← Book details A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 62 OF 111

Sashe 62

A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Hasbunallahu wani'imal wakil" can qasan maqoshinsa,yayin ruf da ciki yana cusa kansa cikin katifar tare da qoqarin dawo da nutsuwarsa cikin jikinsa.

Tuni takai bango,ta tattare dukka jikinta guri daya,tana riqe da rigarta a hannu qam qam,hawaye sun yiwa fuskarta ado,kuka take sosai cikin tsoro da kuma tashin hankali.

Dakin ya dauki shuru na wasu sakanni,har yanzu kansa na cikin katifar,yana sauraren kukan da take rerawa,wanda ya dinga jinsa har tsakiyar kansa,wani tunani yazo mata,ta soma maida rigarta da sauri sauri,saidai ta gaza zuge zip din,sai kawai ta sauke qafafunta qasan gadon ta miqe ta nufi qofa.

Cikin jikinsa yaji alamun takunta,ya daga rinannun idanunsa da har yanzu basu gama komawa dai dai ba yabita da kallo,duk da dakin ba wadatar haske amma kuma yana iya ganin bayanta daya bayyana sosai saboda rashin zuge zip din,wani irin baya dake dauke da wani shape mai jan hankali daya taimaka wajen fidda shape na mazaunanta da qugunta.

Bayajin koda yayi magana zata fita daga maqoshinsa,don haka ya miqe kawai cikin wata iriyar kasala da mutuwar jiki,kamar wanda yasha abun maye,taku uku ya cimmata,ya isa jikin qofar,ya murza key sannan ya waiwayo ya zube mata idanuwansa gaba daya yana kallonta

"Koma ki kwanta" ya fada da dakusashiyar muryarsa,saita janye gefe tana maqale kafada,bai sake mata magana ta biyu ba,illa hannuwansa daya sanya ya dauketa cak,bai direta ko ina ba sai saman gadon,ya kwantar da ita saman pillow,yaja mata duvet sannan ya sunkuya yana kallon qwayar idanunta sosai

"Sleep......banason na sake jin kukanki,idan kuma kika sake tashi....tom" ya fada yana gyada kansa,alamun akwai abinda zai biyo baya,sai ya matsa yaja da baya,sannan ya juya ya shige bandaki.

Runtse idanunta kawai tayi tana qoqarin danne kukan nata,wani haushinsa da tsanarsa takeji,ashe dan iska ne sosai haka?,tunda take ba wansa ya taba yi mata abinda yayi matan sai shi,boye kanta ta sakeyi sosai cikin duvet din tana share hawayen daketa bulbulowa daga idanunta.

Ya jima cikin toilet din sannan ya kunna ruwan zafi dana sanyi ya daidaita temperature dinsu,ya sakarwa kansa shower,bai taba zaton yarinyar zata kunnashi haka ba,akwai wani irin magnet tattare da ita dake saurin jan zuciya da kuma gangar jiki,yayi shuru ruwan yana gangara a sassan jikinsa,yana tuna qamshi da dumin fatarta,da wani laushi kamar fatar jariri,irin yanayin da yakeso tattare da matarsa,irin yanayin daya jima yana fasaltawa,hannu yasa saman kansa ya sharce sauran ruwan da bai gama diga ba sannan ya fita daga qasan shower din ya samu babbabn towel ya daura ya fito daga bandakin.

Koda ya fito turare kawai ya samu ya shafe jikinsa dashi ya sauya wata rigar,ya koma can daya side na gadon ya zauna yana kallonta yadda take nade waje daya,batayi motsi ba ko kadan,saidai duk da haka ya karanci bacci ya fara daukarta,saidai baccin baiyi nauyi ba,ya sauke ajiyar zuciya ya jingina bayansa da fuskar gadon yana sauke idanunsa kan agogon dake saman bedside yana duba time da date,yana buqatar zuwa bauchi lallai,saidai yau din Monday,zai iya jira har sai ran Friday kuwa?, tambayar da ta masa nauyi,kwanakin kuma yaji sunyi masa nisa da yawa,sai kawai ya jawo wayarsa,ya yanke bari ya kira hafsat din,at least ko hira da zata sake bashi nutsuwa ya samu daga gareta.

