Sashe 6
Bani Da Zabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wujdane tunda ta tashi ta tashi da rigima daidai geargwado, cikin ikon Allah bata da hakuri idan dai ka shiga sabgarta toh zaka tarar, a kulun adu.a muke binta da ita Allah ya sanyaya, yau anyi abin kirki aman sai yamacin ya karashe da haka,
Ja nunfashi ya ce" Alhamdulilah, na san Allah na boye wani lamari a tare da ita, a kulun ina gode masa da ya malaka min ita, sannan ina adu.ar Allah ya shiryar min da ita ya saja mata nutsuwa a duk inda take
Cike da kaunar datakon Malan Anwar ya bada umarnin Balki ta fice ta koma itama gidansu, bayan dogon kashedi da gargadin kar ya kuma gannin kafar wata cikinsu a police station din nan domin ba zasu kwashe lafiya ba,
Haka Balki ta juya har gudu take ta tafi tana godewa Allah da ya takaita tashin hankalin nan
Kallon Wujdane suke gaba dayansu, shi Jamail gaba daya ta gama birge shi, yana son ya ga macen da bata daukan raini, shi kuwa Anwar a wani hali ya shiga, yarinyar ta yi masa fiye da tunanin bawa, kallonta yake a ransa yanai mata adu.ar samun nutsuwa ,
Cike da farin ciki Malan ke yi masu godiya wada ya umarce ta da ta yi wa Anwar da Jamail godiya
Dago da kanta ta yi bayan ta goge fuskarta wanda ya baiwa hannunta damar fitowa , yanda farin fuskarta yake haka na hannunta , faratunanta dogaye ne tsar ,
Idannuwanta ta dago a karo na farko ta sauke su a fuskar Anwar, gashin idannuwanta sun jike da hawaye hakan ya saka suka dan harhade suke kyali tsaf bakinsu ya fito radau, sai zagayen idannuwan ya yi jajajir kamar ya kode domin ba wani kwali a idon,
Murya na rawa ta ce" jazakallah
Bai san lokacin da ya lumshe idannuwansa ba, tamkar sarewa haka muryar ta yi masa rada a kunensa, a hankali ya furta" wa.iyaki
Ky din ya mikawa Jamail dan ya kaisu gida bayan an sha darga da Malan kan abin ya yu yawa, da kyar suka shawo kansa ita kuwa wujdane sai kumbura take tana karawa,
Nan suka bar Anwar zaune ya jinginar da kansa yana ta tunanin to ya aka yi basa kama ko kadan da Malan din,, ?????
Jin tunanin yarinyar zai dame shi ya saka ya mike ya fita ya harhada takardu ya fara dubawa yana kara zagaye police station din
Tafe suke malan na kara yi mata nasiha, cike da kula , Jamail kansa yayi tsam yana sauraro yana mamakin du abin nan da ta aikata malan yanai mata nasiha, uhum da wani uban ne ba mai hana shi dakata
Har suka karaso gidan wanda yara yu suka biyo motar suna ihun jirgi a anguwarsu domin irin motar nan ce mai tsayin nan,
Motar na tsayawa Wujdane ta bude ta fito a bayan ai kamar an watsa su suka fara guduwa ta ko.ina suna ihun walahi *MaMa* da malan ne a motar, du suka warwatse dan mai dukan yaro ce va zata saurara masa ba
Yauma bata tsaya cin abincin daren da su ba, ta fada dakin ta shiga baci
Malan bai fada ma inna ba, sannan bai fadawa kowa maganar ba bayan a titi da Mairo ta dan barbada cewar Wujdane na rufe sai ta yi wata , ganninta ta dawo ya saka ake zuwa har gidan su mairon anai mata ihun makaryaciya ta ji kunya
Da safe kofa ka san fitarta bayan ta shaidawa Aisha cewar ta tafi makaranta dan ta samu ta gama rubuce abubuwan da ya kamata bata da a litafinta
Sai da Malan ya fito take shaida masa ai ta fice makaranta da ya tambaya
Dan jim ya yi sannan ya fice har inna na tambayar lafiyar malan kuwa du wani sukuku take ganinsa???????????????????????
Konci tashi yau wajen sati...........
[3/27, 9:59 AM] +234 803 957 7698: 🦄🦄 *BANI DA ZABI*🦄🦄
*09*
WRINTING BY *SAJIDA*
Da sunnan Allah mai rahama mai jin kai,
*SAJIDARKU CE*
MARUBUCIYAR:
*YAR MAHAUKACIYA*
*DUK KARYAR KADA*
*DAGA TAFIYA DAUKAR SOJA*
*NEMAN NA KAINA*
................... *BANI DA ZABI* INSHA ALLAH....
