Sashe 22
A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Am sorry to say no" ya fada yana maida murfin motar a hankali ya rufe,sannan ya tashi motar yayi reverse suka fice daga wajen.
"Har yanxu kana lokaci mutumina,bansan me yake fusgar hankalinsu ba haka,adan bani sirrin mana" ya fuskanci sarai abinda suraj yake fada,fuskarsa kadaram kadaham ya waiwayo kadan ya dubeshi sannan ya maida kansa ga titi
"Kai har yanzu baka girma na suraj,ana ta neman na abincin da za'a kaiwa iyali kuma wa yake ta wannan" ya fada yana shafar habarsa dake zagaye da gemun daya samu wadataccen tsafta da gyara
"Banga alama ba,don duk sanda muka fito irin haka sai wata ta taya"
"To ai sai suyita yi,ta gidanma ya ka cika da ita bare ka sake daukan wata,kayita hadama kanka rigima da zafi,bazan iya daukan wannan ba"
"Fada dai kake,bari ayi katari da wadda zata sace maka zuciya"
"Haka kake gani" abbas ya maida masa amsa,hankali da idanunsa naga titi.
Dariya kawai Suraj yayi,bai sake cewa komai ba suka shiga wata hirar.
Sai daya fara sauke suraj a gida bayan ya hadashi da tashi ledar sannan ya koma gidan hajiyan.
Bayan isha'i ya zauna sukaci abinci,kusan tare da hajiyan,saidai kowa kwanonsa daban,bayan sun kammala ya dauke kwanukan da kansa ya tattare wajen sannan ya dawo ya zauna yana fuskantar hajiyan
"Hajiya kince zamuyi magana ko?" Gyara zamanta tayi sosai
"Eh tabbas"
"To ina jinki,Allah yasa ba wani laifi nayi ba" murmushi ta sake
"Laifi abbas?,a'ah ko kadan,wani alkhairi na hango maka,na kumayi karambanin zartar maka dashi ba tare dana tuntube ka ba" qaramin murmushi ya saki
"Hajiya...ai kinfi qarfin ki yiwa rayuwata karambani,kome kika ga dama ki zartar dashi kanki tsaye kawai" kai ta dan jinjina sannan tace
"Aure na nema maka,'yar uwa ko 'yar muhsin" sosai gabansa ya fadi,abinda ya jima baiji irinsa ba tsahon rayuwarsa
"Hajiya nujood?" Ya fada cikin fargaba,don ko da ya kasance itace bazai iya musawa hajiyan ba,haka zai auretan,yarinyar dake kallonsa a mazaunin ubanta
"A'ah,widad" ajiyar zuciya ya sauke,sai yaji tashin hankalin da yake ciki din ya ragu,ya samu 'yar nutsuwa,duk da fahimci wa take nufi din ba,amma dai ya fahimci wata ce daban ba nujood ba
"Inason kaje ka ganta,duk da ina zaton zuwansu gidan nan kamar ka taba ganinta,amma wannan zuwa ne na musamman,kaje ka gabatar mata da kanka" kai yadan sunkui qasa
"In sha Allah hajiya zan saka rana sai na sanarwa muhsin din sai naje" har cikin ranta ta sake qaunar abbas din,tasan dama bashi da matsala kome kuwa tace yayi,saidai ta dauka zaiyi jayayya ko ya qalubalanci wannan danyan hukuncin nata.
Duk yadda yaso ya fidda damuwa ya zauna suyi hira sosai amma ya kasa,jiki da zuciyarsa dukka a takure suke,dole bayan qarfe tara ya yiwa hajiyan sallama ya wuce gidansa.
A kan hanya yana tuqi amma tunani ne fal kwanyarsa,aure?,wacece widad din ma?,oho shi bai ganeta ba,amma me hajiya ta hango masa?,sai Allah,bazai iya mata wannan tambayar titsiyen ba,da wannan damuwar da kuma tunanin ya isa gida.
