Sashe 47
A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
K'aramin murmushi ya subuce masa,banda yaaya bara'atun babu wanda zasuyi irin wannan maganar dashi
"Jibi nake saka ran wucewa,hutun da suka bani ya qare"
"Sun kyauta ma ai, duka duka yaushe ka koma kadunan ma,Allah ya sanya albarka sun kyautata maka kam"
"Sosai hajiya" ya furta yana gyada kansa.
"Tafiya dai ta kama hafsat zuwa yanzu,tunda dai ai ba zasu tattare gaba dayansu su zauna anan kai kana can ba" anty bara'atu ta sake fadi tana dubansa,duk da bata da tabbacin samun cikakkiyar amsa daga gareshi,ta sani ba kasafai ya fiya son hirarraki irin wadan nan ba.
Kaman hajiyan ta fuskanci bashi da niyyar yin magana din,sai tayi amfani da wannan damar ta isar da saqon da take ta son isar masa din
"Hafsat ai dama bauchi ta zaba,widad itace abokiyar tafiya Kaduna,ita ta riga ta yankewa kanta hukunci,bana jin kuma zata janye" tsaf ya gama karantar saqon hajiyan,saidai can qasan ranshi yana tunanin yadda zai dauki rigimammiyar yarinyar da bata da maraba dasu mimi har zuwa wata uwa duniyar da sunan matarsa
"Amma hajiya sai nakega ba zataji dadi ba,daga zuwan wata sai a tafi da ita ita kuma tana zaune?"
"A'haaannn,to daa waye yayi mata?,ita ta yankewa kanta wannan hukuncin,ta kuma bada zabin ya samo mai zama dashi,meye laifi yanzun dukka a cikin wannan lamarin?" Shuru bara'atun tayi,sai ta dan jinjina kanta
"Allah ya sawwaqe" .
Shigowar fanteka ya tasheshi,ya miqe yana zuba hannayensa a aljihun wandonsa
"Bari na danje bayanmu na dawo"
"Allah ya kiyaye,sai ka dawo" hajiya ta fada kanta tsaye,tashin da yayi yayi mata,don batason wata magana sam a gaban fantekan,tunda ta karanci inda ta sanya gaba.
Ba haka fanteka taso ba,amma saita rakashi da yaqe tare da addu'ar a dawo lafiya.
*Arewabooks:Huguma*
KI KULANI miss xoxo
DAUDAR GORA Billynabdul
RUMBUN K'AYA hafsat rano
IDON NERA Mamuhghee
A RUBUCE TAKE huguma
_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_
_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_
0022419171
Maryam sani
Access bank
Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070
*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261
*Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number*
+227 96 09 67 63
*Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Page 42
Sanda ya dawo gidan babu kowa sai hajiyan tashi,nan yayi zamansa bayan ya fito daga sallar isha'i,yana cin abinci tana qara masa suna hirarsu
"Nidai don Allah zan riqo alfarma guda daya a wajenka abbas" tayi zancan tana ajjiye dan bowl din data qara masa miya,sai ya tattara mata hankalinsa gaba daya,har yana ajjiye spoon din hannunsa
"Hajiya badai alfarma ba,saidai umarni ko?"
"Ko alfarma koma umarni,nidai burina ka cika......don Allah ka kula da yarinyar nan kamar yadda zaka kulaa da hadiyya da kuke fito ciki daya" kai ya jinjina,can qasan ransa yana jinjina tarin qaunar da hajiyar kema yarinyar
"Na daukar miki alqawari hajiya"
"To Allah ya taimakeka,yaci gaba da dafawa al'amuranka"
"Ameen ya raheem,Allah ya qara lafiya da nisan kwana" sai ta bishi da murmushi kawai,kafin ta amsa masa da ameen.
Yau din sassan Widad din ya fara isa,saidai latifa na bude masa qofa taja baya cikin girmamawa,har ya sanya kansa sai ya dakata
"Kuna lafiya?,baku buqatar komai?" Ya tambaya,kai ta girgiza,tana tsananin yabawa da irin kulawar da yake nunawa akan widad din
"Lafiya qalau alhmdlh,babu komai"
"Itafa?" Ya tambaya kai tsaye
"Tayi bacci tun dazu"
"Lafiya dai ko?" Ya tambayeta yana dan ritsata da ido,kusan bai taba zuwa ya sameta tana bacci ba,yafi samunta a daki,data ganshi zata fara tattare jiki waje daya,ta kuma sanyawa bakinta kwado da linzami,har sai ya gana zamansa na mintu biyu zuwa uku sannan ya fito
"Eh bata dan jin dadin jikinta ne wai"
"Subhanallah,amma me yasa ba'a kirani an kaita asibiti ba?"
