← Book details A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 111

Sashe 87

A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kasa zama tayi,ta dinga kai kawo a dakinta,tana ganin kamar ta fara sakewa fa da yawa,kamar abbas din yana son canza hali da dabi'a,indai hakanne bai kamata taci gaba da sakewa yarinyar ba,bai kamata taci gaba da ganin haqorinta a waje ba,lallai dole tasa tsananin rashin wasa da rashin sakin fuska a tsakaninsu,amma ta ina zata fara?,duk shi ya cuceta da haramta mata zuwa kaduna,tasan halinsa kuma,yana da wahala kaga fushinsa,amma a duk sanda ya taurare lallai babu mai sakashi ya sauko,sai wata zuciyar ta bata shawarar ta kaiwa hajia ko kawu hassan qorafinta,to amma kuma hakan bamai yiwu bane,tasan babu abinda hakan zai haifar sai tashin tashina,abun qarshe yazo ya juye a kanta,amma kam tabbas ba zata dauki wannan dokar nashi taci gaba da tafiya a haka ba.

Qarfe goma na safe ta motsa,ta bude idanuwanta a hankali ta zubesu kan fuskarsa,ta lumshe su tana sake budesu,wata bala'e'iyar kunyarsa tana saukar mata,sanda ya motsa yana ajjiye magazine din hannunsa ta maida idanunta ta kulle ganin yana niyyar fahimtar ta farka,batasan ya akayi ya gane ba,tadai ji fitar murmushinsa sannan ya sukunya yayi mata rumfa,ya sakar mata lallausan kiss saman tausasan labbanta dake matuqar jan hankalinsa

"Good morning baby doll" cusa kanta tayi cikin cinyarsa cikin wani yanayi najin kunya,yaja numfashi mau nauyi saboda yadda ta sanya kan nata tana sauke masa numfashi mai dumi yana ratsa fatar cinyoyinsa ya tabashi sosai, hannuwansa ya saka ya dagata gaba daya ya sauketa cikin jikinsa,ya mamayeta da hannuwansa duka ta shige jikinsa sosai cikin wani lallausan riqo.

Kasa kasa yake mata magana cikin kunne,kamar wani na a wajen zai iya jinsu

"Yanzun ke babba ce babyn uncle,don Allah ki daina kunyar nan,tun jiya uncle dinki baiji muryarki ba,mommy tace banda musu...... mommmy tace ni mijinki ne......mommy tace ki kula dani kin manta?" Kai ta gyada a hankali,karon farko qaramin murmushi ya qwacewa fuskarta daya tuna mata da mommyn nata

"That's good mommy's girl,say something please,i wanna hear your sweet sweet sweet voice"

"Ina kwana uncle?" Ta fada a mugun shagwabe,zaka dauka tana sane tayi hakan,saidai ko kusa,kawai sound din ya fita a haka ne.

Hannunta guda ya riqe cikin nasa tana murzawa a hankali

"Lafiya lau baby.....ya jikin?,hope kin warware?" Kafada ta maqale masa a narke tana mele baki kamar yadda qaramin yaro keyi duk lokacin da yake shirin sakin kuka,hakan ya bashi damar ganin baby face dinta da kyau,ta sake wani fresh sossaaii,ko wannan shi ake kira da qyallin amarcin da ake fada?,ya raya hakan a ransa

"Har yanzu gurin da ciwo"

"Sosai?"

"Ba sosai ba" ta amsa mishi tana kallon qwayar idanunsa,abinda ya haifar masa da wani sabon feeling mai qarfi a kanta

"Kinsan me za'a yi?" Ya sake fada yana gyara mata zama sosai a jikinsa

"A sake guda daya zaki warke" wani shagwababben kuka daya tasheshi a aiki ta saka,ta fara tuttureshi tana shura qafafuwa,irin yadda takewa ummunta duk sanda rigimarta ta tashi

"Iyeeee,eh lallai babyn uncle ta warke,let's try again" shigewa jikinsa tayi ta qanqameshi tana sake sakar masa kuka,irin wannan shagwabar yakeso ya gani.....irinta yake da buri.....a matsayinsa na police.....He knows hardship,he knows hardness,duk wani nau'i na tsawa bada umarni da seniority shi ya sani yake gani, at least a gidansa yana buqatar soft and cool attitudes which can make him peaceful and calm.

