← Book details A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 111

Sashe 61

A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Yallabai,da alama kai din ba yayanta bane na hannun dama,ko zaka bamu waje qilan tafiyin bayani" haka kawai cikin ransa yaji bazai iya barinsu su kebe ita dashi ba,don yaga baima fahimci matar aure bace,yayi yunqurin miqewa da nufin matsawa daga koda zuwa bakin window ne,saiji yayi caraf an kamo hannunsa,ya waiwaya a hankali,itace ke kallonsa tana qwalla

"Kada ka tafi please" hada ido sukayi da likitan,sai ya saki dariya sannan ya miqe

"Ta gaya maka abinda takeji,sai kayimin bayani,ina zuwa bari na samo nurse,za'a yi mata scanning,tunda kace ciwon mara ne" sai likitan ya cire abinda ya saqala a wuyansa ya ajjiye ya fice daga office din.

Cikin kunya ta soma qoqarin zame hannunta daga nasa,amma saiya qara matsowa yana sanya dukka tafukan hannunsa a ciki da saman nata,ya rahe gap din dake tsakaninsu sosai yana dubanta

"Uhnnnn.... tell me,kinga idan ya dawo baki fada ba zan tafi na barku tare" qoqarin tsaida kukan nata take tayi,taja majina sannan tace cikin muryar kuka

"Marata ce take ciwo sosai" ta fadi cikin mugun jin kunya

"dai dai ina?" Ya tambayeta yana kallon qwayar idanunta,sai ta motsa hannunta dake mararta kadan,kamar mai tsoron kada ya taba hannun nata.

Idanunsa ya mayar kan hannun nata,sai yasa yatsansa ya nuna wajen

"Wajen nan kenan?' ta gyada kanta a hankali,sai ya dauke dubansa daga wajen yana fidda numfashi,ya miqe a hankali,yayi taku biyu kenan saiga likitan ya dawo,bayansa wata nurse ce,zata kusa shekaru talatin,ba yarinya bace.

Yana dariya ya tambayi abbas me tace?,ya zube hannayensa a aljihun wandonsa yana duban likitan

"Ciwon maranne dai"

"Ba damuwa,da Allah ki mana scanning,bari naje mota na dawo" ya sake fada yana diban wasu takardu ya fice.

Sanda taga an gama saitan scanning machine din tace kuma tahau sai ta fara zare idanu,ganin alamun tana jin tsoro sai nurse din ta dubi abbas

"Yallabai ko zaka taimaka mata" a nutse ya maida dubansa ga widad din,itama shi take kallo,idanun nan har yanzu qwalla ce kwance a ciki,ya cire hannayensa da tun dazun ke aljihunsa,ya tako a nutse ya iso gabanta.

Sosai ua tsugunna a gaban nata,cikin murya qasa qasa, yadda ba wanda zai iya jinsu ya fara magana

"Kije ta dubaki,few minutes ne ta gama miki,ba ciwo ba zafi,just relax...." Baki ta kwabe tana dubansa

"Tsoro nakeji"

"I promise you ba abinda zakiji,muje na rakaki" yadda take a tsorace yasa bata damu da kama hannunta da yayi ba,ya kaita har kan gadon sannan ta kwanta.

"Dage rigar taki" nurse din ta fada tana dauko cream din da zata shafa mata saman cikinta,sai ido ya sake raina fata,matsawa yayi dab da gadon,yasa hannunsa a hankali ya fara janye rigar jikin nata,da hanzari ta riqe tsintsiyar hannunsa,sai suka hada idanu,ya tsareta sosai da manyan idanunsa masu wani irin kaifi da tasiri,ya girgiza mata kai murya kuma can qasa yace

"Nooo,i said just relax" sosai taji idanun nasa sun mata nauyi,saita kauda kanta gefe,hawayen da suka cika idanun nata suna gangarawa ta gefe.

Kamar wanda aka zarewa laka haka ya dage mata rigar har zuwa saman cikinta, kyakkyawar farar fatarta mai sulbi ta bayyana,ya koma a hankali da baya yana jin kamar iska na yawo dashi,ya jingina da wani qaramin locker dake wajen idanunsa nakan saman fatar cikin nata.