Bashi da hadi da sassan hafsa,don haka sassansa ya wuce,yabude ya shiga yana tsaye tsakar falon kamar maison tuna abinda ya kamata yayi wayarsa ta dauki sassanyan busar sarewar dake a mazaunin ringtone dinsa,don bayason ringtone mai hayaniya da yawa,mafi yawan lokutta ma yafi barin wayar tasa a vibration.
Cikin wata kasala da gajiya da maganar hajiya ta saukar masa ya zaro wayar yana duba me kiran,hafsat dince,sai ya daga kiran yana neman kujera daya cikin falon ya zauna
"Ina ka shiga ne inata kira baka daga ba" ta fada muryarta a tsaye carrr,alamun qagauta da son samun mutum,shuru yayi yana nazartar muryarta
"Lafiya?" Ya fada da nutsatsiyar muryarsa mai nauyi,wadda ta dawo da hafsat din cikin nutsuwarta kadan,ta kuma fuskanci yanayin data masa magana baiyi dai dai ba,kishi ne keta cin ranta,har idanunta suka so rufewa,gani take kamar yana tare da wata ne shi yasa yaqi daga wayarta,
"Ah....uhmm lafiya qalau,kawai hankalina ya dan tashi da naga inata kira baka daga ba"
"Oh.....am fine,kufa?"
"Lafiya qalau muke,yara gaba daya sunyi kewarka"
"That's my babies.....kefa?" Ya fada yana danne damuwarsa,murmushi ta saki wanda ya jiyo sautinsa
"To nima nayi" ta fada tana danjin nauyi,idanunsa ya lumshe yana kuma budesu,she's not romantic woman at all,ya rasa yadda zai canzata,kamar irin matan da soyayya bata damesu ba sam,dai dai da greetings cards da yake siya mata time to time,musamman idan yayi tafiya ya dawo bata wani daukar abun da muhimmanci,wani lokaci ma idan ya kawo cards din bata ko budesu bare ta karanta,karba take ta ajjiye bayan ta bishi da SANNU.
"I miss you more than you can imagine" ya fada with softness,wanda har sai data ji tsigar jikinta ta tashi,wani abu ya tsarga mata,amma sai tace
"Allah ya qara zumunci"
"Zumunci dai?" Ya maimaita a ransa,even kalmomin da zatayi appreciating nasa bata dasu,har ya fara sabawa.
Shurun da ya gilma tayi amfani da wannan daqiqun
"Magana da zamuyi ko ince tambaya zanyi"
"Am sorry ranki ya dade,yanzun nan na shigo gida,bari na gama shiryawa saina kiraki,inaso yau ayimin hira sosai,na gaji da yawa"
"Kai da kaje hutu?,me kayi daya gaji da kai?" Ta fadi da salon tambaya,ita sam hankalinta bai kwanciya idan basa tare
"Yawo" ya amsa mata a taqaice,sai ranta ya sosu,anya ba abinda take zato bane
"Yawo kuma abban mimi?,don Allah ka daina banso wallahi"
"It's okay" ya fada fuskarsa na fidda miskilin murmushin da bai shiryawa ba,yasan meke damunta
"Ka kira da wuri,don bacci nakeji inason na kwanta"
"Okay" yace da ita yana katse wayar gami da ajjiye ta gefe
"Hafsat hafsat,ko sai yaushe zata canza?" Yayi maganar shi da zuciyarsa,sai ya miqe yana wucewa bedroom.
KI KULANI miss xoxo
DAUDAR GORA Billynabdul
RUMBUN K'AYA hafsat rano
IDON NERA Mamuhghee
A RUBUCE TAKE huguma
_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so,zasu fara fita a gobe da izinin mai duka_
_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_
0022419171
Maryam sani
Access bank
Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070
*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261
*Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number*
+227 90 16 59 91
*Zafafa biyar kadai keda sinqin nau'ikan kalar labarun da kukafiso jimilla a lokaci guda*🤝😄
*Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks: Huguma*
Page 20
Sai daya gama duk abinda yakeyi ya kwanta yaja bargonsa zuwa qugu bayan ya rage hasken dakin sannan ya kirata.