KI KULANI miss xoxo

DAUDAR GORA Billynabdul

RUMBUN K'AYA hafsat rano

IDON NERA Mamuhghee

A RUBUCE TAKE huguma

_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_

_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_

0022419171
Maryam sani
Access bank

Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070

*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261

*Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number*
+227 96 09 67 63

*Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)

*Arewabooks:Huguma*

Page 56

Sanda yayi kiran farko har ta katse bata daga ba,bai qosa ba ya sake kira,dab da zata katse aka daga.

Sallama ya fara yi mata,cikin muryar bacci ta amsa

"Badai bacci ba?" Ya tambayeta da muryarsa da ta sake sanyi sosai

"Uhmmm....bacci mana,isan banyi bacci ba me zanyi,ka wuni hidimar gida data yara,kiranka ne ma ya tasheni,da banjin zan tashi har zuwa nan da asuba" idanunsa ya ragewa kaifi kadan,sarkin qorafi da mita,ya kauda wannan a kasalance yace

"Sannu da qoqari"

"Yauwa" ta fada a gajarce

"Ina yaran duka sunyi bacci?"

"Eh" ta sake amsa masa a tsaye

"Good......Allah yayi musu albarka"

"Ameen" ta kuma amsawa a gajarce,shuru na sakanni ya ratsa,ya zaci daga sound dinsa zata karanci wani abu,amma baiga alamun hakan ba,don haka yace da ita

"I missed you, that's why I call you,ko zan samu wani abu special haka who will cheer me up da daren nan" baki ta tabe daga can,zuciyarta na mata zafi,ya ma raina mata wayo ne kawai,me zata masa tunda ya zabi ta zauna a nan?,ai sai kowa ya zauna da lalurarsa

"Kai da kake da amarya?,me zaka nema a wajena?" Duk da baiso ba qaramin murmushi sai daya qwace masa,there is jealousy in her words,bai kuma shirya gamsar da ita ba,don haka yace

"Sister din taki yarinya ce qarama,she can't take all my needs,so dole ki tallafa mata kamar yadda kikacemin zakiyi" idanunta ta runtse tana jin wani ciwo,kamar da gayya abbas din yake gaya mata hakan,yanason ce mata yana samun kulawa daga wajen yarinyar kenan?

"It is better to go back to her" ta fada cikin haqiqancewa

"She's sick" shima ya amsa mata a gajarce,ba dacewa bane ya bata qofan da zata karanci me yake gudana tsakaninsu,wannan wani abu ne daya shafesu su biyu.

Bata shiryawa tashi ta zauna ba amma sai gata a zaune,qirjinta ya buga sosai,me ya sameta?,kodai ya aikata?,indai da gaske bata da lafiya to tabbatar suna tare a yanzu haka,tafi kowa saninsa,yana da tsananin tausayi da kulawa akan iyali,idan baki da lafiya kulawarsa ta musamman ce

"Tana ina?"
"No need ki sani..... just relax me madam" a yadda hankalinta ya daga bata jin zata iya masa komai

"I feel sleepy....so i can't do anything" Maimaita words din data fada din yayi a kunnuwanta sannan yace

"Alright.... good night" sai ya kashe wayar ya ajjiye ta a gefe yana shafa kansa zuwa fuskarsa hadi da furzar da iska,tunani kala daban daban cikin ransa da zuciyarsa,yana ganin kiranta amma sam bashi da interest na dagawa,saboda yana da yaqinij ba ta kirashi don tayi masa abinda yake da buqata bane,wala'alla ma ta kira ne ta bishi da qorafi ko kuma mita.

Kamar yadda ya zata kuwa saiga gajeran tex bayan ta fahimci bazai daga kiran ba

_Na gode da wulaqantani da kayi,ka daga wayar ka bani ita zamuyi magana,i called her,but bata daga wayan itama_

Tsaki yaja ya ajjiye wayar,mamakin halayen hafsat har yau basa barinsa,she call her to tell her what?,a wannan daren?,she refused to do what he wanted amma kuma tana son magana da weedad for what?,baisan sanda zatayi hankali ba da gaske,duk sanda tayi masa irin wannan sake fita takeyi daga ransa,daga qarshe qur'ani ya rungume sannan ya samu bacci ya daukeshi.