Wujdane dake konce mamaki fal cikin ranta, mamakin yanda aka yi su malan suka sake da wannan bawan Allah, har wani dan uwanta inna ke cewa, a ina ya zama dan uwan nata????
Cike da jin haushi ta fito jin inna na kuma kiran sunnanta, wannan karin ba nikaf din aman da hijab dinta har kasa
Silbar wajen Malan da a ciki ake zuba masa ruwa idan ya zo domin ya fi kowanne haske ta dauko , ta bude randar cikin dakin inna tsaftataciya da kulun sai ta wanke ta ta juya wani ruwa sanyi karai da kanshi ta zuba masa ta kawo ta ajiye masa
Can gefe ta zauna ta turo baki ta hade fuska ta sada kanta kasa,
Kallonta Jamail yake can kasan zuciyarsa dariya tamkar ta kashe shi, shi kam ba zata bashi wuya ba domin yana zaune da wanda ya fita miskilanci, dan ita idan ta hana kanta abu akoy wa.inda suke tursasata, shi kuwa yaya Alaidine sai dai a hakura dan ko kalonku ba zai yi ba bake ka saka a kokon zuciyarka zai yi abin
A hankali ya ce" kanwata wujdane,
Da gangan ya fadi dan sau goma zai fadi hakan sai ta dago ta watsa masa harara dan ita ta tsani a mayar da ita yarinya, duda ya girme matan ya bata shekara biyu a kala aman sai tana ganin ya raina ta danme ba zai kirayi sunnanta kawai ba
Bata dago da kan ba, sannan bata amsa ba,
Murmushi yake saki na samun nasarar ya hauda ta, zai kara magana Aisha ta shigo da salama
Da fara.a yake mata oyoyo ya ce" lale da mamana,(kamar yanda su Malan ke fada mata), ya ci gaba haba yanzu bakina zai daina tsami kin ga inna na fama da kicin dinta Kanwats kuwa idan ta kulani toh wannan dutsen ya kulani
Aisha dariya ta saki tana karasa shigowa, dukawa ta yi ta ce" ina yini yaya Jamail,
Amsawa yake cike da fara.a , ta juya wajen Wujdane ta shagwabe fuska ta ce" aunty shine kika yi tafiyarki kika barni? Na saba kwana biyu da dawowa da ke har na watsar da abokan tafiyar tawa yau ni kadai na bi hanya ina ta waige
Wujdane ta dan dago, bata da niyar tankawa a yau sanadiyar Jamail dake guri wanda ta radawa natace,
Yana shirin kara tunzurata wayarsa baba ta dauki tsuwa
Da sauri ya zaro ido ya daga
Kafin ya yi magana daga dayan bangaren aka ce" ka zo
Kit aka kashe kiran,
Mikewa yayi yana dan sauri yana salamar su inna da fadin" Inna baban yaya na kirana bara na artaya kar ya daki banza,
Yana fada ne yana kokarin cusa wani abu kasan kwannan ruwan sannan yayi ficewarsa yana dariyar inna na yi masa adu.a har soro
Tuki yake na garari yana adu.ar kar ya kagauta,
Da gudu ya haura ya shige fallon yayan nasa da salama a bakinsa
Zaune yake yana ta faman danna laptop aman wani dan yaro da ba zai fi shekara biyu da ba na ta kokowa da wuyansa da jikinsa, shi kuwa sai dai ya dan kawar da kansa ya ce" boy stop it!
