Sashe 4
Bani Da Zabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mairo ta mike ta dauki rigar mamar ta leka ta jikin zanar ta jefa masu tana fadin" banzaye fitinanu, wai fa Adamu ne zai kara aure kuma na budurwa shine ya basu naira dubu dadaya harda dari bibiyu abinda bai taba yi masu a matsayin kishin laifi dan ya kawo amaryarsa, toh shine Hajara ta ajiye nata kudin ta tafi dauko markade kafin ta dawo ta tarar ba dari biyun shine wannan fadan tace ai Lami ce tunda su kasai suka san da kudin sannan da ta fita ba kowa a gidan sai su din, tun safe suke wannan ragabzar mijin ya fice abinsa yayi tafiyarsa, umanmu kuwa ta hane mu da shiga domin tunda adamu ya taba nuna yana son nan nawa suka sha masifa da umanmu sai bama shiga sabgarsu
Wujdane ta tabe baki cike da kyankyannin Adamun kansa, bata cewa Mairon komai ba
Mairo ta saba da halayar kawarta hakan ya saka itama taci gaba da shiryawa tana tayi mata labarai dan karta daina tafiyar
Tunda bus ta ajiye su suke tafe har anguwar sunnan,
Anguwa ce irin ta daidaikun masu hannu da shuni, irin anguwar nan ce dake cakude da masu abin da talakawan
Ja tayi ta tsaya sanadiyar hango gugun samari a kofar gidan
Mairo da ta shan jan baki ta juyo tana kallonta daman ta san a rina wai an saci zanin mahaukaciya domin du dabararka da Wujdane bata bi ta tsakiyar maza koda a idi ne zata rakube ne, aman da mata ne koda sun cika anguwar nan sai ta bi kuma ka tsakwaleta ku daku
Waje ta samu ta zauna gindin wata bishiya tana fadin" sai kin fito
Mairo bata tsaya magiya ba domin ta san kare kukanka ne ba zata bita ba hakan ya saka ta juya kawai ta tafi cikin sake salon tafiya wai ita yan mata🤔
Zaune take tana kallob kasa,tunani take tana fatan su koma kafin yama Yaya Abdul fatah bai dawo ba dan yana da haushinta ( ita bata ma damu da daga fita gaisawa da saurayi ta fice mai gaba daya ba)
Yan mata ne su biyu, sanye da ankin gidan sunnan da wani saurayi a gefensu suna tafe suna labari suna dara na darawa na jin haushi su ji
Wace ke gefe ta juyo da biyar dinta a hannu ta ce" bara na bayar da sadakar biyar nin nan zaifi gyara ni da na je na jefar idan ya so khalifan ya zo nema sai na amsan masa a wajen mama
Saurayin ne yayi dariya ya ce" ke da aka baki ajiya zaki yi kyauta da shi? Bakya gudun rigima ko???
Gaba tayi ta Nufo wajen wujdane itama tana dariyar ta miko tana fadin malama karbi sadaka
Ta maimaita ya kai sau biyar Wujdane na kallon kasa bata dago da kanta ba sannan gaba daya ta nanade kafafuwanta da hannunta a cikin hijabinta baki,
Jin mai maganar taki ta bar wajen ne ya sakata dago da kanta cike da bacin rai ta sauke idannuwanta a fuskar yarinyar
Ihu ta saki ta saki naira biyar din tana fadin" Aljanna wayo aljanna wayo na shiga uku Aljanna
Mutannen dake gefe da wannan saurayin suka yo wajenta suna tambayar a ina aljannar ne,?????
Wujdane da 5ake nunawa suke kallo, wani irin fari tamkar bata da jini a cikin jikinta, sai idannuwanta kalar maciji, wannan saurayin dake tare da su ya shiga janyeta yana fadi tun karfinsa" Inahu sulaimana wa.inahu bismilahi rahamani rahim
Shi kansa ya tsorata da yannayin halitarta, abinka da farin mutun ya saka bakin hijabi,
Du kama guduwa suka yi suka bar wani saurayi shi daya dake kallon Wujdane wada ta cika da takaici
A hankali ya duko ya ce""""""""":""""""""":::"""""""
[3/27, 9:58 AM] +234 803 957 7698: 🦄🦄 *BANI DA ZABI*🦄🦄
*05*
WRINTING BY *SAJIDA*
Da sunnan Allah mai rahama mai jin kai,
*SAJIDARKU CE*
MARUBUCIYAR:
*YAR MAHAUKACIYA*
*DUK KARYAR KADA*
*DAGA TAFIYA DAUKAR SOJA*
*NEMAN NA KAINA*
................... *BANI DA ZABI* INSHA ALLAH....