Har tayi ringing ta gama bata dauka ba,ya sake kira karo na biyu sannan ta miqe daga kwanciyar da tayi,ta jawo wayar tana sakin hamma,dan qaramin tsaki taja,banda maganar da takeso suyi nada muhimmanci da bazata daga ba,batason zancan motar yayi nisa kada taje ta zama rabon wasu,abinda kawai bataso yanzun zaice saita tsaya sunyi hirar soyayya,batasan me dame zata ce masa ba,daga qarshe kuma ya tada mata feelings ko ya isheta da fitina idan ya dawo.
Cikin qaramin sauti tayi masa sallamar wanda baccin data fara ji ya jawo hakan,saidai shi din abun ya tabashi,har ya tada masa tsigar jikinsa,ya rufe idanunsa yana amsa mata
"Am sorry,na tasheki halan?"
"Ummm,babu komai"
"Thanks" da hanzarinta ta katsi numfashinsa
"Abban mimi ina cikin maka gyara ne shekaran jiya naga key din sabuwar mota,to yau kuma mimi ta tabo wajen ta zubda kaya,da na maida kayan banga key din ba,nace Allah yasa ba wani wajen ta jefa maka ba"
"Noo,ni na tafi dashi,motar dama ta hajiya ce,so sai na baiwa samuel nace gobe ya biyoni da ita a kawo mata,kinsan motar da ake fita da ita ta samu matsala" idan tace ga irin bacin ran da taji ya saukar mata ma ta yiwa kanta qarya,abinda taketa hasashe kenan,take kuma gudu,yanzun motar ya dauka ya baiwa hajiyan bayan yasan tana da buqata,tana ta kuma gaya masa ya canza matan bai canza ba?,ta yaya zata nuna masa ma zallar bacin ranta?
"Abban mimi amma dai kasan ina da buqatar motar nan ko?,sati nawa ina maka naci ka hanani?,amma a gabana ka siya......"
"Hafsatu" ya kirata da sunan da mafi yawa jama'a ke kiranta ba tare da ya bari ta idar da maganarta ba,kiran kuwa ya ratsa mata ko ina,yana da wata murya dake da kwarjini
"Baki gane wacce na siyawa motat bane?,hajiyata mahaifiya ta nake magana" boyayyar ajiyar zuciya ta sauke,tana kuma qoqarin sassauta harshenta
"Bance bakayi dai dai ba ai,amma nafi buqatar motar,da sai ka karba ta wajena ayi mata gyara ka bata,tunda hajiya bako yaushe ta fiya fita ba,sai ta dade a gida bata fita ba,zata iya manage da ita"
"Hajiyan tawa za'a bawa ragowar motarki tayi manage?" Cikin zallar mamaki ya jefa mata tambayar, jikinta daga can yayi sanyi,saidai bacin ran da takeji a zuciyarta ya hanata gayawa kanta tana fadin abinda bai kamata bane
"To menene a ciki?"
"A wajena wani abunne,idan bakisan darajarta ba ni nasan darajarta,tafi qarfin cin ragowar kowa a duniya bare taki ragowar,karki kuskura ki kaini bango da banzayen maganganunki,idan ba haka ba zaki gane kuskurenki,ki adana maganganunki basu da wani amfani a wajena,kudi dai nawa ne,zan kuma wahaltawa mahaifiya ta a duk sanda naso ba tare da shawara ko yardarki ba"
"Amma dai kasan nima ina da hakki ai a kanka ko?,tunda nima matark......"
"You are very stupid" ya fada da zafi yana datse kiran,bayason yaci gaba da saurarenta kada ta tunzarashi,idan ya tunzura baisan me zai biyo baya ba,yana kallonta tanata kiransa amma yaqi dagawa,sai ma ya maida wayar silent ya maida kansa ya kwanta yana ta furzar da iska a bakinsa ko zai samu zuciyarsa ta rage zafin da take masa.
