Sashe 9
Bani Da Zabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dan Allah ki saurareni, shi mutun daraja gare shi, Dan Allah na yarda da ja min aji ina neman alfarmar na san sunnan kawai a hankali za.a amince da soyayata
Mamaki ne ya cika mata zuciya, a ranar da ya ganta ma bai nuna tsoro ba, shi ne harda maganar soyaya? Haka kawai ta ji ya birge ta ko ba komai ya nuna mata kauna a fili
Dan gefensa ta bi ta ratsa shi ya juyo yana kallonta ya harde hannayensa fuskarsa kalar tausayi
Murmushi ta kuma saki wanda baya gani shi domin da nikaf, kasa kasa ta ce" *WUJDANE MAMA*
Wuf ta shige cikin gidan ita kadai sai murmushi take dokawa ta cire nikaf din
Inna dake bakin murhu tana iza ice ta dago cike da mamaki tana kallonta, murmushi na matukar kawata fuskar yarta, itama sai ji ta yi nata murmushin na fitowa domin fuskar mahaifinta sak ta fito a fuskar yar tata
Karasowa ta yi ta duka har kasa tana gaishe da innar
Cike da kulawa inna ta ce" ina Maman kuwa? ( Aisha )
Bayanta ta juya ta juyo ta ce" a can na barota ni gajiya na yi inna
Inna ta ci gaba da kallonta , sam Wujdane bata iya karya ba idan dai zaka tambayeta toh zata fada ne kai tsaye, ta yi imanin wannan murmushin kuwa da dalilinsa
Kallonta ta yi ta ce" mai ya saka ki nishadi haka,????
Wujdane ta dago da kanta cike da wani abu da take ji kadan kadan na taso mata , ta buda baki zata yi magana kenan sai ga muryar Jamail yna kwala salama
Kanta ta dafe irin na takurar nan ta mike ta yi dakinsu inda inna ke amsawa jamail salamarsa cike da murnar ganninsa, domin Jamail yayi tuwo ya yi tsaki har tsakar gida yake shigowa shi kawai gidansu ne
Tabarma inna ke shinfida masa tana amsa gaisuwarsa,
Dakin su wujdane ta juya ta kwala mata kira tana fadin ki fito ki ba dan uwanki ruwa mana Wujdane!
[3/27, 9:59 AM] +234 803 957 7698: 🦄🦄 *BANI DA ZABI*🦄🦄
*10*
WRINTING BY *SAJIDA*
Da sunnan Allah mai rahama mai jin kai,
*SAJIDARKU CE*
MARUBUCIYAR:
*YAR MAHAUKACIYA*
*DUK KARYAR KADA*
*DAGA TAFIYA DAUKAR SOJA*
*NEMAN NA KAINA*
................... *BANI DA ZABI* INSHA ALLAH....
Haka ya daukosu ya nufi gidansa da ya gina boyaye wanda ko mahaifiyarsa bata san da shi ba, ya kai su Marwa sannan ya nemo wata tsohuwa ya hada su
Komawa ya yi wa mahaifansa da mahaifan Marwar, aman cikin ikon Allah mahaifansa ko kalo bai ishe su ba, daga karshe mahaifinsa yayi rantsuwar idan ya kuma gannin kafarsa a gidansa toh lale zai tsine masa tunda ya nuna mace ta fi su, cike da tashin hankali ya dauki carte sin banki da mahifinsa ya bara masa wada keda kudadensa a ciki na kasewa ya karbe duka sauran abinda ya bashi kan sharadin in dai ba watsar da Marwa zai yi ba ya je ya bara mata shi
Cike da tashin hankali ya nufi gidan su Marwar, a nan ma dai zancen daya ne, ta yar da dan ta dawo gidan ida bata yarda ba ya yafe ta, mahaifiyarta ce ta biyo bayansa a boye ta bashi yan zannuwa tana kuka ta fada masa dan Allah ya kula da Marwa, karta yada kautar da Allah ya yi mata, ba laifinsa bane, kadara ce sai a karbe ta, insha Allah idan mahaifinta ya huce zata dawo
Haka ya dawo gidan ya zauna da Marwa ya sanar mata komai,
Ta jima tana kuka, ta jima tana astagafari tana rokan Allah ya yafe mata, ta rungumi yaronta inda Elhaj kadri a dakin kofa yake zaune idan ya shiga gidan sai dai dan ya ga lafiyarsu ne ya yiwa yaronsa wasa sannan ya fice,
Haka har ta yaye Alaidine cikin ikon Allah a masalaci ya nemi alfarma wajen liman ya fada masa duka yanda ake ciki