*Arewabooks:Huguma*

KI KULANI miss xoxo

DAUDAR GORA Billynabdul

RUMBUN K'AYA hafsat rano

IDON NERA Mamuhghee

A RUBUCE TAKE huguma

_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_

_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_

0022419171
Maryam sani
Access bank

Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070

*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261

*Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number*
+227 96 09 67 63

*Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)

*Arewabooks:Huguma*

Page 55

Da numfashinsa da idanunsa ya dauke lokaci guda sanda taja zanin nata sosai qasan marar tata,har jan pant dinta yana bayyana

"Ya Allah" ya furta yana sake rintse idanunsa,har suka gama bai bude ba sai da yaji nurse din na magana

"Zaki iya tashi?" Ta tambayeta,ya bude idanunsa a hankali ya maida kanta,sai ya taka a hankali zuwa gabanta,ya miqa mata hannunsa,idanunta a qas, karon farko da kunya tayi mata mugun kamu fiye da ko yaushe ta miqa masa hannun nata,ya dagota a tausashe.

Sosai ta zauna saman gadon tana gyara daurin dankwalinta, likitan ya shigo yana qarasawa gaban computer scanning din yana duba scan din data bari a jiki

"Ba wata matsala,zan rubuta mata magunguna,zata samu relief in sha Allah".

Koda suka fito dinma tana riqe a hannunsa,gaba daya ta narke masa,tana ta sharar qwalla,ummu take tunawa da yadda take kula da ita idan bata da lafiya,dan riqetan da yayi sai takejin kamar tana tare da ummun ne,don haka ta narke masa sosai kamar yadda takewa ummu.

Tun a pharmacy din cikin asibitin ya siya magungunan,fruit kawai ya tsaya ya siya a hanya suka wuce gida.

Dakinsa kai tsaye ya wuce da ita,ya shiga kitchen da kansa ya dauko gorar ruwa da cup,ya zuba abinci a plate ya zauna da kansa a gabanta yana dubanta

"Kici abinci,magani zaki sha" kai ta girgiza,fuska yadan hade kadan,ya zama serious,ya debi abincin da kansa yakai bakin bakinta

"Oya....karbi" haka ta dinga bude bakinta yana saka mata abincin,har yanzu hawayenta yaqi tsayawa,duk ta narke,kamar yadda takewa ummu,bai saba daukan shagwaba irin wanna ba,sai ya rasa ta inda zai bi da ita,a haka ya samu tadanci,ya balla mata magungunan ya bata tasha,sannan ya miqe yana kallonta

"Ki huta kadan,sai na rakaki ki kwanta" ya fada muryarsa can qasa,saita gyada kai tana rintse ido,kawai yadda zata tafi dakin ta kwanta ita kadai take hasasowa.

Toilet ya shiga,ya sauya kayansa zuwa jallabiyya mai sulbi saqar qasar india,ya daura alwala,ya dawo cikin dakin ya shimfida abun sallah yana dan duban sashenta,ta sanya pillow daga bayanta,idanunta na a lumshe,amma da alama idanunta biyu,sai ya juya ya kabbara sallarsa.

Tun tana satar kallonsa da kadan da kadan har bacci ya soma rinjayar idanunta,tayita dagewa batason hawa gadon sosai,yana fusgarta tana qwacewa,har yaci qarfinta,ta kwanta riris saman gadon,bacci mai dadi yayi gaba da ita saboda sassaucin ciwon data samu.

Da murmushi akan fuskarsa yake dubanta sanda ya idar da sallar yaga tayi bacci,ya qarasa addu'o'in sa ya sauya kayan baccin sannan ya matso dab da ita,ta ranqwafa saman kanta yana kallon fuskarta sosai da sukayi gab da juna,siraran tausasan labbanta masu kama da an shafa musu ban lebe suka dauki hankalinsa,ya miqa hannu a hankali ya dora saman lips din nata yasa yatsunsa ya shafasu kadan,saita motsa,ta turo baki gaba cikin shagwaba

"Ummu na.....ummu don Allah fa ni...." Ta fadi tana yin juyi,abinda ya sake kawo kusancin dake tsakaninsu sosai har suka fara musayar numfashi,ta haye kusan rabin cinyarsa,ya kalleta yadda tayi relaxing a jikinsa,jikinsa ya bashi idan yace ma zai tasheta ne wata really rigimar ce,don haka kawai sai ya zame ya kwanta,hakan kuwa sai ya zamar mata kamar wata hanya data samu ta shige jikinsa sosai,harda curewa waje daya kamar kwanciyar yaro a cikin mahaifiyarsa,taja hannunsa kuma ta riqe gam tana cewa