Bayan kiran ya tsagaita da shigowa sai kuma wani haske yayi blinking,alamun shigowar tex,wayar ya jawo da niyyar kasheta gaba daya,saidai saqon ya fito saman screen din
_Tunda ni bankai wani bigire na abu mai muhimmanci a tare da kai ba,nima bazan zauna ina aikin da ba'a gani ba,zan dawo garinmu inda akasan darajata_
"Har yanxu kana lokaci mutumina,bansan me yake fusgar hankalinsu ba haka,adan bani sirrin mana" ya fuskanci sarai abinda suraj yake fada,fuskarsa kadaram kadaham ya waiwayo kadan ya dubeshi sannan ya maida kansa ga titi
"Kai har yanzu baka girma na suraj,ana ta neman na abincin da za'a kaiwa iyali kuma wa yake ta wannan" ya fada yana shafar habarsa dake zagaye da gemun daya samu wadataccen tsafta da gyara
"Banga alama ba,don duk sanda muka fito irin haka sai wata ta taya"
"To ai sai suyita yi,ta gidanma ya ka cika da ita bare ka sake daukan wata,kayita hadama kanka rigima da zafi,bazan iya daukan wannan ba"
"Fada dai kake,bari ayi katari da wadda zata sace maka zuciya"
"Haka kake gani" abbas ya maida masa amsa,hankali da idanunsa naga titi.
Dariya kawai Suraj yayi,bai sake cewa komai ba suka shiga wata hirar.
Sai daya fara sauke suraj a gida bayan ya hadashi da tashi ledar sannan ya koma gidan hajiyan.
Bayan isha'i ya zauna sukaci abinci,kusan tare da hajiyan,saidai kowa kwanonsa daban,bayan sun kammala ya dauke kwanukan da kansa ya tattare wajen sannan ya dawo ya zauna yana fuskantar hajiyan
"Hajiya kince zamuyi magana ko?" Gyara zamanta tayi sosai
"Eh tabbas"
"To ina jinki,Allah yasa ba wani laifi nayi ba" murmushi ta sake
"Laifi abbas?,a'ah ko kadan,wani alkhairi na hango maka,na kumayi karambanin zartar maka dashi ba tare dana tuntube ka ba" qaramin murmushi ya saki
"Hajiya...ai kinfi qarfin ki yiwa rayuwata karambani,kome kika ga dama ki zartar dashi kanki tsaye kawai" kai ta dan jinjina sannan tace
"Aure na nema maka,'yar uwa ko 'yar muhsin" sosai gabansa ya fadi,abinda ya jima baiji irinsa ba tsahon rayuwarsa
"Hajiya nujood?" Ya fada cikin fargaba,don ko da ya kasance itace bazai iya musawa hajiyan ba,haka zai auretan,yarinyar dake kallonsa a mazaunin ubanta
"A'ah,widad" ajiyar zuciya ya sauke,sai yaji tashin hankalin da yake ciki din ya ragu,ya samu 'yar nutsuwa,duk da fahimci wa take nufi din ba,amma dai ya fahimci wata ce daban ba nujood ba
"Inason kaje ka ganta,duk da ina zaton zuwansu gidan nan kamar ka taba ganinta,amma wannan zuwa ne na musamman,kaje ka gabatar mata da kanka" kai yadan sunkui qasa
"In sha Allah hajiya zan saka rana sai na sanarwa muhsin din sai naje" har cikin ranta ta sake qaunar abbas din,tasan dama bashi da matsala kome kuwa tace yayi,saidai ta dauka zaiyi jayayya ko ya qalubalanci wannan danyan hukuncin nata.
Duk yadda yaso ya fidda damuwa ya zauna suyi hira sosai amma ya kasa,jiki da zuciyarsa dukka a takure suke,dole bayan qarfe tara ya yiwa hajiyan sallama ya wuce gidansa.
A kan hanya yana tuqi amma tunani ne fal kwanyarsa,aure?,wacece widad din ma?,oho shi bai ganeta ba,amma me hajiya ta hango masa?,sai Allah,bazai iya mata wannan tambayar titsiyen ba,da wannan damuwar da kuma tunanin ya isa gida.
Bashi da hadi da sassan hafsa,don haka sassansa ya wuce,yabude ya shiga yana tsaye tsakar falon kamar maison tuna abinda ya kamata yayi wayarsa ta dauki sassanyan busar sarewar dake a mazaunin ringtone dinsa,don bayason ringtone mai hayaniya da yawa,mafi yawan lokutta ma yafi barin wayar tasa a vibration.