Kamar wanda yake fadin" Boy ka yi kokowar, domin kara makale shi yake
Jamail na shigowa ya san kwannan zancen ya hana shi aiki ne, cikin hikima yake kokarin janye shi a jikin yayan nasa, aman yaron sai ya kuma makale shi yana ihun shi park shi park gashi ranar ranar aiki ce park din ba wani dadi ne da ita ba, du yawanci matan aure ne da yan mata yan school da samarinsu irin masu dan hannu da shunin nan
Kansa ya dafe ya furta " oh goshhh🤦🏻♂
Mikewa ya yi tsaye , dan zuwa bedroom dinsa ya dauko abu, a nan tsayinsa da kirar jikinsa ta bayana, Ya salam, wannan bakin mutun ne a africa ko mai? *ALAIDINE* ba fari bane,
Aman ya fi duka yan uwansa haske, irin fatar nan ce ta yan ethiopia, domin sam ba zaka kiraye shi da bakin mutun ba, Alaidine dogo ne zambak , har ya dara Anwar a tsayi,
Ba zaka taba kusanto jikin Alaidine da rama ba sannan ba irin jikin nan ne mai tumbi ko wani loko loko na kiba ba, aa hasalima jikinsa irin na yan dambe ne, hannunsa a wani murde yake dalilin excercise da yake ba dare ba rana du lokacin da yake jinsa a irin yannayin kadaita ko tunanin rayuwa yakan mike ya shige dakinsa na sports ya zagine ya gurzu , yana gamawa lipton kawai zai dan sha ya konta ya huta domin ba kasafai yake fita aiki ba dan irin mutanen da suke zube shagunnansa ,
Alaidine na da idannuwa masu girma sai dai a ko da yaushe cikin ja suke, sannan akoy shi da rashin tsoron saka idannuwansa cikin na mutun koma waye, hakan ke kayar da gaban mutane da dama
Shin menene tarihin rayuwar wannan familly???????????????
Elhaj Kadri ganninka riba, miji a wajen Hajiya Marwa mahaifan ALAIDINE, ANWAR da JAMAIL,
Hajiya Marwa Ya ce a wajen Elhaj Muhamadu itace auta ita da yar uwarta marigayiya Shafa,
Matarsa daya, wace tayi ta hayayafa cikin ikon Allah tayi ta yin yan bibiyu har sau hudu sannan ta yi daya ta kuma samun su Marwa
Daga Marwa haihuwar ta tsaya sannan su uku kadai ne mata Shafa ta koma ya yi sauran biyu kuma Marwar ce auta
Marwa cikin wani irin gata ta tashi, takan fita ta je makotansu gidan Elhaj Abdallah mahaifin Elhaj Kadri,
Elhaj Abdallah ya ninka Elhaj Muhamadu arziki nesa ba kusa ba, sannan mutun ne mai mutunci yana da sadaka da zaka,
Yayansa biyu kawai maza Elhaj Kadri ne baba sai kanninsa Elhaj Abubakar,
Ragamar kulawa da kasuwancin Elhaj Abdallah a hannun yayansa, sosai yake saka su a hanyar koyan aiki su koyi neman na kansu, sai dai saken yayi mugun yawan da su Elhaj Kadri sukan yi wuta a cikin gari ba laifi
Ja nunfashi ya ce" Alhamdulilah, na san Allah na boye wani lamari a tare da ita, a kulun ina gode masa da ya malaka min ita, sannan ina adu.ar Allah ya shiryar min da ita ya saja mata nutsuwa a duk inda take
Cike da kaunar datakon Malan Anwar ya bada umarnin Balki ta fice ta koma itama gidansu, bayan dogon kashedi da gargadin kar ya kuma gannin kafar wata cikinsu a police station din nan domin ba zasu kwashe lafiya ba,
Haka Balki ta juya har gudu take ta tafi tana godewa Allah da ya takaita tashin hankalin nan
Kallon Wujdane suke gaba dayansu, shi Jamail gaba daya ta gama birge shi, yana son ya ga macen da bata daukan raini, shi kuwa Anwar a wani hali ya shiga, yarinyar ta yi masa fiye da tunanin bawa, kallonta yake a ransa yanai mata adu.ar samun nutsuwa ,
Cike da farin ciki Malan ke yi masu godiya wada ya umarce ta da ta yi wa Anwar da Jamail godiya
Dago da kanta ta yi bayan ta goge fuskarta wanda ya baiwa hannunta damar fitowa , yanda farin fuskarta yake haka na hannunta , faratunanta dogaye ne tsar ,
Idannuwanta ta dago a karo na farko ta sauke su a fuskar Anwar, gashin idannuwanta sun jike da hawaye hakan ya saka suka dan harhade suke kyali tsaf bakinsu ya fito radau, sai zagayen idannuwan ya yi jajajir kamar ya kode domin ba wani kwali a idon,
Murya na rawa ta ce" jazakallah
Bai san lokacin da ya lumshe idannuwansa ba, tamkar sarewa haka muryar ta yi masa rada a kunensa, a hankali ya furta" wa.iyaki
Ky din ya mikawa Jamail dan ya kaisu gida bayan an sha darga da Malan kan abin ya yu yawa, da kyar suka shawo kansa ita kuwa wujdane sai kumbura take tana karawa,
Nan suka bar Anwar zaune ya jinginar da kansa yana ta tunanin to ya aka yi basa kama ko kadan da Malan din,, ?????