"Ba zazzabi ko ciwon kai bane,kawai bata da kuzadi ne kamar yadda ta saba" sai yadan kada kai kadan
"Allah ya sawwaqe,ammmm..... Please,koda akwai wani damuwa,a kirani ko ta wayarta ne"
"In sha Allah" ta fada cikin girmamawa,cikin ranta tana yaba kulawa da sanin darajar dan adam irin nasa.
Sanda ya shiga falon hafsa a zaune ya sameta,yaran na kwance a wajen saman carfet kowa d'ai d'ai,itama saman carfet din take a zaune,hannunta riqe da waya,plates din abinci ne da abincin da sukaci suka zuzzubar kaca kaca,saman kanta ba dankwali,gashinta dake samun qarancin kulawa qwarai da gaske daure a kyauro.
Idonsa ya dauke daga kanta yana qarasawa wajen yaransa,saita janye qafafunta tana masa sannu da zuwa,qasa qasa ya amsa mata,yana dauke yaran daga qasa ya nufi dakinsu dasu.
A hargitse ya samu dakin kamar ko yaushe,sai a gadon nawwara ya fara ajesu,ya karkade gadon mimi ya maidasu kai,sannan ya gyarawa nawwara nata gadon itama ya maidata kai,bayan ya duba cupboard dinsu ya canza musu wankakken zanin gado,ya tattara karikicen kayan wasansu dake tsakiyar dakin ya killace a drawer dinsu ya hade kayan wankinsu a laundry basket.
Yana gab da kammala mopping na dakin ta turo qofar ta shigo,zuwa yanzu daurin dankwalin ture kaga tsiya ne a kanta,dinkin atamfa ce doguwar riga data bude sosai daga qasa,saidai idan ka kalli kayan sosai a jikinta zakasan ta dan sha jiki.
"Ya daga shigowarka kuma dear?" Ta fada tana jin wani iri a ranta,shi ya fiya qaqale qaqale,banda hakan bataga wani shahararren datti da dakin yayi wanda zai hana mutum yin bacci ba,taga ko daxun kafin ta fita sai data tattare kayan wankin gefe daya,amma shi baima gani ba.
Idanu ya aza mata kafin ya janye yaci gaba da qarasa goge wajen,sai jikinta ya dan mata sanyi daga kalar kallon da yayi mata,don haka ta saki qofar tana qarasowa ciki.
Kafin ta qaraso ya gama,ya ajjiye mopping stick din,sannan ya goye hannayensa da tuni ya nade hannaun rigar xuwa sama yana kallonta,yadda ya aza mata kallon mayatattun idanuwan nan nasa duka sai taji nauyinsa ya sake kamata,don haka ta daburce gaba daya
"Samu guri ki zauna" ya bata umarni kai tsaye,sai tadan ja tunga,gabanta yana faduwa,bata qaunar fadansa gaba daya,yanzun nan zai sanya ka ka rasa abun fadi,bayan tasan bata da kalar kowacce hujja da zata kare kanta da ita,dole ta samu gefan gadon nawwara ta zauna.
Daya daga cikin kujerun dake hade da teburin karatunsu ya jawo,ya ajjiyeta dab ds ita ya zauna akai.