Cikin wata kasala da gajiya da maganar hajiya ta saukar masa ya zaro wayar yana duba me kiran,hafsat dince,sai ya daga kiran yana neman kujera daya cikin falon ya zauna
"Ina ka shiga ne inata kira baka daga ba" ta fada muryarta a tsaye carrr,alamun qagauta da son samun mutum,shuru yayi yana nazartar muryarta
"Lafiya?" Ya fada da nutsatsiyar muryarsa mai nauyi,wadda ta dawo da hafsat din cikin nutsuwarta kadan,ta kuma fuskanci yanayin data masa magana baiyi dai dai ba,kishi ne keta cin ranta,har idanunta suka so rufewa,gani take kamar yana tare da wata ne shi yasa yaqi daga wayarta,
"Ah....uhmm lafiya qalau,kawai hankalina ya dan tashi da naga inata kira baka daga ba"
"Oh.....am fine,kufa?"
"Lafiya qalau muke,yara gaba daya sunyi kewarka"
"That's my babies.....kefa?" Ya fada yana danne damuwarsa,murmushi ta saki wanda ya jiyo sautinsa
"To nima nayi" ta fada tana danjin nauyi,idanunsa ya lumshe yana kuma budesu,she's not romantic woman at all,ya rasa yadda zai canzata,kamar irin matan da soyayya bata damesu ba sam,dai dai da greetings cards da yake siya mata time to time,musamman idan yayi tafiya ya dawo bata wani daukar abun da muhimmanci,wani lokaci ma idan ya kawo cards din bata ko budesu bare ta karanta,karba take ta ajjiye bayan ta bishi da SANNU.
"I miss you more than you can imagine" ya fada with softness,wanda har sai data ji tsigar jikinta ta tashi,wani abu ya tsarga mata,amma sai tace
"Allah ya qara zumunci"
"Zumunci dai?" Ya maimaita a ransa,even kalmomin da zatayi appreciating nasa bata dasu,har ya fara sabawa.
Shurun da ya gilma tayi amfani da wannan daqiqun
"Magana da zamuyi ko ince tambaya zanyi"
"Am sorry ranki ya dade,yanzun nan na shigo gida,bari na gama shiryawa saina kiraki,inaso yau ayimin hira sosai,na gaji da yawa"
"Kai da kaje hutu?,me kayi daya gaji da kai?" Ta fadi da salon tambaya,ita sam hankalinta bai kwanciya idan basa tare
"Yawo" ya amsa mata a taqaice,sai ranta ya sosu,anya ba abinda take zato bane
"Yawo kuma abban mimi?,don Allah ka daina banso wallahi"
"It's okay" ya fada fuskarsa na fidda miskilin murmushin da bai shiryawa ba,yasan meke damunta
"Ka kira da wuri,don bacci nakeji inason na kwanta"
"Okay" yace da ita yana katse wayar gami da ajjiye ta gefe
"Hafsat hafsat,ko sai yaushe zata canza?" Yayi maganar shi da zuciyarsa,sai ya miqe yana wucewa bedroom.
KI KULANI miss xoxo
DAUDAR GORA Billynabdul
RUMBUN K'AYA hafsat rano
IDON NERA Mamuhghee
A RUBUCE TAKE huguma
_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so,zasu fara fita a gobe da izinin mai duka_
_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_
0022419171
Maryam sani
Access bank
Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070
*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261
*Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number*
+227 90 16 59 91
*Zafafa biyar kadai keda sinqin nau'ikan kalar labarun da kukafiso jimilla a lokaci guda*🤝😄
*Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks: Huguma*
Page 20
Sai daya gama duk abinda yakeyi ya kwanta yaja bargonsa zuwa qugu bayan ya rage hasken dakin sannan ya kirata.
