Sashe 20
A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
_wannan kenan_
Kwanaki biyu suka qara suka gama shirinsu,har zuwa lokacin yana mamakin abinda ya sauya mata ra'ayin binsa kadunan,saidai bai matsa da sai ya sani ba,tunda zurfafa binciken a wadansu lokuttan ba alkhairi yake haifarwa ba.
Ana gobe zasu tafi ya sanyata ta shirya don suje su yiwa hajiya sallama,daga nan kuma ya sauketa a gidansu,tana ta qoqarin danne zuciyarta ne,da kuma bin dukka abinda yakeso,saboda bataso ta bata hanyar data fara sharewa kanta,don antyn ummee tana ta jan kunnenta kan sai tayi juriya,kuma saita kula,don haka ta shirya ta bishi.
Hannu bibbiyu hajiyan ta karbeta kamar yadda ta saba,cikin kirki da karamcin nan nata,ba laifi hafsat din kadaran kadaham itama,har suka gama gaisawar suka taba hira sama sama,saita miqe tana duba agogo gami da kallonsa
"Inaga ya kamata ka saukeni a gidan,lokacin yana tafiya" kansa ya dauke daga kan jaridar da yake dubawa ya kalleta,har ya buda baki zaiyi magana hajiyan ta rigashi
"Gaskiya kam,kuma sallama zakuyi ya kamata ace kinje da wuri don ki samu isashen lokaci,tashi ka sauketa abbas" baice uffan ba,saboda maganar hajiya gaba take da maganar kowa a fadin duniya,banda haka xamanta a gidan yayi kadan sosai,duka duka ko awa guda bata rufa ba,sai ya ajjiye jaridar ya miqe yana daukan key din motar sa ya fice,ta yiwa hajiya sallama,ita kuma tasa muneera ta bita da kayan amfanin kitchen data tanadar musu,kamar su kuka kubewa daddawa kanwa da yaji da sauransu,saboda tasan abbas din ma'abocin son tuwo ne,a halayya kuma irin ta hafsat din babu lallai ta tsaya tunanin tanadarsu,ta bisu da addu'a suka lafiya,qwaqwalwarta fal mamakin yadda hafsat din ta sauya ra'ayi,duk da bata tsaya tambayar abbas din ba.
***********
Gab da sallar magariba hajjaa ta iso gidan hajiyan,cike da gajiya da kuma farincikin gama cooking classe din da sukayi na kwanaki biyar,wanda dai dai yake da na kwanaki sittin a wata makarantar,ita kanta tasan ta qaru over da abubuwa masu yawa.
Tana shiga ta miqawa nujood jakarta ta daura alwala kawai sannan ta shige falon hajiyan,ta zauna suka gaisa hajiyan tayi mata sannu,sannan ta kira muneera kan ta zubo abincin dare suci kafin su wuce
"Hajiya da kin barsu,yauma kafin na fito sai da nayi girki"
"Me yasa kike nuna wa gidan nan kamar ba gidanku bane hadiyya?,kinga muneera zubo,idan ba zata ci ba yaran zasu ci,xakuci ai ko widad?" Tayi tambayar tana kallon widad,wadda keta faman hada kayansu a jaka tana kammalewa.
Murmushi ta saki tana sadda kanta qasa,ba tare data amsawa hajiyan ba
"Au,babarki zaki goyawa baya kenan,sai faman hada kaya kike,kamar dama kin gaji da zuwa gidanmu " wannan karon har sai da haqoranta suka fito tana dariya cike da kunya
"Ba haka bane hajiya,muna ta saki aiki fa kwama biyar din nan,kema zaki huta" maganar yarinyar saita burgeta,ta kuma sake saka mata qaunarta a zuciyarta,haka kawai cikin kwanakin taji yarinyar ta kwanta mata,tana kuma burgeta,saboda taga bambancin dabi'a tsakaninta da sauran yara,sau tari takan zauna nan kusa da hajiyan suyita hira abinsu,widad din najin hajiya kamar ummunta,idan tana tare da ita sai taji kamar ummu,tana debe mata kewarta sosai.