"Ummu......na....gode" ajiyar zuciya mai nauyi ya sauke,da alama mafarki takeyi,hakanan ya samu kansa da sake kusanto da ita cikin jikinsa suna musayar dumin juna,ya lumshe idanunsa a hankali yana jin wani abu yana bin jinin jikinsa,zuciyarsa ta fara sauya tsarin bugunta,sannu sannu numfashinsa ya fara sauyawa,ya dinga fita a jejjere,mode dinsa ya canza gaba daya,yasan me jikinsa yakeso,amma bayajin wannan buqatar zata samu,ta yaya ma daga samun kusanci da yarinyar zuciyarsa zata bijiro da wannan babbar buqatar?,bashi da sauran zabi illa qoqarin zameta daya fara yi daga jikinsa,saidai ta riqeshi qam,daga bisani ma da yayi nasarar zameta din,juyi daya tak tayi ta dawo jikinsa,idanunta a rufe amma kukan shagwaba take saki,yayi shuru yana sauraren siririyar muryarta dake fidda wani irin kuka a shagwabe,wanda yake qara sanya tsigar jikinsa zubawa,ya sake rufe idanunsa da kyau yana sake qoqarin zameta a karo na barkatai,amma saita riqo hannunsa,ta kuma cusa kanta cikin qirjinsa sosai.

Duk yadda yaso yayi controlling kansa ya kasa,komai na jikinsa ya gama amsawa,qwaqwalwarsa kuma ta dauki chargy fiye da kima,dukka hannuwansa ya sanya ya jawota cikin jikinsa,shi da ita suka sauke ajiyar zuciya a tare,a hankali ya nutsa hannunsa cikin sassalkar sumarta dake fidda qamshin man kitsonta mai hade da sinadarin menthol me sanyi,cikin sanyi taushi da nutsuwa ya fara yamutsa shi yana jin dukkan wata gaba ta jikinsa tana sake amsawa,abinda ya sanya widad sake sakankancewa cikin baccinta,zuciya da ranta suna bata tana tare da ummu.

A nutse hannunsa ya biyo tsahon gashin nata daya sauka har zuwa gadon bayanta,yana kaiwa qarshe hannunsa ya zarce ta cikin rigarta dake da faffadan baya,lallausan tafin hannunsa ya hadu da fatar bayanta mai santsi da dumi,ya zura hannunsa a hankali yana shafota,idanunsa suna sake nauyi da kyau,zuciyarsa na sake dugunzuma da dokantuwa da samun biyan buqatar ransa,bai gushe ba yana ci gaba da murza fatar bayanta,duk inda yayi qasa da hannunsa zip din na bashi hadin kai wajen zugewa,har yakai can qasa,ya dora hannunsa numfashin sa yana sake gudu kamar wanda yayi tsere,wannan ya sake sanyashi matsa qaimi,ya birkitata a hankali ya soma sabule rigar tata,ya sake dora hannayensa saman wuyanta,hancinsa yana kaiwa wajen,sassanyan qamshin daya zamewa jikinta kamar dabi'a ya zuqa,qamshin da zai iya cewa tunda yake bai taba jin irinsa a jikin hafsat ba,sai yaji bashi da muradin daya wuce yayi sharing qamshin nata da tasa gangar jikin,don haka yasa fuskar sa sosai saman fatar wuyanta,ya kuma fara gangarowa ga qirjinta a hankali yana sauke wani irin birkitaccen numfashi.

A hankali ya fara isowa ga tudun saman qirjinta,abinda ya sanya shi da ita sukaji tamkar an sanya musu wani irin electric shock,ya qanqameta da kyau yana sake zuqar qamshin turaren,yayin da ita kuma taji kamar ance mata tashi!!!,cak kwanyarta ta tsaya waje daya tana son rarrrabe abinda yake faruwa,sanyin daya fara ratsa fatar jikinta ta fahinci saura kadan rigarta ta sauka qasan qirjinta,yunqurin riqe masa hannu tayi cikun matuqar tashin hankali amma ta gaza,saboda yadda jikinsu take rawa gaba daya ita dashi

"Don Allah.....don Allah" ta fara fada cikin mugun rawar murya da kuma kuka,cak ya tsaya kamar wanda aka sanyawa sarqa,ya zame hannunsa daga jikinta a hankali ya mirgina gefe yana fadin
Chapter 61 · 0% Book details