A wunin ranar nan Wujdane ko kofar gida bata leka ba, tana ta bacin gajiya daman tana fashin sallah
Can da malan ya zo ya tarar da fara.a a fuskar Inna da ya tambayi dalili ya gano ta fara samun kan yar tata ne, cikin murna ya dube ta ya ce" innar Wujdane, koda kinyi kokarin boye soyayarta a zuciyarki a idannuwana bata boyuwa, Allah ya inganta
Kanta ta sada tana murmushi bata ce komai ba, haka ya mike ya leka dakinsu ya tarar har sun yi baci su dukansu kan Aisha na saman cikin Wujdane ya yi masu adu.a ya rufo dakin
Yau ta kama talata, tun karfe bakwai Wujdane ke zaune kofar dakin mahaifinta, kanta a kasa tana dan kallon yanda tsuntsaye ke saukowa su ci geron da innarsu ke zubawa du asuba ta Allah a tsakar gidan hakan ke janyo tsuntsaye kala kala su yi ta ci suna dan waken su
Yau ba bakin hijabin bane a jikinta, kayan makaranta ne irin na Aisha, blue din dogon wando sakake da hijab fari har kasa da riga blue a ciki, gefenta nikaf dinta ne da ya sha wanki kaf jikinta kalkal bata da dati ko kadan,
Malan Laminu ne ya fito da shigarsa na jalabiya fara da rawaninsa dan madaidaici kamar yanda ya saba
Da mamaki yake kallon Wujdane, idan dai ba idannuwansa sun samu matsala bane kayan makaranta ne ta saka, toh aman mai ya canza mata ra.ayinta ne? Ita dake maganar makaranta sai dai a aljannah idan tana cikin bayin da zasu shiga, dalili kuwa shine, a makarantar ya kasance wasu malaman na wawar neman soyayarta, wasun lalata da ita, wasun su tsangwami rayuwarta , haka dalibai idan dai ta fice sai an tsokane ta da zagin mai idannun kurukuru ya na mage, mai farin zabaya da sauransu
Amsa gaisuwarta yake yanda ta kara dukawa har kanta, Wujdane ba dai ba ladabi da biyaya bata da raina mutun koda a waje ne sai idan ka tabota nan fa zaka gane bata da wayo
Tsaye suke da innarsu malan na kallon yanda take zaune bata furta masa muradinta ba, aman shi ba sai ta fada ba tsakanin da da mahaifi fuskarta kadai zai kalla ya gane yarenta
Malan, ni kam ba katsalandan nake son yi ba, aman ka fi kowa sannin halayar Wujdane, nafi kowa murnar ta je makaranta ko dan yawon nan da ta saka a gaba, aman Malan kar ka manta zuwanta na karshe fa, ta yiwa yaya da kanwarta dukan tsiya ta tare hanya sai da aka kirawo ka, malan yara ba zasu daina tsokanarta ba, haka nima nayi rayuwa kai shaida ne, a kauye ma an hana ni zama bale ita a birni? Malan kana gani yaran anguwar nan dan dole suke ce mata MaMa, idan rigimar Wujdane ta fita nesa ba lale ne a yi hakuri da ita ba, ita kuwa ba zata iya mayar da komai ba komai ba ta kawar da kanta har yanzu tamkar wata yarinya karama
Inna ke mitar nan ta dage kan kawai kar ma a soma kai Wujdane Makaranta
Malan ya dago da kansa yana sauraronta, shi kam yana mamakin halayar mata har yanzu, innar yara dai ba wata yarinya karama ba aman cikin ikon Allah du girman mace ana yi ana tarota ne, cikin tausasashiyar murya ya ce" haba innar yara, idan fa hakan na cikin adu.armu na ta nutsu? Ke ganau ce ba jiyau ba Wujdane rabonta da wuni a gida har an manta cikin ikon Allah yau ta farka da muradin komawa makaranta sai a jaraba a gani, ina mai yi miki nuni da a kulun kwanan duniya adu.arki wa Wujdane ita ce abar so ba magana ba, sai mun dawo
Haka ya saka kai Wujdane na biye da shi da Aisha Bayan ta saka nikaf dinta, inna ta yi masu Allah kiyaye ta shiga dan aikacen aikacen cikin gidan cike da zulumin yanda za.a kaya da yarta