Shuru ya ratsa dakin,tana ta kasa kunne taji me zayace da ita,yayin da shi kuma bai furta komai ba,sai kallo da ya ritsata dashi,kallon dake sake sanyata jin cewa da gaske ita din mai laifi ce
"Hafsat" ya kira sunanta kai tsaye,wanda abune mawuyaci kaji ya kirata din
"Na'am" ta amsa masa ba tare data iya kallon qwayar idanunsa ba
"Ki gayamin me kika nema kika rasa a gidan nan,wanne nauyi ne nawa da bana sauke miki?" Motsawa tayi,kamar wadda ke zaune saman wuta,kasa bashi amsa tayi,har ya gaji da jiranta,sai ya sauke hannayensa qasa ya dafe kujerar da yake kai yana ci gaba da kallonta
"A iya sanina babu wani abu da yayi saura wanda bana miki shi,ci sha suttura,kudin kashewa,hatta da lighter da za'a kunna gas a gidan nan alhmdlh ban bari ko yarda ki siya ba,me kika rasa hafsat?,amma kin kasa tsaida hankalinki ki tsaftace gidanki,ki kula da yaranki,ki sauke hakkina dake kanki,zaki iya tuna when last da kika kawo kanki gareni?" Ys jefa tambaya mafi girma da taketa tsoron yayi mata ita
"Don Allah kada ka kawo wannan zancan,ka san dai ina iya bakin qoqarina ai......" Wani miskilin murmushin takaici ya saki
"Well......am listen to you" da qyar ta tattaro dukka jarumta da qwarin gwiwar ta,duk da cikin ranta har yanzu bata jin kanta a matsayin mai laifi
"Ina fa kwatantawa,ina qoqarina dear,aikin gida fa ba is not easy at all,sauqinta ma ace ina da 'yar aiki,amma yanzun komai fa ni nakeyin abina,ga yara,ga makarantar mimi,dole wania abun fa sai ana haquri" ta fada tana dan tsuke girarta fuskarta qasa qasa,ita ala dole bataji dadin gyaran da yakeson mata ba.
Shuru yayi kawai yana kallon fuskarta, reaction din da ta nuna saman fuskarta ya isa ya gamsar dashi cewa bata dauki kanta a tana aikata wani abu na ba dai dai ba,an dade hakan tana faruwa a tsakaninsu
"Idan aiki ya hanaki gyara muhallin mijinki dana yaranki.....shi kuma kitchen da kika tara kwanukan wanke wanke fa?, harda na tuwon jiya?"
"Yau ai fita nayi,kuma ka sani dear,ban zauna gaba daya a gidan ba,amma gobe in sha Allah da aikinsu zan tashi,idan na gyara gobe zaka ga kamar ba'ayi ba,ba shikenan ba?" A hankali ya lumshe idanuwansa gaba daya yana kiran sunan Allah,mata nawa ne keda nauyin da yafi nata amma zaka samesu su da gidansu da iyalinsu tsaf?,wannan muguwar qazantar baisan ta yaya zai raba hafsat din da ita ba,tafi komai ci masa tuwo a qwarya,ya yiwa qazanta wani mugu tsana da har baisan iyakarsa ba,abinda hafsat din har kwanan gobe ta kasa ganowa,mai aiki dai mai aiki dai.....shikam ba sakaran namiji bane da zai daukoma hafsat mai aiki,ya tabbatar daga qarshe ita zata koma yin komai.na gidan,qarshe harda abincinsa da zaya ci.
Miqewa kawai yayi,ya zura hannayensa a aljihunsa
"Duk abinda ya kamata nayi miki na miki shi,ya kamata ki canza for now.....yaranki suna girma,zasu kuma dauki jalar kowacce dabi'a daga wajenki,dama sau daya tak take zuwa ma mutum a rayuwa" yayi maganar yana daga yatsansa guda daya,sanann ya juya yana barin dakin.
Gabanta ya fadi,binsa tayi da kallo har ya fice,to me yake nufi?,abbas din yana da wuyar fahimta wani lokacin,ta janye idanunta daga kallon qofar da tuni ya jima da wucewa,ta dawo da dubanta cikin dakin,komai yayi fea gwanin sha'awa,ta tabbatar koda ita tayi wannan gyaran bazaiyi kyau haka ba,to itadai bataga laifi ba,idan ma yayin ba duka yaransu bane shi da ita?.
Taso sharewa itama,amma sai zuciyarta ta gaza nutsuwa da hakan,wannan dalilin yasa ta bashi kusan awa guda,sannan ta tattara kayan abincin tana ta mita a ranta na wahalar da ya bata na diban abincin tayi sashensa.
Da sallama ta tura qofar bedroom din nasa,sassanyan qamshinsa ya fara mata maraba,babu wadataccen haske a dakin sosai,yana daga gefe saman dan table din da yake dora system dinsa yayi wasu ayyuka da suka shafeshi yana duba wasu takardu.