Shuru yayi ba tare da ya lallasheta ba,ya lumshe ido yana jin yadda muryarta ke fita da da wani irin taushi sakalci da kuma quruciya,har sai da yaga bata da niyyar tsagaitawa da gaske ta tsorata,sai ya saki murmushi,ya sunkuya a hankali,ya cusa fuskarsa ta gefan fuskarta ya lalubi kunnenta,cikin rada yake gaya mata wasu.maganganu da suka sanyata jin kunya

"Uncle..... uncle" abinda ta fara fada kenan tana riqe gaban rigarsa da kyau wai zata boye fuskarta a ciki,sai ya saki siririyar dariya ya dagata gaba daya yana cewa

"it's bath time".

Sai da sukayi wanka gaba dayansu ya hada musu breakfast a gurguje sannan ya bata magungunanta tasha.

Komai ya hanata yi,tana daga kwance tana kallo,saidai duk giftarawar da zaiyi saiya bar mata abinda zai sanyata dariya,inda zaka ganshi a lokacin,zaka rantse ba ASP abbas bane,miskilin da ganin haqorinsa ko murmushinsa ke zama wani babban aiki,zaka zaci wani mutum ne can na daban mai kama da abbas din.

Cikin kwanaki biyun gaba da babu inda yaje,suna tare cikin gidan,komai na gidan ya dauke mata,yayi wani irin mugun sakewa da ita matuqa gaya,ya kuma jata jikinsa sosai,a yanzun babban burinsa ya gina rayuwa mai.inganci ya gina rayuwar da zata zame masa madubin gobensa,duk wani abu da yasan tana so,ya kuma fuskanci yana sakata nishadi da walwala shi yakeyi,wani irin tattali da kula yake nuna mata,wani abunma baisan yanayi ba,don yana tasowa ne daga qasan zuciyarsa komai yake tasowa,wani irin yanayi dashi kansa baisan a ina zai ajjiyeshi ba.

Kudi yake zuba mata sosai a waya,tana daga zaune tayita kiran 'yan gida tana shan hira,musamman ummunta da mommynta,kusan ko da yaushe maganar mommyn tabi mijinta,banda musu ko taurin kai,sabawa umarninsa da sauran dukka abubuwan da bayaso,koda yaushe tana gaya masa

"Ki kula dashi,kiyi masa dukkan abinda yakeso,banason na sake jin kowa yaji wani abu da yake gudana a tsakaninku,ko meye zaiyi miki ko ke zakiyi masa,mai dadi ko mara dadi,sirri ne tsakaninku,ki zauna kiyi tunani ki koyi warwarewa da kanki,idan kin gaza ki nemeni" kusan rabi da rabin hirarsu da ita kenan cikin hikima.

Hutun satin ya dauka ganin ba wasu tarin ayyuka sosai a office,saidai lokaci lokaci ya leqa office din yayi awa daya ko biyu ya dawo gida a daddafe,don baya iya haura hakan,sai yaji gaba daya nutsuwarsa da hankalinsa sunyo gidan.

Ita dinma komawa take kamar wata mara lafiya muddin xai fita ya barta a gidan,saidai idan ta fita makaranta,wanda zuwa yanzun da kansa yake jigilar kaita da daukota,bai sake yarda wani ya kaita koya dauko masa ita ba,bayajin zuciyarsa zata iya dauka wannan.

Cikin sati guda ta warware,ta warware da wani irin soyayya da shaquwa dashi sabuwa data ginu a ranta,ya bar mata wani babban tambari da ya kame ilahirin zuciyarta gaba daya ba tare data ankara kota fuskanci meye ba,tasan dai a wannan lokacin tana matuqar son kasancewa tare dashi,tana jin wani farinciki duk lokacin daya zamana yana kusa da ita,suna hira aikin gida ko kuma assignments,tana jinta sukuku cikin rashin sakewa da walwala a duk lokacin da ya zamana ya nesanta da ita.