A makaranta Malan ya yankawa Malan lamunu kudade wa.inda dole a bayar idan dai ana bukatar Wujdane ta ci gaba da daukan karatu a aji
Bayan dogon nazari ya basu lokaci wanda da yardar Allah zai dawo da wa.innan kudade sannan ya nemi alfarmar ta fara daukan karatu kafin ya cika alkawari da yardar mai duka
Malamin mai mutunci ne, sannan ya san irin kwazon Wujdane, duda yana tsoron dayan halin aman ya yarjewa Malan Aminu ya yiwa Wujdane rakiya har kofar aji sannan ya koma kasuwa dan bubuga abinda ya samu
Du cikin ajin ba mai nikaf, sannan kowa dake zaune sai surutu suke,
Can gefe Wujdane ta samu ta rakube ta sada kanta tana dan juya bironta
Shiru kake ji ajin ya dauka hakan ya saka ta dan dago da kanta,
Malam yusuf ne ya shigo mai koyar masu maths
Rubuce rubuce ya fara a allon makarantar cike da kwarewa yana yi yana kwatanta masu sosai da sosai yanda zasu fahimta
Juyowa yayi yana tambayar ko da wanda bai fahimta ba? Nan ya hango wujdane zaune da nikaf
Cikin yaren turanci ya ce" wannan mai nikaf din fa? Shin bata san dokar makarantar ba cewar ba.a shiga aji da nikaf???
Shiru Wujdane tayi tamkar bata wajen, ko bata san abinda yake nufi ba
Wata yar matashiya mai suna Salima take fada masa cewar bakuwa ce mai yiwuwa bata san abinda yake fadi ba, domin Malan Yusuf akoy rigima sosai bashi da sauki
Cikin bacin rai ya fara fadi yana nufota da hausa cewar" idan har bata iya turanci ba uban me take nema a school din nan kuma ajin nan? Malama ki cire nikaf din idannuwanki mu nan bamu taru a nan dan fuskarki ko wani abin ba,
Cike da kunan rai ta kai hannunta da sauri dan kar ya cire mata ta cire nikaf din kanta a kasa
Tsaki ya ja yana fadin" useless kawai
A hankali Wujdane ta dago da kanta, wani banzan harara ta bala masa wanda ya saka idannuwanta suka yi wuluk da su , ciki ciki take gunaguni wanda Allah kadai ya san mai take fada, ta kada kai ta buda litafinta da niyar rubutu
Wujdane ta tabe baki cike da kyankyannin Adamun kansa, bata cewa Mairon komai ba
Mairo ta saba da halayar kawarta hakan ya saka itama taci gaba da shiryawa tana tayi mata labarai dan karta daina tafiyar
Tunda bus ta ajiye su suke tafe har anguwar sunnan,
Anguwa ce irin ta daidaikun masu hannu da shuni, irin anguwar nan ce dake cakude da masu abin da talakawan
Ja tayi ta tsaya sanadiyar hango gugun samari a kofar gidan
Mairo da ta shan jan baki ta juyo tana kallonta daman ta san a rina wai an saci zanin mahaukaciya domin du dabararka da Wujdane bata bi ta tsakiyar maza koda a idi ne zata rakube ne, aman da mata ne koda sun cika anguwar nan sai ta bi kuma ka tsakwaleta ku daku
Waje ta samu ta zauna gindin wata bishiya tana fadin" sai kin fito
Mairo bata tsaya magiya ba domin ta san kare kukanka ne ba zata bita ba hakan ya saka ta juya kawai ta tafi cikin sake salon tafiya wai ita yan mata🤔
Zaune take tana kallob kasa,tunani take tana fatan su koma kafin yama Yaya Abdul fatah bai dawo ba dan yana da haushinta ( ita bata ma damu da daga fita gaisawa da saurayi ta fice mai gaba daya ba)
Yan mata ne su biyu, sanye da ankin gidan sunnan da wani saurayi a gefensu suna tafe suna labari suna dara na darawa na jin haushi su ji
Wace ke gefe ta juyo da biyar dinta a hannu ta ce" bara na bayar da sadakar biyar nin nan zaifi gyara ni da na je na jefar idan ya so khalifan ya zo nema sai na amsan masa a wajen mama
Saurayin ne yayi dariya ya ce" ke da aka baki ajiya zaki yi kyauta da shi? Bakya gudun rigima ko???