"Ni ai ban gaji da ganinku ba widad"
"To mu zauna hajiya?" Ta tambayeta cike da quruciya,murmushi hajiyan ta sake,ta waiwaya tana duban hajjaa dai dai sanda ta sallame daga sallar
"nikam da zaku bani widad da nayi murna na kuma gode muku" dariya hajjaa ta saki,ba tare daga fahimci abinda hajiya ke nufi ba,ta zare hijabinta tana cewa
"Widad hajiya?,wannan mara sabo din da rashin sakewa da mutane?,idan muka baki widad ai mun gayyatowa kanmu ummu,takanas zata tahi bauchi ta dauke kayarta,dama 'yar aro ce" kai hajiya ta kada
"Ni ba aro nakeso a bani ita ba,inaso a bani ita na baiwa abbas dina,kinga shikenan ta zama diyata babu zancan aro kuma" a yadda hajiyan tayi maganar yasa hajjaa maido hankalinta jikinta,ta kalli fuskar hajiyan da kyau,sai taga gaskiya baro baro kwance saman fuskarta,kalamanta sunyi kama da kalaman da suke fita daga can qasan zuciya,babu alamun wasa ko kakaci a ciki.
Daurewa hajjaa tayi tayi murmushi,don zancan gaba daya sanyayar mata da jiki yayi,abbas hajiya ke magana,dan gayun matashin nan, mahaukacin damarar nan da kwanan nan aka qara masa rank?,abbas din dake da mata da yara biyu?,,abbas fa
"To ai hajiya idan kinaso sai a bakin ai"
"So kai,saboda inaso dinne ma na sako zancan,amma dai zan sake tuntubarki,ki shaidawa muhsin din"
"To hajiya ba matsala" ta fada tana murmushi,zuciyarta na bata da wasa hajiyan tayi maganar,saita maida dubanta ga widad wadda tuni ta matsa gaba suna magana da nujood,don haka batasan ma wainar da ake toyawa ba.
Sanda suka tashi tafiyar kayan ciye ciye ta hada musu da yawa a leda,hajiyan 'yar gatan tsohuwa ce,babu abinda ta rasa a gidanta,wannan ya sanya babu abinda zakaje baka samu ba a gidan.
*BAYAN SATI DAYA*
Tsaye take hadiyya take cikin kitchen din tana hadawa uncle muhsin abincinsa,gefe daya yaranne gaba daya sun cika mata kunne,hayaniya suketa yi suna tsokanar widad,wadda gaba daya cikin satin ta fara birkice musu,tunda tayi waya da ummun ta gaba daya hankalinta ya karkata zuwa komawa gida
"Ya isa don Allah kuyi mana shuru" waiwaya tayi ga widad
"Zan gayawa uncle dinki kada ki damu,zai kaiki kiga ummun da kansa indai free yake bashi da aiki" kai ta gyada tana danjin relief a ranta,a kwanakin nan ji take kamar tayi tsuntsuwa ta ganta gaban ummun,bata taba zaton akwai abinda zai kawo rabuwarsu haka na tsahon lokaci ba,tama yi qoqari,don ko kwana guda batayi gidan kowa indai ba tare da ita ba,sai gashi yau ta doshi wata kusan guda cur.
Sanda hajjaa ta isa yana amsa waya ne,saita zuba masa komai ta kuma jera a gabansa,tana niyyar tashi don ta koma kitchen din ta sallami yaran yayi mata nuni da hannu kan ta zauna,saita koma ta zauna din,ya kammala wayarsa ya kashe yana dubanta
"Wanne saqo hajiyan abbas ya baki baki gayamin ba?" Cikin mamaki don ita sam ta ajjiye wannan batun tace
"Saqo kuma?,anya kuwa?"
"Gashi yanzun ta kirani tana tambayata,tace idan kin kammala gayamin din zata sake kirana" sai a sannan hankalinta yakai,tadan dafe kanta tana fadin
"Ya salam,wallahi sai da kazo da maganar na tuna" kansa ya girgiza
"Bai kuma.kamata ba,hajiya kamar uwa take a wajenmu gaba daya"
"Ba haka bane abba,zancan ne naji kamar zolaya take yi,hankali na bai kama ba" ta fada tana kada kai
"Wanne irin zance ne haka?" Uncle muhsin da ya fara cin abincinsa ya fada yana kallonta
"Widad takeso a basu ta baiwa abbas aurenta"
*_AREWABOOKS: Huguma_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
*DAUDAR GORA*🔥
*IDON NERA*🔥
*A RUBUCE TAKE*🔥
*KI KULANI*🔥
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*🔥🔥🔥🔥🔥
0022419171
Maryam sani
Access bank.
