ta shirya mama tace tana nemanta dan shi wani shakkanta yake ji dan bai taba ganin ta hada rai haka ba.
Ba wanda ya karya cikin mu dan ko kitchen din ban leka ba muka nufi cikin gida.
Ko a mota ba mai kula wani shi tsoron yi mata magana yake ita kuma dama a sama taje jiran kadan take.
Zaune nake gaban momy tana fahimtar dani makasudin auran tare da min nasiha kuka nake tukuru amma zuciyata ta dan sanyaya dan tabbas alamu sun nuna ba kowa ke son auran ba dan kam ko da mama bata furta ba fuskan ya nuna baro baro bata son auran.
Ita taje gaya min irin tashin hankalin da yah rid ya shiga da akayi mishi maganan auran take nadama da tausayin mijina suka shigeni.
Kunyarshi ce ta kamani yanda na rufe ido nayi ta mishi rashin kunya jiya Allah sarki yah rid zan tayaka yiwa iyayyenmu biyayya and i will support you in every aspect.
KUYI HAKURI DA WANNAN ZUWA DARE.
.
SAWWAMA QAWWAM
💖BANI NAYI KAINA BA💖
By Sawwama A.
Page 43.
Lekowa dakin yayi jikinshi duk a sanyaye ganin tana bacci a kan gadon mamah ya sa shi sakin ajiyar zuciya.
Tun da ya kawota ya fita wajen sameer yanzu ma ya zo ya mata sallama ne dan jirgin karfe shida zai bi.
A hankali ya karaso ya zauna a bakin gadon innocent face dinta ya kurawa ido yanda bakin zara zaran eye lashes dinta ke kwance.
Bakinta ya kalla dan tsut dashi a cune murmushi ya saki ba tare da ya shiryawa hakan ba babban yatsarsa yasa yana shafan leban.
Da sauri ya janye hannunshi ganin ta motsa the last thing je want shine fada da precious dinshi kafin ya tafi ya gwamace ya tafi bai mata sallama ba.
Allah ka huci zuciyar baiwarkan nan bai daddara ba ya kai hannunshi kan fuskanta yana shafawa a hankali.
Abba..... Abba.... Abba dafa shi abban yayi yace yi shiru ridwan tashi kaje Allah yayi maka albarka ni zan dau dawainiyar komi tunda har ka amince na da yan sati uku ne bikin Allah ya muku albarka.
Mikewa yayi kanshi na wani irin sarawa da kyar ya kai kanshi side dinshi na gidan key din motanshi ya lalubo dan key din na jiki ya bude ya shiga.
Dakin duk yayi kura cikin kuran ya shiga ya hau gadon ya kwanta .
Meke shirin faruwa da rayuwansu shi da precious me yasa abba ke mishi haka sai kace shi kadai ne namiji a zuriyar innalillahi.
Ta ina zai fara fadawa precious wannan maganan gashi lokacin a kure the last thing he want shine daga mata hankali a condition din nan nata.
Bam ta banko kofar tare da juyo da yar uwarta me nake ji haka fadeela me kika aikata?
Wato ke baza ki taba barin rayuwar zakiyya ba ko me zakiyya ta miki ne haka ki rasa wanda zaki aura sai mijinta ta karasa tana hawaye.
Murmushin rainin hankali fadilan tayi tace lallai tambayata kike me zakiyya ta min ko yanda kike behaving kadai ya isa yasa in tsani zakiyya ke yar uwata ce ta haihuwa amma kin fifita zakiyya a kaina.
Yanzu akan zakiyya iyayena haushina suke ji duk saboda zakiyya.
Kina wani maganan zan aure mata miji naga dai dan uwana ne ita bare ma ta sameshi balle ni.
Girgiza kai fareeda tayi kawai ta furta Allah ya shiryeki a hankali ta fita.
Cikin daga sauti tace ameen in har zuci ne.
Bangarena ganin har 11:30 ba alamun yah rid ba wayarsa hankalina yayi mugun tashi sai lokacin na fara jin tsoron kiran da abban ya mishi.
Allah dai yasa lafiya dan nayi ta gwada number dinshi a kashe.
Tashi daya hadari ya hadu ruwa ya kece hankalina ya kuma tashi wayar mama na kira nace mata yah bai dawo ba har yanzu itama hankalinta a tashe ta nufi side din abba duk da ba ita bace da shi
Hango motanshi tayi hakan ya tabbatar mata yana gidan dakinshi ta nufa nan ta sameshi.