Gaba tayi ta Nufo wajen wujdane itama tana dariyar ta miko tana fadin malama karbi sadaka
Ta maimaita ya kai sau biyar Wujdane na kallon kasa bata dago da kanta ba sannan gaba daya ta nanade kafafuwanta da hannunta a cikin hijabinta baki,
Jin mai maganar taki ta bar wajen ne ya sakata dago da kanta cike da bacin rai ta sauke idannuwanta a fuskar yarinyar
Ihu ta saki ta saki naira biyar din tana fadin" Aljanna wayo aljanna wayo na shiga uku Aljanna
Mutannen dake gefe da wannan saurayin suka yo wajenta suna tambayar a ina aljannar ne,?????
Wujdane da 5ake nunawa suke kallo, wani irin fari tamkar bata da jini a cikin jikinta, sai idannuwanta kalar maciji, wannan saurayin dake tare da su ya shiga janyeta yana fadi tun karfinsa" Inahu sulaimana wa.inahu bismilahi rahamani rahim
Shi kansa ya tsorata da yannayin halitarta, abinka da farin mutun ya saka bakin hijabi,
Du kama guduwa suka yi suka bar wani saurayi shi daya dake kallon Wujdane wada ta cika da takaici
A hankali ya duko ya ce""""""""":""""""""":::"""""""
[3/27, 9:58 AM] +234 803 957 7698: 🦄🦄 *BANI DA ZABI*🦄🦄
*05*
WRINTING BY *SAJIDA*
Da sunnan Allah mai rahama mai jin kai,
*SAJIDARKU CE*
MARUBUCIYAR:
*YAR MAHAUKACIYA*
*DUK KARYAR KADA*
*DAGA TAFIYA DAUKAR SOJA*
*NEMAN NA KAINA*
................... *BANI DA ZABI* INSHA ALLAH....
A wunin ranar nan Wujdane ko kofar gida bata leka ba, tana ta bacin gajiya daman tana fashin sallah
Can da malan ya zo ya tarar da fara.a a fuskar Inna da ya tambayi dalili ya gano ta fara samun kan yar tata ne, cikin murna ya dube ta ya ce" innar Wujdane, koda kinyi kokarin boye soyayarta a zuciyarki a idannuwana bata boyuwa, Allah ya inganta
Kanta ta sada tana murmushi bata ce komai ba, haka ya mike ya leka dakinsu ya tarar har sun yi baci su dukansu kan Aisha na saman cikin Wujdane ya yi masu adu.a ya rufo dakin
Yau ta kama talata, tun karfe bakwai Wujdane ke zaune kofar dakin mahaifinta, kanta a kasa tana dan kallon yanda tsuntsaye ke saukowa su ci geron da innarsu ke zubawa du asuba ta Allah a tsakar gidan hakan ke janyo tsuntsaye kala kala su yi ta ci suna dan waken su
Yau ba bakin hijabin bane a jikinta, kayan makaranta ne irin na Aisha, blue din dogon wando sakake da hijab fari har kasa da riga blue a ciki, gefenta nikaf dinta ne da ya sha wanki kaf jikinta kalkal bata da dati ko kadan,
Malan Laminu ne ya fito da shigarsa na jalabiya fara da rawaninsa dan madaidaici kamar yanda ya saba
Da mamaki yake kallon Wujdane, idan dai ba idannuwansa sun samu matsala bane kayan makaranta ne ta saka, toh aman mai ya canza mata ra.ayinta ne? Ita dake maganar makaranta sai dai a aljannah idan tana cikin bayin da zasu shiga, dalili kuwa shine, a makarantar ya kasance wasu malaman na wawar neman soyayarta, wasun lalata da ita, wasun su tsangwami rayuwarta , haka dalibai idan dai ta fice sai an tsokane ta da zagin mai idannun kurukuru ya na mage, mai farin zabaya da sauransu
Amsa gaisuwarta yake yanda ta kara dukawa har kanta, Wujdane ba dai ba ladabi da biyaya bata da raina mutun koda a waje ne sai idan ka tabota nan fa zaka gane bata da wayo
Tsaye suke da innarsu malan na kallon yanda take zaune bata furta masa muradinta ba, aman shi ba sai ta fada ba tsakanin da da mahaifi fuskarta kadai zai kalla ya gane yarenta