Shaidar biya tanan👇🏻
09033181070
*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+227 90 16 59 91
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*
*Thanks for choosing us*🔥
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:huguma*
Page 18
Shi kansa zancan yazo masa a bazata,sai ya ajjiye spoon din hannunsa yana duban hajjaa
"Abbas....abbas nawa fa" kai ta gyada
"Eh shi" kamar me jiran hajjaa ta tabbatar masa da batun sai ga kiran hajiya ya sake shigowa wayarsa,ya kalli wayar na wasu sakanni zuciyarsa na gaya masa da gaske hajiyan take,tunda har ta kasa sakat saita samu tabbacin isar saqon kunnensa,ya dauka wayar a nutse ya kara a kunnensa
"Ina fata saqon nawa ya riskeka?" Kai ya gyada kamar tana gabansa
"Eh hajiya,yanzun take isarmin dashi"
"To alhamdulillah" ta fadi tana sauraren ji daga gareshi
"Amma hajiya....wani hanzari ba gudu ba,kina ganin babu matsala daga wajen shi abbas din?" Yayi tambayar saboda sanin halin abokin nasa,sun jima a tare tun zuwanshi bauchi,duk da cewa ya girmewa abbas din,amma suna tare dashi,don itama dama abota ba sai da sa'anka ba,takan iya zuwa ta kowacce fuska,Itama hajiyan kai ta kada kamar yana wajen
"Bani da haufi akan abbas ko kadan,bamu ita din shine mai wuyar" sosai hajiyan ta aza masa nauyin da bazai iya kufcewa ba,tana masa kallon mazaunin uba a wajen widad,tasan kuma ya isa ya zartar da hukunci a kanta shi yasa ta nemeshi kai tsaye,uwa uba kuma abbas din wani irin mutum ne mai kima da daraja a wajensa,yafi kowa sanin irin qaunar da yakema mahaifiyarsa,kamar yadda ta dauki shi shima a mazaunin d'a,bai kyautu ya dubi tsabar qwayar idanunta yace mata bazasu bada auren widad ga abbas din da yana sahun farko farko na wadanda zasu bada shaidar kyawun hali da nagartarsa,bayan gajeran nazarin da bai wuce shurun sauraren hajiyar ba ya amsa mata
"Hajiya ai abbas nawa ne,babu damuwa,an bashi widad,zan kuma sanar da can gida in sha Allah". Irin addu'ar da yaji hajiyan tana kwararo masa sai da abin ya bashi mamaki,wanne irin so take mata haka?,lallai da bai amsa ba Allah ne kadai yasan rashin dadin da zataji,duk da ba zata nuna masa ba.
Wayar ya ajjiye gefe,ya daga kai yana duban hajjaa data tsareshi da idanu,kafin yace komai ta rigashi
"Abbaa,aure fa kake bayarwa,auren widad din da ummu ta baka aronta?,ba tare da sahalewar ummu ko yaaya mahmud ba?" Dan gajeran murmushi ya saki
"Yadda zan bada auren nujood kai tsaye babu haufi haka zan bada na widad,ina da wannan license din"
"Amma kana ganin aurenta da abbas yayi dai dai?" Ta sake tambayarsa cikin jin d'ar d'ar da fargaba
"Yana da wani aibune da musulunci yace idan namiji yana dashi bai cancanci ku bashi auren diyarku ba?" Kai ta girgiza da sauri
"Ko kadan,abbas nagartaccen mutum ne mai kyawawan dabi'u abun kwaikwayo,amma abba kada fa ka manta yana da mata,sannan matarsa din nan ko kwanaki na danji ana kuka da ita,bata da kirki abba,zamansu da widad mai qananun shekaru a mazaunin kishiya zai yiwu?"