"Jibi nake saka ran wucewa,hutun da suka bani ya qare"
"Sun kyauta ma ai, duka duka yaushe ka koma kadunan ma,Allah ya sanya albarka sun kyautata maka kam"
"Sosai hajiya" ya furta yana gyada kansa.
"Tafiya dai ta kama hafsat zuwa yanzu,tunda dai ai ba zasu tattare gaba dayansu su zauna anan kai kana can ba" anty bara'atu ta sake fadi tana dubansa,duk da bata da tabbacin samun cikakkiyar amsa daga gareshi,ta sani ba kasafai ya fiya son hirarraki irin wadan nan ba.
Kaman hajiyan ta fuskanci bashi da niyyar yin magana din,sai tayi amfani da wannan damar ta isar da saqon da take ta son isar masa din
"Hafsat ai dama bauchi ta zaba,widad itace abokiyar tafiya Kaduna,ita ta riga ta yankewa kanta hukunci,bana jin kuma zata janye" tsaf ya gama karantar saqon hajiyan,saidai can qasan ranshi yana tunanin yadda zai dauki rigimammiyar yarinyar da bata da maraba dasu mimi har zuwa wata uwa duniyar da sunan matarsa
"Amma hajiya sai nakega ba zataji dadi ba,daga zuwan wata sai a tafi da ita ita kuma tana zaune?"
"A'haaannn,to daa waye yayi mata?,ita ta yankewa kanta wannan hukuncin,ta kuma bada zabin ya samo mai zama dashi,meye laifi yanzun dukka a cikin wannan lamarin?" Shuru bara'atun tayi,sai ta dan jinjina kanta
"Allah ya sawwaqe" .
Shigowar fanteka ya tasheshi,ya miqe yana zuba hannayensa a aljihun wandonsa
"Bari na danje bayanmu na dawo"
"Allah ya kiyaye,sai ka dawo" hajiya ta fada kanta tsaye,tashin da yayi yayi mata,don batason wata magana sam a gaban fantekan,tunda ta karanci inda ta sanya gaba.
Ba haka fanteka taso ba,amma saita rakashi da yaqe tare da addu'ar a dawo lafiya.
*Arewabooks:Huguma*
KI KULANI miss xoxo
DAUDAR GORA Billynabdul
RUMBUN K'AYA hafsat rano
IDON NERA Mamuhghee
A RUBUCE TAKE huguma
_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_
_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_
0022419171
Maryam sani
Access bank
Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070
*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261
*Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number*
+227 96 09 67 63
*Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Page 42
Sanda ya dawo gidan babu kowa sai hajiyan tashi,nan yayi zamansa bayan ya fito daga sallar isha'i,yana cin abinci tana qara masa suna hirarsu
"Nidai don Allah zan riqo alfarma guda daya a wajenka abbas" tayi zancan tana ajjiye dan bowl din data qara masa miya,sai ya tattara mata hankalinsa gaba daya,har yana ajjiye spoon din hannunsa
"Hajiya badai alfarma ba,saidai umarni ko?"
"Ko alfarma koma umarni,nidai burina ka cika......don Allah ka kula da yarinyar nan kamar yadda zaka kulaa da hadiyya da kuke fito ciki daya" kai ya jinjina,can qasan ransa yana jinjina tarin qaunar da hajiyar kema yarinyar
"Na daukar miki alqawari hajiya"
"To Allah ya taimakeka,yaci gaba da dafawa al'amuranka"
"Ameen ya raheem,Allah ya qara lafiya da nisan kwana" sai ta bishi da murmushi kawai,kafin ta amsa masa da ameen.
Yau din sassan Widad din ya fara isa,saidai latifa na bude masa qofa taja baya cikin girmamawa,har ya sanya kansa sai ya dakata
"Kuna lafiya?,baku buqatar komai?" Ya tambaya,kai ta girgiza,tana tsananin yabawa da irin kulawar da yake nunawa akan widad din
"Lafiya qalau alhmdlh,babu komai"
"Itafa?" Ya tambaya kai tsaye
"Tayi bacci tun dazu"
"Lafiya dai ko?" Ya tambayeta yana dan ritsata da ido,kusan bai taba zuwa ya sameta tana bacci ba,yafi samunta a daki,data ganshi zata fara tattare jiki waje daya,ta kuma sanyawa bakinta kwado da linzami,har sai ya gana zamansa na mintu biyu zuwa uku sannan ya fito
"Eh bata dan jin dadin jikinta ne wai"
"Subhanallah,amma me yasa ba'a kirani an kaita asibiti ba?"