Liman din da kansa ya je wajen iyayensu dan gannin ko za.a sasanta, aman suna nan kan bakansu, sai dai shima mahaifiyarsa ta sauko aman tana mugun tsoron mijin nata
Du yada liman ya so ya kwatantawa iyayensu a sasanta basu saurare shi ba, kowane ya hau dokin zuciya duda shima mahaifin Marwar ya dan sauko aman gannin mahaifin Kadri bai sauko ba ya saka shima ya botsare
Liman ya wakilce su bayan salar juma.a aka daura masu aure, inda suka ci gaba da rainon Yarensu mai wani irn hali tun yana yaro,
Alaidine baya son hayaniya, ko dan ya rayu daga shi sai mahaifiyarsa da mahaifinsa ne , Alaidine bashi da tankiya, gumgum da shi baya shiga sabgar kowa ko da wasa
Mahaifinsa ya ci gaba da juya dukiyarsa wanda Allah ya saka mata albarka ta yi ta habaka,
Makarantar biya yake , yana da shekara takwas mahaifiyarsa ta sake haihuwa aka sakawa yaron sunna Anwar
Alaidine girmansa abin al.ajabi ne, bai jawowa iyayensa magana ko sau daya, kwazo gare shi a makaranta wanda hankalinsa ya fi karkata a kasuwanci,
Yana da shekara 18 aka yi masa gori a anguwa, wata mata haka kawai ya zo wucewa ta ce" wannan ai shine shegen gidan cen, sai dagin kai tamkar wani tsarkakake
Wannan magana ta saka su a tashin hankali domin a ranar ya san ko shi wanene , ya yi kuka har ya gode Allah, inda mahaifinsa ya dauke su da mahaifiyarsa da dan kanninsa msi shekara goma da tsohon cikinta suka koma sabon gidansa nesa da anguwar da yan uwansu da kowa suke zaune suna rayuwarsu
Alaidine ya saka wannan magana a ransa, hakan ya saka yake kauracewa mutanne domin yanai masu kallon wa.inda basu da uzuri shima sai ya daina yi masu uzuri
Tun yana da shekara goma sha tara ya nemi jari wajen mahaifinsa
Cike da farin ciki Elhaj Kadri ya bashi ya ja sana.a, wada suke mamakin husa.a ta yanda yake kirkirar abubuwa kala kala
Nan da nan sunnansa ya fito a yaro da kudi, farin jinninsa ya daukaka, lungu da sako maganarsa ce ake ana radin yaro da kudi yaro da kudi
Gashi ya dauko kyau da hutu, nan da nan ya rikide ya kara zama wani hamshaki mai aji
Sosai mata ke wawarsa, abinda ke dagawa mahaifiyarsa hankali kennan, domin har gida wasun ke zuwa nemansa
Du da irin taurin halin Alaidine akiy sadaka, zaka, yana taimakawa marayu, ya gina masalaci tankameme a unguwar da ya gina gidansa wanda yan anguwar kansu ke kiran gidan da ko a turai, domin babu ne kawai babu
Wani lokaci mahaifiyarsa ta saka shi gaba tana ta mita harda kuka kan ya fitar da mace, shi ko budurwar bashi da ita, mahaifinsa dake saukowa daga sama yana sauraron su, shi kansa ya lura da yannayin halitar Alaidine, ya dace ace da mace a kusan sa zuwa wannan lokacin aman shi sam baya ra.ayin yin aure bisa dalilinsa nasa na kansa,
Cike da fushi ya dago da kansa yana kallon mamansa ya ce" Mom, kina tsoron tarihi ya maimaita kansa a kaina ne? Ki yi hakuri da yardar Allah hakan ba zata faru ba
Cikin tsananin bacin rai da tir da halayarsa na fadin gaskiya kwadokwado baya shayi koma wanene ta wanka masa mari ta kara masa, muryarta na rawa ta nuna shi da yatsa ta ce" dan ka ga ana gudun zuciyarka dan kar ranka ya bace ka yi rashin lafiya ba wai tsoronka bane ya saka ko ka fi karfin mu bane, haihuwarka aka yi Alaidine kuma dole ka yi biyaya, idan har baka dauki kadarar rayuwarka ba kai ta gano aman baka isa ka jefe mu da wata kalma ba bayan kadara ce *Bamu da zabi* dole muka dauka, kaima haka zaka dauka
Tana gama fada ta haura sama da gudu mijinta ya tare ta yayi ta rarashinta
Bayan wannan da kwanaki mahaifinsa ya shaida masa an bashi auren yar gidan amininsa wanda ya san komai kuma ya yi amana da hada auren