Kwanaki biyu suka qara suka gama shirinsu,har zuwa lokacin yana mamakin abinda ya sauya mata ra'ayin binsa kadunan,saidai bai matsa da sai ya sani ba,tunda zurfafa binciken a wadansu lokuttan ba alkhairi yake haifarwa ba.
Ana gobe zasu tafi ya sanyata ta shirya don suje su yiwa hajiya sallama,daga nan kuma ya sauketa a gidansu,tana ta qoqarin danne zuciyarta ne,da kuma bin dukka abinda yakeso,saboda bataso ta bata hanyar data fara sharewa kanta,don antyn ummee tana ta jan kunnenta kan sai tayi juriya,kuma saita kula,don haka ta shirya ta bishi.
Hannu bibbiyu hajiyan ta karbeta kamar yadda ta saba,cikin kirki da karamcin nan nata,ba laifi hafsat din kadaran kadaham itama,har suka gama gaisawar suka taba hira sama sama,saita miqe tana duba agogo gami da kallonsa
"Inaga ya kamata ka saukeni a gidan,lokacin yana tafiya" kansa ya dauke daga kan jaridar da yake dubawa ya kalleta,har ya buda baki zaiyi magana hajiyan ta rigashi
"Gaskiya kam,kuma sallama zakuyi ya kamata ace kinje da wuri don ki samu isashen lokaci,tashi ka sauketa abbas" baice uffan ba,saboda maganar hajiya gaba take da maganar kowa a fadin duniya,banda haka xamanta a gidan yayi kadan sosai,duka duka ko awa guda bata rufa ba,sai ya ajjiye jaridar ya miqe yana daukan key din motar sa ya fice,ta yiwa hajiya sallama,ita kuma tasa muneera ta bita da kayan amfanin kitchen data tanadar musu,kamar su kuka kubewa daddawa kanwa da yaji da sauransu,saboda tasan abbas din ma'abocin son tuwo ne,a halayya kuma irin ta hafsat din babu lallai ta tsaya tunanin tanadarsu,ta bisu da addu'a suka lafiya,qwaqwalwarta fal mamakin yadda hafsat din ta sauya ra'ayi,duk da bata tsaya tambayar abbas din ba.
***********
Gab da sallar magariba hajjaa ta iso gidan hajiyan,cike da gajiya da kuma farincikin gama cooking classe din da sukayi na kwanaki biyar,wanda dai dai yake da na kwanaki sittin a wata makarantar,ita kanta tasan ta qaru over da abubuwa masu yawa.
Tana shiga ta miqawa nujood jakarta ta daura alwala kawai sannan ta shige falon hajiyan,ta zauna suka gaisa hajiyan tayi mata sannu,sannan ta kira muneera kan ta zubo abincin dare suci kafin su wuce
"Hajiya da kin barsu,yauma kafin na fito sai da nayi girki"
"Me yasa kike nuna wa gidan nan kamar ba gidanku bane hadiyya?,kinga muneera zubo,idan ba zata ci ba yaran zasu ci,xakuci ai ko widad?" Tayi tambayar tana kallon widad,wadda keta faman hada kayansu a jaka tana kammalewa.
Murmushi ta saki tana sadda kanta qasa,ba tare data amsawa hajiyan ba
"Au,babarki zaki goyawa baya kenan,sai faman hada kaya kike,kamar dama kin gaji da zuwa gidanmu " wannan karon har sai da haqoranta suka fito tana dariya cike da kunya
"Ba haka bane hajiya,muna ta saki aiki fa kwama biyar din nan,kema zaki huta" maganar yarinyar saita burgeta,ta kuma sake saka mata qaunarta a zuciyarta,haka kawai cikin kwanakin taji yarinyar ta kwanta mata,tana kuma burgeta,saboda taga bambancin dabi'a tsakaninta da sauran yara,sau tari takan zauna nan kusa da hajiyan suyita hira abinsu,widad din najin hajiya kamar ummunta,idan tana tare da ita sai taji kamar ummu,tana debe mata kewarta sosai.