Jin tunanin yarinyar zai dame shi ya saka ya mike ya fita ya harhada takardu ya fara dubawa yana kara zagaye police station din
Tafe suke malan na kara yi mata nasiha, cike da kula , Jamail kansa yayi tsam yana sauraro yana mamakin du abin nan da ta aikata malan yanai mata nasiha, uhum da wani uban ne ba mai hana shi dakata
Har suka karaso gidan wanda yara yu suka biyo motar suna ihun jirgi a anguwarsu domin irin motar nan ce mai tsayin nan,
Motar na tsayawa Wujdane ta bude ta fito a bayan ai kamar an watsa su suka fara guduwa ta ko.ina suna ihun walahi *MaMa* da malan ne a motar, du suka warwatse dan mai dukan yaro ce va zata saurara masa ba
Yauma bata tsaya cin abincin daren da su ba, ta fada dakin ta shiga baci
Malan bai fada ma inna ba, sannan bai fadawa kowa maganar ba bayan a titi da Mairo ta dan barbada cewar Wujdane na rufe sai ta yi wata , ganninta ta dawo ya saka ake zuwa har gidan su mairon anai mata ihun makaryaciya ta ji kunya
Da safe kofa ka san fitarta bayan ta shaidawa Aisha cewar ta tafi makaranta dan ta samu ta gama rubuce abubuwan da ya kamata bata da a litafinta
Sai da Malan ya fito take shaida masa ai ta fice makaranta da ya tambaya
Dan jim ya yi sannan ya fice har inna na tambayar lafiyar malan kuwa du wani sukuku take ganinsa???????????????????????
Konci tashi yau wajen sati...........
[3/27, 9:59 AM] +234 803 957 7698: 🦄🦄 *BANI DA ZABI*🦄🦄
*09*
WRINTING BY *SAJIDA*
Da sunnan Allah mai rahama mai jin kai,
*SAJIDARKU CE*
MARUBUCIYAR:
*YAR MAHAUKACIYA*
*DUK KARYAR KADA*
*DAGA TAFIYA DAUKAR SOJA*
*NEMAN NA KAINA*
................... *BANI DA ZABI* INSHA ALLAH....
Wujdane dake konce mamaki fal cikin ranta, mamakin yanda aka yi su malan suka sake da wannan bawan Allah, har wani dan uwanta inna ke cewa, a ina ya zama dan uwan nata????
Cike da jin haushi ta fito jin inna na kuma kiran sunnanta, wannan karin ba nikaf din aman da hijab dinta har kasa
Silbar wajen Malan da a ciki ake zuba masa ruwa idan ya zo domin ya fi kowanne haske ta dauko , ta bude randar cikin dakin inna tsaftataciya da kulun sai ta wanke ta ta juya wani ruwa sanyi karai da kanshi ta zuba masa ta kawo ta ajiye masa
Can gefe ta zauna ta turo baki ta hade fuska ta sada kanta kasa,
Kallonta Jamail yake can kasan zuciyarsa dariya tamkar ta kashe shi, shi kam ba zata bashi wuya ba domin yana zaune da wanda ya fita miskilanci, dan ita idan ta hana kanta abu akoy wa.inda suke tursasata, shi kuwa yaya Alaidine sai dai a hakura dan ko kalonku ba zai yi ba bake ka saka a kokon zuciyarka zai yi abin
A hankali ya ce" kanwata wujdane,
Da gangan ya fadi dan sau goma zai fadi hakan sai ta dago ta watsa masa harara dan ita ta tsani a mayar da ita yarinya, duda ya girme matan ya bata shekara biyu a kala aman sai tana ganin ya raina ta danme ba zai kirayi sunnanta kawai ba
Bata dago da kan ba, sannan bata amsa ba,
Murmushi yake saki na samun nasarar ya hauda ta, zai kara magana Aisha ta shigo da salama
Da fara.a yake mata oyoyo ya ce" lale da mamana,(kamar yanda su Malan ke fada mata), ya ci gaba haba yanzu bakina zai daina tsami kin ga inna na fama da kicin dinta Kanwats kuwa idan ta kulani toh wannan dutsen ya kulani
Aisha dariya ta saki tana karasa shigowa, dukawa ta yi ta ce" ina yini yaya Jamail,
Amsawa yake cike da fara.a , ta juya wajen Wujdane ta shagwabe fuska ta ce" aunty shine kika yi tafiyarki kika barni? Na saba kwana biyu da dawowa da ke har na watsar da abokan tafiyar tawa yau ni kadai na bi hanya ina ta waige
Wujdane ta dan dago, bata da niyar tankawa a yau sanadiyar Jamail dake guri wanda ta radawa natace,
Yana shirin kara tunzurata wayarsa baba ta dauki tsuwa
Da sauri ya zaro ido ya daga
Kafin ya yi magana daga dayan bangaren aka ce" ka zo
Kit aka kashe kiran,
Mikewa yayi yana dan sauri yana salamar su inna da fadin" Inna baban yaya na kirana bara na artaya kar ya daki banza,
Yana fada ne yana kokarin cusa wani abu kasan kwannan ruwan sannan yayi ficewarsa yana dariyar inna na yi masa adu.a har soro
Tuki yake na garari yana adu.ar kar ya kagauta,
Da gudu ya haura ya shige fallon yayan nasa da salama a bakinsa
Zaune yake yana ta faman danna laptop aman wani dan yaro da ba zai fi shekara biyu da ba na ta kokowa da wuyansa da jikinsa, shi kuwa sai dai ya dan kawar da kansa ya ce" boy stop it!