Bayan sati biyu aka daura masa aure da khadija
Shi kansa bai san haka yake da muradin mace ba sai a kan Khadija, khadija ta kawo masa mutuncinta sannan tana gannin girmansa
Wai dai wani mugun abin , mahaifiyarta ta ji labarin ko wanene alaidine, nan fa ta kama hure mata kune har Khadija ta fara fito da halayen da bai santa da su ba
Daman ba aikin fari take ba bale na baki, domin da ma.aikata birjik a gidan masu kula da komai, sai ya kasance shi Khadija ta fara kauracewa a shinfida,
Da ta lura da ciki ya shigeta sai tashin hankali na kulun kala daban, tayi ta kuka idan ya tambayi ba.asi sai ta furta" ni dai an cuce ni an lalata min rayuwa
Abu tamkar wasa cikinta ya girma ta haife ta samu yaro namiji aka saka masa" *Huzaifa* suke kiransa da boy
Tunda ta haihu sai sabon kulafuci, ita ce wannan ita ce wancen, Alaidine bai taba kai kashenta ko kararta ba, kudi kuwa tamkar wuta haka take kashe su, shi kansa baya kashe kudin da take kashewa, boy kuwa tamkar ba ita ce ta haife shi ba, ta banzatar da shi bata damu da shi ba
Wata safiyar Asabar, Mahaifinta ya zo nemansa har gida dan ya kasa samunsa a waya kan harkar business, ya tarar da Khadija sai sababi take Alaidine kuwa yana sama yana hangenta ya harde hannu a kirjinsa yana tir da halayenta a kasan zuciyarsa harma yana mamakin kansa da yake iya kawar da kai yanai mata uzuri
Cike da masifa ta wsnkawa Huzaifa mari , wanda ya ji tamkar ta watsa masa wuta a fuska, cikin azama yake saukowa inda mahaifinta ya labe yana kallon ikon Allah
Yana saukowa ya dauki yaronsa idannuwansa har sun canza launi, ya nunota da yatsa ya ce" rashin mituncin naki har ya kai ki tsalake banzatar da aurenki da kike ki dawo dukan min yaro? Why Khadija? Mai yasa bakya gannin irin yanda nake kokarin gannin na fita a hakin ki na kula da amanar mahaifina? Idan bakya iya rayuwa ne da ni ai gwara ki fada da ki cutar da yarona, idan ni ne ki je ki yi bani da damuwa aman harda dan da kika haifa khadija?
Mamaki ne ya cika mata zuciya, a ranar da ya ganta ma bai nuna tsoro ba, shi ne harda maganar soyaya? Haka kawai ta ji ya birge ta ko ba komai ya nuna mata kauna a fili
Dan gefensa ta bi ta ratsa shi ya juyo yana kallonta ya harde hannayensa fuskarsa kalar tausayi
Murmushi ta kuma saki wanda baya gani shi domin da nikaf, kasa kasa ta ce" *WUJDANE MAMA*
Wuf ta shige cikin gidan ita kadai sai murmushi take dokawa ta cire nikaf din
Inna dake bakin murhu tana iza ice ta dago cike da mamaki tana kallonta, murmushi na matukar kawata fuskar yarta, itama sai ji ta yi nata murmushin na fitowa domin fuskar mahaifinta sak ta fito a fuskar yar tata
Karasowa ta yi ta duka har kasa tana gaishe da innar
Cike da kulawa inna ta ce" ina Maman kuwa? ( Aisha )
Bayanta ta juya ta juyo ta ce" a can na barota ni gajiya na yi inna
Inna ta ci gaba da kallonta , sam Wujdane bata iya karya ba idan dai zaka tambayeta toh zata fada ne kai tsaye, ta yi imanin wannan murmushin kuwa da dalilinsa
Kallonta ta yi ta ce" mai ya saka ki nishadi haka,????
Wujdane ta dago da kanta cike da wani abu da take ji kadan kadan na taso mata , ta buda baki zata yi magana kenan sai ga muryar Jamail yna kwala salama
Kanta ta dafe irin na takurar nan ta mike ta yi dakinsu inda inna ke amsawa jamail salamarsa cike da murnar ganninsa, domin Jamail yayi tuwo ya yi tsaki har tsakar gida yake shigowa shi kawai gidansu ne
Tabarma inna ke shinfida masa tana amsa gaisuwarsa,
Dakin su wujdane ta juya ta kwala mata kira tana fadin ki fito ki ba dan uwanki ruwa mana Wujdane!