Tace haba sojana ba a san soja da ragwantaka ba kabi ka tadawa kanka hankali tare da matarka ka manta yanayin da take cikine.
A firgice ya mike yana duba lokaci ya kalli maman a sanyaye yace mama ban san me zance mata ba.
Kar kace mata komi gobe ka kawo min ita ni zan fahimtar da ita ai zakiyya yar albarka ce zaka sha mamakinta kai dai kayi kokarin danna damuwarka tashi ka tafi gidanka dare yayi hankalinta ya tashi.
A sukwane ya mike ya mata sallama ya fita.
SAWWAMA QAWWAMA
💖BANI NAYI KAINA BA💖
By Sawwama A.
42.
KU GAFARCENI NAJI NA SHIRU JIYA I WAS CARRIED AWAY BAN TASHI FARGAWA BA SAI WAJEN 12am.
Gudu yake ba kakkautawa ga ruwa da ake tsulawa titi yayi tsantsi hakan ya bawa tayoyin motan daman gogar titin kaman ana ja.
Ikon Allah ne kawai ya kai shi gida saboda irin gudun fitar hankalin da yake yi.
Horn yake dannawa kaman wanda aka koro a gigice sojojin suka bude mishi gate suna al-ajabin me ya fusata uban gidan nasu.
Yana karasowa bakin kofan palon na bude kofa a jike yake jagab dan fitowan da yayi daga car park zuwa kofar palon ne ya jike saboda ruwan da ake tsulawa.
Taranshi nayi ina tunanin me ke damun mijina haka.
Da karfi ya hade jikin mu ya min wani irin matsa da yasa ni zaro idanuna waje.
Dan patting bayanshi nayi duk da ban san meke damunshi ba hakan bai hanani lallashinshi ba.
Shhshh is okey cire kayan nan kar sanyi ya kama min kai na fadi hakan ina zamewa tare da balle botin din rigarsa.
A nan na cire mishi kayan ya rage i sai boxers janshi nayi zuwa dakinshi muka wuce toilet.
Taimaka mishi nayi yayi wanka na dakko abinci na feeding dinshi kaman yaro.
Shi kam ba abinda yake in ba kallonta ba,suna zamansu cikin aminci ana neman kawo musu fitina.
Bathroom na kuma kaishi muka yi brush ban matsa mishi da son jin meke damunshi ba tunda dai na san mahaifinshi ya kirashi kuma ba zai cutar dashi ba beside tsakanin da da mahaifi sai Allah ni yar kallo ce duk lokacin da yaso in san matsalar shi zai fada min.
Precious....
Dago kai nayi ina kallonshi da murmushi a fuskata nace na'am mijin precious.
Shima murmushin yayi yace na gode.
Gira daya na daga nace da akayi me.
Na gode da kulawarki a gareni Allah ya miki albarka.
Amin na ansa.
Precious, nace hummm.
Ki yafe min zan miki babban laifi wanda ko a mafarki ban taba tunanin zan aikata miki haka ba.
Da sauri na dago kaina nace me kake fada yah rid wani irin laifi kuma.
Rintse ido yayi yace ba zan iya yi miki shiru in barki a duhu ba har sai gobe precious abba na so in auri fadeela nan da sati uku.
Ido na kura mishi ba tare da ina gane me nake kallo ba dan Wani duhu duhu na fara gani kaina na wani jujjuyawa me nake ji ko dai mafarki nake yi.
Dan jijigata yayi yace babe dawo hankalin ki wallahi bana sonta ban son auranta ban san me zanyi ba ina cikin tashin hankali.
Hannu yasa ya riko fuskata ban san lokacin da na buge hannun ba idona yayi ja dan wani irin tukuki zuciyata yake yi.
Ya Allahu pls kar ki min haka ki fahimceni ke kadai zuciyata ke so da ke kadai nake burin kammala rayuwata ya kara kokarin kai hannu jikina.
Wani karfine ya zo min na dira daga kan gadon nace kar ka kara gigin tabani hmmm nayi murmushi nace zaka auri yar uwarka kake fada min ko na girgiza kai kwalla na cika idona dan na rasa da wata kalma zanyi amfani dan ina iya fadan mara kyau.