Malan, ni kam ba katsalandan nake son yi ba, aman ka fi kowa sannin halayar Wujdane, nafi kowa murnar ta je makaranta ko dan yawon nan da ta saka a gaba, aman Malan kar ka manta zuwanta na karshe fa, ta yiwa yaya da kanwarta dukan tsiya ta tare hanya sai da aka kirawo ka, malan yara ba zasu daina tsokanarta ba, haka nima nayi rayuwa kai shaida ne, a kauye ma an hana ni zama bale ita a birni? Malan kana gani yaran anguwar nan dan dole suke ce mata MaMa, idan rigimar Wujdane ta fita nesa ba lale ne a yi hakuri da ita ba, ita kuwa ba zata iya mayar da komai ba komai ba ta kawar da kanta har yanzu tamkar wata yarinya karama
Inna ke mitar nan ta dage kan kawai kar ma a soma kai Wujdane Makaranta
Malan ya dago da kansa yana sauraronta, shi kam yana mamakin halayar mata har yanzu, innar yara dai ba wata yarinya karama ba aman cikin ikon Allah du girman mace ana yi ana tarota ne, cikin tausasashiyar murya ya ce" haba innar yara, idan fa hakan na cikin adu.armu na ta nutsu? Ke ganau ce ba jiyau ba Wujdane rabonta da wuni a gida har an manta cikin ikon Allah yau ta farka da muradin komawa makaranta sai a jaraba a gani, ina mai yi miki nuni da a kulun kwanan duniya adu.arki wa Wujdane ita ce abar so ba magana ba, sai mun dawo
Haka ya saka kai Wujdane na biye da shi da Aisha Bayan ta saka nikaf dinta, inna ta yi masu Allah kiyaye ta shiga dan aikacen aikacen cikin gidan cike da zulumin yanda za.a kaya da yarta
A makaranta Malan ya yankawa Malan lamunu kudade wa.inda dole a bayar idan dai ana bukatar Wujdane ta ci gaba da daukan karatu a aji
Bayan dogon nazari ya basu lokaci wanda da yardar Allah zai dawo da wa.innan kudade sannan ya nemi alfarmar ta fara daukan karatu kafin ya cika alkawari da yardar mai duka
Malamin mai mutunci ne, sannan ya san irin kwazon Wujdane, duda yana tsoron dayan halin aman ya yarjewa Malan Aminu ya yiwa Wujdane rakiya har kofar aji sannan ya koma kasuwa dan bubuga abinda ya samu
Du cikin ajin ba mai nikaf, sannan kowa dake zaune sai surutu suke,
Can gefe Wujdane ta samu ta rakube ta sada kanta tana dan juya bironta
Shiru kake ji ajin ya dauka hakan ya saka ta dan dago da kanta,
Malam yusuf ne ya shigo mai koyar masu maths
Rubuce rubuce ya fara a allon makarantar cike da kwarewa yana yi yana kwatanta masu sosai da sosai yanda zasu fahimta
Juyowa yayi yana tambayar ko da wanda bai fahimta ba? Nan ya hango wujdane zaune da nikaf
Cikin yaren turanci ya ce" wannan mai nikaf din fa? Shin bata san dokar makarantar ba cewar ba.a shiga aji da nikaf???
Shiru Wujdane tayi tamkar bata wajen, ko bata san abinda yake nufi ba
Wata yar matashiya mai suna Salima take fada masa cewar bakuwa ce mai yiwuwa bata san abinda yake fadi ba, domin Malan Yusuf akoy rigima sosai bashi da sauki
Cikin bacin rai ya fara fadi yana nufota da hausa cewar" idan har bata iya turanci ba uban me take nema a school din nan kuma ajin nan? Malama ki cire nikaf din idannuwanki mu nan bamu taru a nan dan fuskarki ko wani abin ba,
Cike da kunan rai ta kai hannunta da sauri dan kar ya cire mata ta cire nikaf din kanta a kasa
Tsaki ya ja yana fadin" useless kawai
A hankali Wujdane ta dago da kanta, wani banzan harara ta bala masa wanda ya saka idannuwanta suka yi wuluk da su , ciki ciki take gunaguni wanda Allah kadai ya san mai take fada, ta kada kai ta buda litafinta da niyar rubutu