*_W A S H E G A R I_*

Ta jima da gama shiryawa cikin uniform dinta,amma ta kasa fitowa,tayi zaune gefan gadonta tana duban fuskarta time to time ta madubi,batasan yadda zata fuskanceshi ba,haushinsa takeji a zahiri,a badini kuma idan ta tuna abinda ya farun jiya sai taji kamar ta nutse a qasa,da qyar ta samu hawayen ta ya tsaya.

Tana jin an taba qofar za'a bude ta runtse idanu,idonsa a kanta,qaramar dariya tana cinsa,yasan wannan rufe idanun duka nasa ne

"Kin fasa zuwa school dinne?" Kai ta girgiza da sauri alamun a'ah,sai ta tashi tana juya masa baya,ta rataya jakarta tayo bakin qofa,a lokacin tuni yabar wajen.

Tayi tsammani Samuel ne zai kaita kamar jiya,sai data shiga motar sannan taga shine ashe,ya tada motar suka fara tafiya,babu wanda ke cewa da dan uwansa komai,har suka isa makarantar,ya cira kudi ya bata

"Ga kudin break,idan an tashi ki jira,idan ban samu zuwa ba samuel zaizo" bata iya hada idanu dashi ba tasa hannu biyu ta karba

"Na gode" ta fadi qasa qasa sannan ta juya da hanzari tana yin hanyar class,yana zaune cikin motar yana kallonta har ta shige sannan ya tada motar yana kada kai da qaramin murmushi kan fuskarsa yayi reverse yabar makarantar.

Wunin ranar sukuku tayishi,don ma 'yan ajin nasu suna da saurin sabo da jan mutum a jiki,nan da nan tadan fara sabawa dasu bayan tasan sunayen wasunsu,da azahar aka tashi,bata tsammaci ganinsa ba still sai gashi,yana sanye da uniform dinsa din nan dake qara masa wani mugun kwarjini haiba da kamala,da suka isa gida ta dauka zaya koma aiki ne,sai taga ya canza kaya ya kirata suka shiga kitchen.

Koda suka gama kowa ya diba nasa,dakinta ta wuce dashi taci a can,bata sake jin motsinsa ba kamar yadda ta wuni a kwance,sai da yamma ya leqo yace tasha magungunta ta shaida masa tasha,hakanan tun bayan magariba daya leqo ya tabbatar tasha maganin dare bata sake jinsa ba.

Wanka tayi tayi shirin bacci kamar yadda ta saba,saidai bacci yaqi zuwan mata,data gaji ta dauki wayarta ta duba,taga tana da kati a ciki sosai,kusan katin tun sanda aka siya wayar yake cikin layin,batasan na nawa ya loda mata haka ba,though dai bata fiya kiran waya ba,mostly saidai ayi kiranta.

Mutanen gida ta dinga kira,ummunta ta fara kira,sai abbanta,anty madina hajjaa sai anty deena,wadda sunfi jimawa da anty deena din,tana ta mata hannunka mai sanda da jirwaye mai kama da wanka akan kula da miji,saidai hankalinta baima wani kawo mata ba,tadai jita ne,sai kusan tara na dare sannan sukayi sallama.

Sam bacci ya qauracewa idanunta,ta dinga juyi ita daya tana tuna daren jiya,rabon da tayi cikakken baccin mai dadi irin na jiya har ta manta,saboda ita din mutum ce da tayi sabo da kwana a jikin ummu,shi yasa a kullum idan zatayi bacci da qyar yake zuwa mata tun bayan tafiyar latifa.

Karar wayarta ta katse mata tunaninta,har tadan tsorata ma saboda ta manta da ita,sunan mommy hafsat data gani ya sanyata tashi ta zauna ba shiri,gabanta yayi mugun faduwa,hakanan takejin mummunan faduwar gaba a duk sanda taga wani abu daya danganceta,kamar sunanta muryarta da sauransu.

Muryarta na dan rawa ta daga wayar tana sallama tare da yunqurin gaisheta
Chapter 62 · 0% Book details