A hankali na furta me yasa suka aura maka ni tunda ga farko sun san zasu aura maka yar uwarka.
Me yasa basu bari na auri wani cikin dimbin masoya na ba suka aura maka ni alhalin sun san zasu baka yarsu girgiza kai na kuma yi hawayen dake mamale a idona ya zubo.
Right ni banda gata bani da zabi saboda mu ba wasu bane tallafawa rayuwata aka yi.
Da farko an daurawa wanda baya sona aure dani na ci wuyarsa sai yanzu da na samu soyayyarsa nake ganin zan samu kulawarsa nafi ko wace mace sa'a a dai dai wannan gaban ne za a aura masa wata.
Kallonta kawai yake dan bai taba ganinta a cikin wannan yanayin ba katse mishi tunani tayi da fadin wai kai baka da zabi ne a rayuwarka especially rayuwarka ta aure sai yanda aka tsara maka?
Biyota yace zakiyya kar kishi da bacin rai ya saki furta abinda zakiyi da na sani ki fahimceni ki fahimci iyayyenmu basu taba kinki ba asalima sun san da fadeelan suka yi kwadayin hadamu aure fadila ce kawai da fitina ta taso da wannan maganan a yanzu.
Right fadeela ta sha cewan ban dace da rayuwarka ba ko mai yasa oho kaima ka san ban dace da rayuwarka ba ko.
Tausayi ta bashi sosai ganin yanda take kaman sabuwar kamu duk maganganun da take a nutse take yi sai da yayi kokarin kusanto kanshi da ita a lokacin ne ta bude murya tana fadin nace kar ka matso kusa dani.
Ture bedside lamp din nayi lokaci daya na dire guiwowina akasa ina wani irin kuka me cin rai dan tabbas an gama da rayuwata.
Matsowa yayi ahankali ya rumgumeni tun ina turje turje har na hakura saboda irin rikon da ya min.
Kuka nake sosai ina surututai da ni kaina ban san mai nake fada ba a takaice daren ranan ba wanda ya runtsa a cikinmu.
Da safe ko kallo bai isheni ba dan gani nake shima munafuki ne ai bai nuna kin auran kaman yanda ya nuna kin aurena ba ko dan ita yar uwarshi ce oho.
A daddare yace mata ta shirya mama tace tana nemanta dan shi wani shakkanta yake ji dan bai taba ganin ta hada rai haka ba.
Ba wanda ya karya cikin mu dan ko kitchen din ban leka ba muka nufi cikin gida.
Ko a mota ba mai kula wani shi tsoron yi mata magana yake ita kuma dama a sama taje jiran kadan take.
Zaune nake gaban momy tana fahimtar dani makasudin auran tare da min nasiha kuka nake tukuru amma zuciyata ta dan sanyaya dan tabbas alamu sun nuna ba kowa ke son auran ba dan kam ko da mama bata furta ba fuskan ya nuna baro baro bata son auran.
Ita taje gaya min irin tashin hankalin da yah rid ya shiga da akayi mishi maganan auran take nadama da tausayin mijina suka shigeni.
Kunyarshi ce ta kamani yanda na rufe ido nayi ta mishi rashin kunya jiya Allah sarki yah rid zan tayaka yiwa iyayyenmu biyayya and i will support you in every aspect.
KUYI HAKURI DA WANNAN ZUWA DARE.
.
SAWWAMA QAWWAM
💖BANI NAYI KAINA BA💖
By Sawwama A.
Page 43.
Lekowa dakin yayi jikinshi duk a sanyaye ganin tana bacci a kan gadon mamah ya sa shi sakin ajiyar zuciya.
Tun da ya kawota ya fita wajen sameer yanzu ma ya zo ya mata sallama ne dan jirgin karfe shida zai bi.
A hankali ya karaso ya zauna a bakin gadon innocent face dinta ya kurawa ido yanda bakin zara zaran eye lashes dinta ke kwance.
Bakinta ya kalla dan tsut dashi a cune murmushi ya saki ba tare da ya shiryawa hakan ba babban yatsarsa yasa yana shafan leban.
Da sauri ya janye hannunshi ganin ta motsa the last thing je want shine fada da precious dinshi kafin ya tafi ya gwamace ya tafi bai mata sallama ba.
Allah ka huci zuciyar baiwarkan nan bai daddara ba ya kai hannunshi kan fuskanta yana shafawa a hankali.