"Ni ai ban gaji da ganinku ba widad"
"To mu zauna hajiya?" Ta tambayeta cike da quruciya,murmushi hajiyan ta sake,ta waiwaya tana duban hajjaa dai dai sanda ta sallame daga sallar
"nikam da zaku bani widad da nayi murna na kuma gode muku" dariya hajjaa ta saki,ba tare daga fahimci abinda hajiya ke nufi ba,ta zare hijabinta tana cewa
"Widad hajiya?,wannan mara sabo din da rashin sakewa da mutane?,idan muka baki widad ai mun gayyatowa kanmu ummu,takanas zata tahi bauchi ta dauke kayarta,dama 'yar aro ce" kai hajiya ta kada
"Ni ba aro nakeso a bani ita ba,inaso a bani ita na baiwa abbas dina,kinga shikenan ta zama diyata babu zancan aro kuma" a yadda hajiyan tayi maganar yasa hajjaa maido hankalinta jikinta,ta kalli fuskar hajiyan da kyau,sai taga gaskiya baro baro kwance saman fuskarta,kalamanta sunyi kama da kalaman da suke fita daga can qasan zuciya,babu alamun wasa ko kakaci a ciki.
Daurewa hajjaa tayi tayi murmushi,don zancan gaba daya sanyayar mata da jiki yayi,abbas hajiya ke magana,dan gayun matashin nan, mahaukacin damarar nan da kwanan nan aka qara masa rank?,abbas din dake da mata da yara biyu?,,abbas fa
"To ai hajiya idan kinaso sai a bakin ai"
"So kai,saboda inaso dinne ma na sako zancan,amma dai zan sake tuntubarki,ki shaidawa muhsin din"
"To hajiya ba matsala" ta fada tana murmushi,zuciyarta na bata da wasa hajiyan tayi maganar,saita maida dubanta ga widad wadda tuni ta matsa gaba suna magana da nujood,don haka batasan ma wainar da ake toyawa ba.
Sanda suka tashi tafiyar kayan ciye ciye ta hada musu da yawa a leda,hajiyan 'yar gatan tsohuwa ce,babu abinda ta rasa a gidanta,wannan ya sanya babu abinda zakaje baka samu ba a gidan.
*BAYAN SATI DAYA*
Tsaye take hadiyya take cikin kitchen din tana hadawa uncle muhsin abincinsa,gefe daya yaranne gaba daya sun cika mata kunne,hayaniya suketa yi suna tsokanar widad,wadda gaba daya cikin satin ta fara birkice musu,tunda tayi waya da ummun ta gaba daya hankalinta ya karkata zuwa komawa gida
"Ya isa don Allah kuyi mana shuru" waiwaya tayi ga widad
"Zan gayawa uncle dinki kada ki damu,zai kaiki kiga ummun da kansa indai free yake bashi da aiki" kai ta gyada tana danjin relief a ranta,a kwanakin nan ji take kamar tayi tsuntsuwa ta ganta gaban ummun,bata taba zaton akwai abinda zai kawo rabuwarsu haka na tsahon lokaci ba,tama yi qoqari,don ko kwana guda batayi gidan kowa indai ba tare da ita ba,sai gashi yau ta doshi wata kusan guda cur.
Sanda hajjaa ta isa yana amsa waya ne,saita zuba masa komai ta kuma jera a gabansa,tana niyyar tashi don ta koma kitchen din ta sallami yaran yayi mata nuni da hannu kan ta zauna,saita koma ta zauna din,ya kammala wayarsa ya kashe yana dubanta
"Wanne saqo hajiyan abbas ya baki baki gayamin ba?" Cikin mamaki don ita sam ta ajjiye wannan batun tace
"Saqo kuma?,anya kuwa?"
"Gashi yanzun ta kirani tana tambayata,tace idan kin kammala gayamin din zata sake kirana" sai a sannan hankalinta yakai,tadan dafe kanta tana fadin
"Ya salam,wallahi sai da kazo da maganar na tuna" kansa ya girgiza
"Bai kuma.kamata ba,hajiya kamar uwa take a wajenmu gaba daya"
"Ba haka bane abba,zancan ne naji kamar zolaya take yi,hankali na bai kama ba" ta fada tana kada kai
"Wanne irin zance ne haka?" Uncle muhsin da ya fara cin abincinsa ya fada yana kallonta
"Widad takeso a basu ta baiwa abbas aurenta"
*_AREWABOOKS: Huguma_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
*DAUDAR GORA*🔥
*IDON NERA*🔥
*A RUBUCE TAKE*🔥
*KI KULANI*🔥
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*🔥🔥🔥🔥🔥
0022419171
Maryam sani
Access bank.