_cikin wannan yanayin sati biyu da suka biyo baya ya shirya ma zuwa gida weekend,yace ta shirya su wuce tare,don baya jin zai iya barinta har tsahon kwanaki uku ba tare da tana kusa kusa da rayuwarsa ba_

*_muje zuwa dai masu karatu,yanzu takun zai fara daukan zafi_*

*H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Page 80

Tsaye yake gaban mirror yana taje kansa,shirye yake cikin mulberry silk da ya kwanta sosai a jikinsa,ya kuma fidda kyan fatarsa data wadata da tsafta da kuma hutu,jikinsa na fidda sassanyan qamshin turarensa.

A nutse take takowa zuwa qofar dakin nasa,tura qofar a hankali saita tsaya tana kallonsa ta cikin madubin ba tare data saki hannun qofar ba,hakanan bata koma ba bata kuma shigo dakin ba.

Idanu ta zuba masa sosai tana kallonsa,yayi bala'in yi mata wani sassanyan kyau,a yau din quruciya kyansa da haduwarsa sun sake fito mata muraran fiye da ko yaushe, shigar ta karbeshi,duk da dama zaiyi wuya ya saka kaya a jikinsa basu karbeshin ba,ta'ammali da uniform saboda yanayin aikinsa ya sanya yafi mu'amala da manyan kaya akan qanana,saita saki qofar a hankali ta goye hannunta a qirji taci gaba da kallonsa.

A nutse ya sauke idanunsa a kanta,shi dinma shigarta ta yau ta fusgi hankalinsa sosai,abaya ce a jikinta ruby color,saita dora dan qaramin Vail a kayanta dusty rose,dan siririn pink lips dinta na fidda qyallin lipstick data shafa musu, fuskar ta ta kwanta da color din powder din data shafa

"Ma sha Allah" ya fada ta hanyar motsa labbansa,ya ajjiye comb din hannunsa a hankali,yana so yau ne ya kamata real tana satar kallonsa,abinda ya lura fa koya kenan cikin satin nan,idan kuma ya fada saita waske harda qananun hawayen ita ba kallonsa take ba.

Batayi zato ba taga ya waiwayo gaba dayansa,idanunsu suka sarqe cikin na juna,kunya ta kamata,tayi taku biyu baya zata koma ya dakatar da ita

"Don't move baby" yayi maganar muryarsa nadan sarqewa,ganin da yayi mata a yanzu da idanu sai yake ganin kamar madubin ashe ya rage kyan da tayi,turarenta da ko yaushe yake tsaye masa a rai ya iska na kadoshi kadan kadan yana cakuda da nasa yana bayar da wani kalar qamshi na musamman,sai ya cira qafarsa ya soma takawa a hankali zuwa inda take, qafafunsa na nutsewa cikin lallausan carfet din daya malale dakin dashi,bazai iya kauda kai ba a yanzun,yana qishirwa wadan nan labban nata,yanason yaji duminta sosai.......wanda rabonsa da hakan tun randa ya maidata tasa halak malak,duk kuwa da cewa gado daya suke kwana,amma bai sake neman komai daga gareta ba, saboda yana son fidda duk wani sauran tsoro nasa dake ranta.

Qugunta ya kamo da dukka hannayensa biyu ya matso da ita jikinsa sosai har jikin nasa yana gogar nata,gabanta ya fadi sosai ta lumshe ido tana son hadiye tsoronta

"Bude idon na gani..... please my baby" ji tayi ba zata iya tsallake umarninsa ba,sautin muryarsa gaba daya ta kashe mata jiki,ta bude manyan idanuntan fes a kansa,sai yaja numfashi da kyau,yasa yatsunsa biyu ya kama kumatunta yadan ja kadan

"Inason wadan nan idanun,inajin kamar na hadiyesu" ido ta fidda fuskarta na washewa

"Ana cinye idon mutum uncle?" Ta fada a sakarce,sai ya saki murmushi kawai yana tunanin yaushe widad din tashi zata gama girma ne,ya girgiza kansa a hankali,yana jin komai na jikinsa yana amsawa

"Ba'a cinye ido,amma ana iya lasheshi,ana lashe kunne,ana lashe baki ana lashe harsh........"

"Stop uncle,wallahi kunya nakeji" ta fada a narke kamar zata sanya kuka,yadda fuskarta tayi ta sake tafiya da imaninsa,mitsitsin bakinta data turo gaba ya kalla,zuwa yanzun gaba daya burinsa ya tattara a kai,a tausashe yace
Chapter 87 · 0% Book details