"Ba zazzabi ko ciwon kai bane,kawai bata da kuzadi ne kamar yadda ta saba" sai yadan kada kai kadan
"Allah ya sawwaqe,ammmm..... Please,koda akwai wani damuwa,a kirani ko ta wayarta ne"
"In sha Allah" ta fada cikin girmamawa,cikin ranta tana yaba kulawa da sanin darajar dan adam irin nasa.
Sanda ya shiga falon hafsa a zaune ya sameta,yaran na kwance a wajen saman carfet kowa d'ai d'ai,itama saman carfet din take a zaune,hannunta riqe da waya,plates din abinci ne da abincin da sukaci suka zuzzubar kaca kaca,saman kanta ba dankwali,gashinta dake samun qarancin kulawa qwarai da gaske daure a kyauro.
Idonsa ya dauke daga kanta yana qarasawa wajen yaransa,saita janye qafafunta tana masa sannu da zuwa,qasa qasa ya amsa mata,yana dauke yaran daga qasa ya nufi dakinsu dasu.
A hargitse ya samu dakin kamar ko yaushe,sai a gadon nawwara ya fara ajesu,ya karkade gadon mimi ya maidasu kai,sannan ya gyarawa nawwara nata gadon itama ya maidata kai,bayan ya duba cupboard dinsu ya canza musu wankakken zanin gado,ya tattara karikicen kayan wasansu dake tsakiyar dakin ya killace a drawer dinsu ya hade kayan wankinsu a laundry basket.
Yana gab da kammala mopping na dakin ta turo qofar ta shigo,zuwa yanzu daurin dankwalin ture kaga tsiya ne a kanta,dinkin atamfa ce doguwar riga data bude sosai daga qasa,saidai idan ka kalli kayan sosai a jikinta zakasan ta dan sha jiki.
"Ya daga shigowarka kuma dear?" Ta fada tana jin wani iri a ranta,shi ya fiya qaqale qaqale,banda hakan bataga wani shahararren datti da dakin yayi wanda zai hana mutum yin bacci ba,taga ko daxun kafin ta fita sai data tattare kayan wankin gefe daya,amma shi baima gani ba.
Idanu ya aza mata kafin ya janye yaci gaba da qarasa goge wajen,sai jikinta ya dan mata sanyi daga kalar kallon da yayi mata,don haka ta saki qofar tana qarasowa ciki.
Kafin ta qaraso ya gama,ya ajjiye mopping stick din,sannan ya goye hannayensa da tuni ya nade hannaun rigar xuwa sama yana kallonta,yadda ya aza mata kallon mayatattun idanuwan nan nasa duka sai taji nauyinsa ya sake kamata,don haka ta daburce gaba daya
"Samu guri ki zauna" ya bata umarni kai tsaye,sai tadan ja tunga,gabanta yana faduwa,bata qaunar fadansa gaba daya,yanzun nan zai sanya ka ka rasa abun fadi,bayan tasan bata da kalar kowacce hujja da zata kare kanta da ita,dole ta samu gefan gadon nawwara ta zauna.
Daya daga cikin kujerun dake hade da teburin karatunsu ya jawo,ya ajjiyeta dab ds ita ya zauna akai.