Shaidar biya tanan👇🏻
09033181070
*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+227 90 16 59 91
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*
*Thanks for choosing us*🔥
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:huguma*
Page 18
Shi kansa zancan yazo masa a bazata,sai ya ajjiye spoon din hannunsa yana duban hajjaa
"Abbas....abbas nawa fa" kai ta gyada
"Eh shi" kamar me jiran hajjaa ta tabbatar masa da batun sai ga kiran hajiya ya sake shigowa wayarsa,ya kalli wayar na wasu sakanni zuciyarsa na gaya masa da gaske hajiyan take,tunda har ta kasa sakat saita samu tabbacin isar saqon kunnensa,ya dauka wayar a nutse ya kara a kunnensa
"Ina fata saqon nawa ya riskeka?" Kai ya gyada kamar tana gabansa
"Eh hajiya,yanzun take isarmin dashi"
"To alhamdulillah" ta fadi tana sauraren ji daga gareshi
"Amma hajiya....wani hanzari ba gudu ba,kina ganin babu matsala daga wajen shi abbas din?" Yayi tambayar saboda sanin halin abokin nasa,sun jima a tare tun zuwanshi bauchi,duk da cewa ya girmewa abbas din,amma suna tare dashi,don itama dama abota ba sai da sa'anka ba,takan iya zuwa ta kowacce fuska,Itama hajiyan kai ta kada kamar yana wajen
"Bani da haufi akan abbas ko kadan,bamu ita din shine mai wuyar" sosai hajiyan ta aza masa nauyin da bazai iya kufcewa ba,tana masa kallon mazaunin uba a wajen widad,tasan kuma ya isa ya zartar da hukunci a kanta shi yasa ta nemeshi kai tsaye,uwa uba kuma abbas din wani irin mutum ne mai kima da daraja a wajensa,yafi kowa sanin irin qaunar da yakema mahaifiyarsa,kamar yadda ta dauki shi shima a mazaunin d'a,bai kyautu ya dubi tsabar qwayar idanunta yace mata bazasu bada auren widad ga abbas din da yana sahun farko farko na wadanda zasu bada shaidar kyawun hali da nagartarsa,bayan gajeran nazarin da bai wuce shurun sauraren hajiyar ba ya amsa mata
"Hajiya ai abbas nawa ne,babu damuwa,an bashi widad,zan kuma sanar da can gida in sha Allah". Irin addu'ar da yaji hajiyan tana kwararo masa sai da abin ya bashi mamaki,wanne irin so take mata haka?,lallai da bai amsa ba Allah ne kadai yasan rashin dadin da zataji,duk da ba zata nuna masa ba.
Wayar ya ajjiye gefe,ya daga kai yana duban hajjaa data tsareshi da idanu,kafin yace komai ta rigashi
"Abbaa,aure fa kake bayarwa,auren widad din da ummu ta baka aronta?,ba tare da sahalewar ummu ko yaaya mahmud ba?" Dan gajeran murmushi ya saki
"Yadda zan bada auren nujood kai tsaye babu haufi haka zan bada na widad,ina da wannan license din"
"Amma kana ganin aurenta da abbas yayi dai dai?" Ta sake tambayarsa cikin jin d'ar d'ar da fargaba
"Yana da wani aibune da musulunci yace idan namiji yana dashi bai cancanci ku bashi auren diyarku ba?" Kai ta girgiza da sauri
"Ko kadan,abbas nagartaccen mutum ne mai kyawawan dabi'u abun kwaikwayo,amma abba kada fa ka manta yana da mata,sannan matarsa din nan ko kwanaki na danji ana kuka da ita,bata da kirki abba,zamansu da widad mai qananun shekaru a mazaunin kishiya zai yiwu?"