Kamar wanda yake fadin" Boy ka yi kokowar, domin kara makale shi yake
Jamail na shigowa ya san kwannan zancen ya hana shi aiki ne, cikin hikima yake kokarin janye shi a jikin yayan nasa, aman yaron sai ya kuma makale shi yana ihun shi park shi park gashi ranar ranar aiki ce park din ba wani dadi ne da ita ba, du yawanci matan aure ne da yan mata yan school da samarinsu irin masu dan hannu da shunin nan
Kansa ya dafe ya furta " oh goshhh🤦🏻♂
Mikewa ya yi tsaye , dan zuwa bedroom dinsa ya dauko abu, a nan tsayinsa da kirar jikinsa ta bayana, Ya salam, wannan bakin mutun ne a africa ko mai? *ALAIDINE* ba fari bane,
Aman ya fi duka yan uwansa haske, irin fatar nan ce ta yan ethiopia, domin sam ba zaka kiraye shi da bakin mutun ba, Alaidine dogo ne zambak , har ya dara Anwar a tsayi,
Ba zaka taba kusanto jikin Alaidine da rama ba sannan ba irin jikin nan ne mai tumbi ko wani loko loko na kiba ba, aa hasalima jikinsa irin na yan dambe ne, hannunsa a wani murde yake dalilin excercise da yake ba dare ba rana du lokacin da yake jinsa a irin yannayin kadaita ko tunanin rayuwa yakan mike ya shige dakinsa na sports ya zagine ya gurzu , yana gamawa lipton kawai zai dan sha ya konta ya huta domin ba kasafai yake fita aiki ba dan irin mutanen da suke zube shagunnansa ,
Alaidine na da idannuwa masu girma sai dai a ko da yaushe cikin ja suke, sannan akoy shi da rashin tsoron saka idannuwansa cikin na mutun koma waye, hakan ke kayar da gaban mutane da dama
Shin menene tarihin rayuwar wannan familly???????????????
Elhaj Kadri ganninka riba, miji a wajen Hajiya Marwa mahaifan ALAIDINE, ANWAR da JAMAIL,
Hajiya Marwa Ya ce a wajen Elhaj Muhamadu itace auta ita da yar uwarta marigayiya Shafa,
Matarsa daya, wace tayi ta hayayafa cikin ikon Allah tayi ta yin yan bibiyu har sau hudu sannan ta yi daya ta kuma samun su Marwa
Daga Marwa haihuwar ta tsaya sannan su uku kadai ne mata Shafa ta koma ya yi sauran biyu kuma Marwar ce auta
Marwa cikin wani irin gata ta tashi, takan fita ta je makotansu gidan Elhaj Abdallah mahaifin Elhaj Kadri,
Elhaj Abdallah ya ninka Elhaj Muhamadu arziki nesa ba kusa ba, sannan mutun ne mai mutunci yana da sadaka da zaka,
Yayansa biyu kawai maza Elhaj Kadri ne baba sai kanninsa Elhaj Abubakar,
Ragamar kulawa da kasuwancin Elhaj Abdallah a hannun yayansa, sosai yake saka su a hanyar koyan aiki su koyi neman na kansu, sai dai saken yayi mugun yawan da su Elhaj Kadri sukan yi wuta a cikin gari ba laifi