[3/27, 9:59 AM] +234 803 957 7698: 🦄🦄 *BANI DA ZABI*🦄🦄
*10*
WRINTING BY *SAJIDA*
Da sunnan Allah mai rahama mai jin kai,
*SAJIDARKU CE*
MARUBUCIYAR:
*YAR MAHAUKACIYA*
*DUK KARYAR KADA*
*DAGA TAFIYA DAUKAR SOJA*
*NEMAN NA KAINA*
................... *BANI DA ZABI* INSHA ALLAH....
Haka ya daukosu ya nufi gidansa da ya gina boyaye wanda ko mahaifiyarsa bata san da shi ba, ya kai su Marwa sannan ya nemo wata tsohuwa ya hada su
Komawa ya yi wa mahaifansa da mahaifan Marwar, aman cikin ikon Allah mahaifansa ko kalo bai ishe su ba, daga karshe mahaifinsa yayi rantsuwar idan ya kuma gannin kafarsa a gidansa toh lale zai tsine masa tunda ya nuna mace ta fi su, cike da tashin hankali ya dauki carte sin banki da mahifinsa ya bara masa wada keda kudadensa a ciki na kasewa ya karbe duka sauran abinda ya bashi kan sharadin in dai ba watsar da Marwa zai yi ba ya je ya bara mata shi
Cike da tashin hankali ya nufi gidan su Marwar, a nan ma dai zancen daya ne, ta yar da dan ta dawo gidan ida bata yarda ba ya yafe ta, mahaifiyarta ce ta biyo bayansa a boye ta bashi yan zannuwa tana kuka ta fada masa dan Allah ya kula da Marwa, karta yada kautar da Allah ya yi mata, ba laifinsa bane, kadara ce sai a karbe ta, insha Allah idan mahaifinta ya huce zata dawo
Haka ya dawo gidan ya zauna da Marwa ya sanar mata komai,
Ta jima tana kuka, ta jima tana astagafari tana rokan Allah ya yafe mata, ta rungumi yaronta inda Elhaj kadri a dakin kofa yake zaune idan ya shiga gidan sai dai dan ya ga lafiyarsu ne ya yiwa yaronsa wasa sannan ya fice,
Haka har ta yaye Alaidine cikin ikon Allah a masalaci ya nemi alfarma wajen liman ya fada masa duka yanda ake ciki
Liman din da kansa ya je wajen iyayensu dan gannin ko za.a sasanta, aman suna nan kan bakansu, sai dai shima mahaifiyarsa ta sauko aman tana mugun tsoron mijin nata
Du yada liman ya so ya kwatantawa iyayensu a sasanta basu saurare shi ba, kowane ya hau dokin zuciya duda shima mahaifin Marwar ya dan sauko aman gannin mahaifin Kadri bai sauko ba ya saka shima ya botsare
Liman ya wakilce su bayan salar juma.a aka daura masu aure, inda suka ci gaba da rainon Yarensu mai wani irn hali tun yana yaro,
Alaidine baya son hayaniya, ko dan ya rayu daga shi sai mahaifiyarsa da mahaifinsa ne , Alaidine bashi da tankiya, gumgum da shi baya shiga sabgar kowa ko da wasa
Mahaifinsa ya ci gaba da juya dukiyarsa wanda Allah ya saka mata albarka ta yi ta habaka,
Makarantar biya yake , yana da shekara takwas mahaifiyarsa ta sake haihuwa aka sakawa yaron sunna Anwar
Alaidine girmansa abin al.ajabi ne, bai jawowa iyayensa magana ko sau daya, kwazo gare shi a makaranta wanda hankalinsa ya fi karkata a kasuwanci,
Yana da shekara 18 aka yi masa gori a anguwa, wata mata haka kawai ya zo wucewa ta ce" wannan ai shine shegen gidan cen, sai dagin kai tamkar wani tsarkakake
Wannan magana ta saka su a tashin hankali domin a ranar ya san ko shi wanene , ya yi kuka har ya gode Allah, inda mahaifinsa ya dauke su da mahaifiyarsa da dan kanninsa msi shekara goma da tsohon cikinta suka koma sabon gidansa nesa da anguwar da yan uwansu da kowa suke zaune suna rayuwarsu
Alaidine ya saka wannan magana a ransa, hakan ya saka yake kauracewa mutanne domin yanai masu kallon wa.inda basu da uzuri shima sai ya daina yi masu uzuri
Tun yana da shekara goma sha tara ya nemi jari wajen mahaifinsa
Cike da farin ciki Elhaj Kadri ya bashi ya ja sana.a, wada suke mamakin husa.a ta yanda yake kirkirar abubuwa kala kala
Nan da nan sunnansa ya fito a yaro da kudi, farin jinninsa ya daukaka, lungu da sako maganarsa ce ake ana radin yaro da kudi yaro da kudi