Har tayi ringing ta gama bata dauka ba,ya sake kira karo na biyu sannan ta miqe daga kwanciyar da tayi,ta jawo wayar tana sakin hamma,dan qaramin tsaki taja,banda maganar da takeso suyi nada muhimmanci da bazata daga ba,batason zancan motar yayi nisa kada taje ta zama rabon wasu,abinda kawai bataso yanzun zaice saita tsaya sunyi hirar soyayya,batasan me dame zata ce masa ba,daga qarshe kuma ya tada mata feelings ko ya isheta da fitina idan ya dawo.
Cikin qaramin sauti tayi masa sallamar wanda baccin data fara ji ya jawo hakan,saidai shi din abun ya tabashi,har ya tada masa tsigar jikinsa,ya rufe idanunsa yana amsa mata
"Am sorry,na tasheki halan?"
"Ummm,babu komai"
"Thanks" da hanzarinta ta katsi numfashinsa
"Abban mimi ina cikin maka gyara ne shekaran jiya naga key din sabuwar mota,to yau kuma mimi ta tabo wajen ta zubda kaya,da na maida kayan banga key din ba,nace Allah yasa ba wani wajen ta jefa maka ba"
"Noo,ni na tafi dashi,motar dama ta hajiya ce,so sai na baiwa samuel nace gobe ya biyoni da ita a kawo mata,kinsan motar da ake fita da ita ta samu matsala" idan tace ga irin bacin ran da taji ya saukar mata ma ta yiwa kanta qarya,abinda taketa hasashe kenan,take kuma gudu,yanzun motar ya dauka ya baiwa hajiyan bayan yasan tana da buqata,tana ta kuma gaya masa ya canza matan bai canza ba?,ta yaya zata nuna masa ma zallar bacin ranta?
"Abban mimi amma dai kasan ina da buqatar motar nan ko?,sati nawa ina maka naci ka hanani?,amma a gabana ka siya......"
"Hafsatu" ya kirata da sunan da mafi yawa jama'a ke kiranta ba tare da ya bari ta idar da maganarta ba,kiran kuwa ya ratsa mata ko ina,yana da wata murya dake da kwarjini
"Baki gane wacce na siyawa motat bane?,hajiyata mahaifiya ta nake magana" boyayyar ajiyar zuciya ta sauke,tana kuma qoqarin sassauta harshenta
"Bance bakayi dai dai ba ai,amma nafi buqatar motar,da sai ka karba ta wajena ayi mata gyara ka bata,tunda hajiya bako yaushe ta fiya fita ba,sai ta dade a gida bata fita ba,zata iya manage da ita"
"Hajiyan tawa za'a bawa ragowar motarki tayi manage?" Cikin zallar mamaki ya jefa mata tambayar, jikinta daga can yayi sanyi,saidai bacin ran da takeji a zuciyarta ya hanata gayawa kanta tana fadin abinda bai kamata bane
"To menene a ciki?"
"A wajena wani abunne,idan bakisan darajarta ba ni nasan darajarta,tafi qarfin cin ragowar kowa a duniya bare taki ragowar,karki kuskura ki kaini bango da banzayen maganganunki,idan ba haka ba zaki gane kuskurenki,ki adana maganganunki basu da wani amfani a wajena,kudi dai nawa ne,zan kuma wahaltawa mahaifiya ta a duk sanda naso ba tare da shawara ko yardarki ba"
"Amma dai kasan nima ina da hakki ai a kanka ko?,tunda nima matark......"
"You are very stupid" ya fada da zafi yana datse kiran,bayason yaci gaba da saurarenta kada ta tunzarashi,idan ya tunzura baisan me zai biyo baya ba,yana kallonta tanata kiransa amma yaqi dagawa,sai ma ya maida wayar silent ya maida kansa ya kwanta yana ta furzar da iska a bakinsa ko zai samu zuciyarsa ta rage zafin da take masa.
Bayan kiran ya tsagaita da shigowa sai kuma wani haske yayi blinking,alamun shigowar tex,wayar ya jawo da niyyar kasheta gaba daya,saidai saqon ya fito saman screen din
_Tunda ni bankai wani bigire na abu mai muhimmanci a tare da kai ba,nima bazan zauna ina aikin da ba'a gani ba,zan dawo garinmu inda akasan darajata_