Shuru ya ratsa dakin,tana ta kasa kunne taji me zayace da ita,yayin da shi kuma bai furta komai ba,sai kallo da ya ritsata dashi,kallon dake sake sanyata jin cewa da gaske ita din mai laifi ce
"Hafsat" ya kira sunanta kai tsaye,wanda abune mawuyaci kaji ya kirata din
"Na'am" ta amsa masa ba tare data iya kallon qwayar idanunsa ba
"Ki gayamin me kika nema kika rasa a gidan nan,wanne nauyi ne nawa da bana sauke miki?" Motsawa tayi,kamar wadda ke zaune saman wuta,kasa bashi amsa tayi,har ya gaji da jiranta,sai ya sauke hannayensa qasa ya dafe kujerar da yake kai yana ci gaba da kallonta
"A iya sanina babu wani abu da yayi saura wanda bana miki shi,ci sha suttura,kudin kashewa,hatta da lighter da za'a kunna gas a gidan nan alhmdlh ban bari ko yarda ki siya ba,me kika rasa hafsat?,amma kin kasa tsaida hankalinki ki tsaftace gidanki,ki kula da yaranki,ki sauke hakkina dake kanki,zaki iya tuna when last da kika kawo kanki gareni?" Ys jefa tambaya mafi girma da taketa tsoron yayi mata ita
"Don Allah kada ka kawo wannan zancan,ka san dai ina iya bakin qoqarina ai......" Wani miskilin murmushin takaici ya saki
"Well......am listen to you" da qyar ta tattaro dukka jarumta da qwarin gwiwar ta,duk da cikin ranta har yanzu bata jin kanta a matsayin mai laifi
"Ina fa kwatantawa,ina qoqarina dear,aikin gida fa ba is not easy at all,sauqinta ma ace ina da 'yar aiki,amma yanzun komai fa ni nakeyin abina,ga yara,ga makarantar mimi,dole wania abun fa sai ana haquri" ta fada tana dan tsuke girarta fuskarta qasa qasa,ita ala dole bataji dadin gyaran da yakeson mata ba.
Shuru yayi kawai yana kallon fuskarta, reaction din da ta nuna saman fuskarta ya isa ya gamsar dashi cewa bata dauki kanta a tana aikata wani abu na ba dai dai ba,an dade hakan tana faruwa a tsakaninsu
"Idan aiki ya hanaki gyara muhallin mijinki dana yaranki.....shi kuma kitchen da kika tara kwanukan wanke wanke fa?, harda na tuwon jiya?"
"Yau ai fita nayi,kuma ka sani dear,ban zauna gaba daya a gidan ba,amma gobe in sha Allah da aikinsu zan tashi,idan na gyara gobe zaka ga kamar ba'ayi ba,ba shikenan ba?" A hankali ya lumshe idanuwansa gaba daya yana kiran sunan Allah,mata nawa ne keda nauyin da yafi nata amma zaka samesu su da gidansu da iyalinsu tsaf?,wannan muguwar qazantar baisan ta yaya zai raba hafsat din da ita ba,tafi komai ci masa tuwo a qwarya,ya yiwa qazanta wani mugu tsana da har baisan iyakarsa ba,abinda hafsat din har kwanan gobe ta kasa ganowa,mai aiki dai mai aiki dai.....shikam ba sakaran namiji bane da zai daukoma hafsat mai aiki,ya tabbatar daga qarshe ita zata koma yin komai.na gidan,qarshe harda abincinsa da zaya ci.
Miqewa kawai yayi,ya zura hannayensa a aljihunsa
"Duk abinda ya kamata nayi miki na miki shi,ya kamata ki canza for now.....yaranki suna girma,zasu kuma dauki jalar kowacce dabi'a daga wajenki,dama sau daya tak take zuwa ma mutum a rayuwa" yayi maganar yana daga yatsansa guda daya,sanann ya juya yana barin dakin.
Gabanta ya fadi,binsa tayi da kallo har ya fice,to me yake nufi?,abbas din yana da wuyar fahimta wani lokacin,ta janye idanunta daga kallon qofar da tuni ya jima da wucewa,ta dawo da dubanta cikin dakin,komai yayi fea gwanin sha'awa,ta tabbatar koda ita tayi wannan gyaran bazaiyi kyau haka ba,to itadai bataga laifi ba,idan ma yayin ba duka yaransu bane shi da ita?.
Taso sharewa itama,amma sai zuciyarta ta gaza nutsuwa da hakan,wannan dalilin yasa ta bashi kusan awa guda,sannan ta tattara kayan abincin tana ta mita a ranta na wahalar da ya bata na diban abincin tayi sashensa.
Da sallama ta tura qofar bedroom din nasa,sassanyan qamshinsa ya fara mata maraba,babu wadataccen haske a dakin sosai,yana daga gefe saman dan table din da yake dora system dinsa yayi wasu ayyuka da suka shafeshi yana duba wasu takardu.