Gashi ya dauko kyau da hutu, nan da nan ya rikide ya kara zama wani hamshaki mai aji
Sosai mata ke wawarsa, abinda ke dagawa mahaifiyarsa hankali kennan, domin har gida wasun ke zuwa nemansa
Du da irin taurin halin Alaidine akiy sadaka, zaka, yana taimakawa marayu, ya gina masalaci tankameme a unguwar da ya gina gidansa wanda yan anguwar kansu ke kiran gidan da ko a turai, domin babu ne kawai babu
Wani lokaci mahaifiyarsa ta saka shi gaba tana ta mita harda kuka kan ya fitar da mace, shi ko budurwar bashi da ita, mahaifinsa dake saukowa daga sama yana sauraron su, shi kansa ya lura da yannayin halitar Alaidine, ya dace ace da mace a kusan sa zuwa wannan lokacin aman shi sam baya ra.ayin yin aure bisa dalilinsa nasa na kansa,
Cike da fushi ya dago da kansa yana kallon mamansa ya ce" Mom, kina tsoron tarihi ya maimaita kansa a kaina ne? Ki yi hakuri da yardar Allah hakan ba zata faru ba
Cikin tsananin bacin rai da tir da halayarsa na fadin gaskiya kwadokwado baya shayi koma wanene ta wanka masa mari ta kara masa, muryarta na rawa ta nuna shi da yatsa ta ce" dan ka ga ana gudun zuciyarka dan kar ranka ya bace ka yi rashin lafiya ba wai tsoronka bane ya saka ko ka fi karfin mu bane, haihuwarka aka yi Alaidine kuma dole ka yi biyaya, idan har baka dauki kadarar rayuwarka ba kai ta gano aman baka isa ka jefe mu da wata kalma ba bayan kadara ce *Bamu da zabi* dole muka dauka, kaima haka zaka dauka
Tana gama fada ta haura sama da gudu mijinta ya tare ta yayi ta rarashinta
Bayan wannan da kwanaki mahaifinsa ya shaida masa an bashi auren yar gidan amininsa wanda ya san komai kuma ya yi amana da hada auren
Bayan sati biyu aka daura masa aure da khadija
Shi kansa bai san haka yake da muradin mace ba sai a kan Khadija, khadija ta kawo masa mutuncinta sannan tana gannin girmansa
Wai dai wani mugun abin , mahaifiyarta ta ji labarin ko wanene alaidine, nan fa ta kama hure mata kune har Khadija ta fara fito da halayen da bai santa da su ba
Daman ba aikin fari take ba bale na baki, domin da ma.aikata birjik a gidan masu kula da komai, sai ya kasance shi Khadija ta fara kauracewa a shinfida,
Da ta lura da ciki ya shigeta sai tashin hankali na kulun kala daban, tayi ta kuka idan ya tambayi ba.asi sai ta furta" ni dai an cuce ni an lalata min rayuwa
Abu tamkar wasa cikinta ya girma ta haife ta samu yaro namiji aka saka masa" *Huzaifa* suke kiransa da boy
Tunda ta haihu sai sabon kulafuci, ita ce wannan ita ce wancen, Alaidine bai taba kai kashenta ko kararta ba, kudi kuwa tamkar wuta haka take kashe su, shi kansa baya kashe kudin da take kashewa, boy kuwa tamkar ba ita ce ta haife shi ba, ta banzatar da shi bata damu da shi ba
Wata safiyar Asabar, Mahaifinta ya zo nemansa har gida dan ya kasa samunsa a waya kan harkar business, ya tarar da Khadija sai sababi take Alaidine kuwa yana sama yana hangenta ya harde hannu a kirjinsa yana tir da halayenta a kasan zuciyarsa harma yana mamakin kansa da yake iya kawar da kai yanai mata uzuri
Cike da masifa ta wsnkawa Huzaifa mari , wanda ya ji tamkar ta watsa masa wuta a fuska, cikin azama yake saukowa inda mahaifinta ya labe yana kallon ikon Allah
Yana saukowa ya dauki yaronsa idannuwansa har sun canza launi, ya nunota da yatsa ya ce" rashin mituncin naki har ya kai ki tsalake banzatar da aurenki da kike ki dawo dukan min yaro? Why Khadija? Mai yasa bakya gannin irin yanda nake kokarin gannin na fita a hakin ki na kula da amanar mahaifina? Idan bakya iya rayuwa ne da ni ai gwara ki fada da ki cutar da yarona, idan ni ne ki je ki yi bani da damuwa aman harda dan da kika haifa khadija?