← Book details A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 106 OF 111

Sashe 106

A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cikin wasu lafiyayyun indian blazers ya shirya blue black din shima,tamkar yasan color din da zata saka kenam,tun daga nesa kwalliyarta ta tsone masa ido,ya zuba mata dukka idanun nasa yana takowa a hankali,ko qifta idanunsa a kanta qyashin yi yakeyi.

Cikin jikinta taji yana wajen,saita daga kanta ta sauke a kansa,kamar shi,itama kwalliyar sa tatafi da ita ainun,yayi wani mugun kyau,ya koma yaro sosai da bai wuce sha tara zuwa ashirin ba,murmushi ya subuce mata,bakinta ya dinga motsawa tana jiran ya qaraso ta tsokaneshi,saidai dab da zai qaraso din hafsat ta bayyana,ta kwaso sauri cikin baqar abaya data saka ta yafa baqin mayafi wanda ya kasa zama a kafadarta saboda sauri dason ta cimmasu kafin sukai ga fita.

Ganinta sukayi kawai tana kiciniyar bude gaban motar tana cewa

"Banajin dadi abban mimi,ka miqa ni asibiti don Allah" tayi maganar tana shigewa gaban motar.

Da kallo dukkansu suka bita,widad ce ta fara dauke kanta kamar bata ga abinda tayi ba,sai ta matsa ta dauke handbag dinta dake saman motar ta juya zuwa cikin gida

"Ina zuwa kuma?" Dan dakatawa tayi da tafiyar

"Na fasa zuwa ne" iska ya furzar

"Aah,kizo Muje na fara sauketa saina qarasa dake" kai ta girgiza

"Um um.....naje ko gobe ko jibi" ta fada tana qoqarin boye damuwa sa fushinta,kawai ba zata iya hada mota da hafsat din ba,kallo daya tayi mata tasan neman rigima ya fiddota,dazun da umar yazo karbar kayansu mimi taji yana wayar jiya yakai hafsat din asibitin awo

"No....,wuce muje" ya fada yana takowa inda take tsaye,yana karbe jakarta daga hannunta

"Uncle....."

"Wai ba magana ake dake ba!.....yara suyita musu da na gaba dasu,kaga abban mimi just leave her mu tafi kawai" hafsat ta fada cikin tsawa,bayan baqincikin yadda taga yana lallabarta hadi da riqe mata jaka ya saukar mata ya tsaya mata a qirji.

A sukwane widad din ta waiwayo tana jin wutar dai dai take da ita a yau tana tashi cikin kanta,fes ta kalleta ido cikin ido,cikin lallausar muryarta a nutse ta amsata

"Sorry mommy....bafa dake nake ba......da uncle dina......au mijina na,da mijina nake magana"

*H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Page 97

"Sorry mommy.....bafa dake nake ba,da uncle dina,oh mijina,da mijina nake magana" widad din ta fada kanta tsaye,idanunta cikin na hafsat.

Wani abu mai nauyi hafsat din taji kamar an aza mata,kanta ya buga har tana jin wasu sautuka cikin kunnuwanta,ita widad din yau take kalla kai tsaye.....kuma kai tsaye,ido cikin ido take gayawa haka?,a gabanta take kiran abbas da mijinta?.

Kafin ta yanke abun yi har widad din ta soma qoqarin zame jakarta daga hannun abbas din,saidai yaqi cika mata,ganin yaqi cika matan saita juya ta fara takawa tana nufar sassanta,tana jin zuciyarta na mata qunci,batasan me yasa mommyn mimin keson shiga harkarta ba,bayan ita ko ganinta batason yi,batason su hada inuwa guda da ita, infact haushinta ma takeji,musamman lokuttan da zata gansu tare da uncle dinta.

Sanda hafsat din ta yunqura da nufin fita a motar tabi bayan widad din abbas yayi gaba,sai tayi mutuwar zaune tana binsa da kallo tare da son ganin inda zaiyi,zuciyarta na wani irin bugawa,tana fatar ba bayan widad din xaibi ba,yadda ta zata hakance ta faru,sassan widad din ya shige.

Tana shiga ta zare dankwalinta ta aje saman kujera,itama ta haye kujerar wayarta na hannunta tana ci gaba da chat dinta,duk da ranta a bace yake sosai amma batason tabar idanunta da suka tara hawaye su zubda qwalla.

Daga bakin qofa ya tsaya hannuwansa cikin aljihun wandonsa,ya zuba mata ido yana kallonta,qamshinsa ya sanyata gane ya shigo,ta daga kai sau daya ta kalleshi ta maida kanta ga chat dinta,qaramin murmushi yaso subuce masa,yana saurin karantarta fiye da kowacce mace a duniya,ya gane fushi takeyi amma batason nunawa,amma kuma shi bashi yayi laifin ba amma abun yana son qarewa a kansa,sai ya tako ya iso gabanta,ya zame a hankali ya duqa saman qafafunsa,ya riqe hannayenta da take chat din dasu yana duban qwayar idanunta

"Tashi mu tafi weedad......" Ya kira ainihin sunanta a tausashe,kawai tana daga kai suka hada ido dai kuka ya kufce mata,ya matse hannayenta gam cikin nasa yana jin wani abu na masa suka cikin zuciyarsa,bayason kuka sam,kukan ma kuma nata,bai hanata ba sai datayi kusa minti goma tana yi,sannan ta zare hannunta daga nashi ta dauki dankwalinta ta nufi bedroom dinta.

Binta yayi da kallo,bai taba zaton zata bisun ba,amma ga mamakinsa sai gata ta fito,ta wanke fuskarta fes ta sake shafa powder da lip gloss,ta zizarawa fararen idanuwanta kwalli

"Muje" ta fada fuskarta babu walwala,yi yayi kamar baiji ba amma idanunsa suna kanta,har zuwa sanda ta tako tazo dab dashi xata wuce sai ya matse mata hanya,ya kuma sanyata cikin jikinsa

"Bakya kyau da fushi baby doll,smile please" ya rada mata a kunne,a hankali murmushi ya kubce mata tana dan boye fuskarta.

Tuni ta gama cika ta batse,duk inda bacin rai yakai ranta yakai qololuwar zuwa wajen,sau biyu tana aika mimi tayi kiran daddynsu sai tace qofar na a rufe ne,gashi tashi yanzu wuya yake mata,har sai data yunqura zata fita taje da kanta ayi wadda za'a yi,sai gasu sun fito.

Sanda ta kalli fuskokinsu ji tayi qafafun ta sun riqe,haka abbas din zaiyi mata?,fuskar widad din kamar ma komai bai faru ba,ta shaqa iya shaqa,sai taji kamar numfashinta xai dauke,dole ta kauda kai daga kallonsu,wata zuciyar na bata shawarar ta fice a motar kawai tace ta fasa zuwa,amma sai wani sashen na zuciyarta ke gaya mata,idan tayi hakan ai kamar taci galaba a kanta kenan.

Fuska fs muryarta duka wasai tana tsokanar mimi daketa shirya beads masu dauke da alphabet nawwara na watsa mata,ta buda gidan bayan ta shige,taja yarinyar jikinta ta kama hannunta tana tayata saka beads din tare da warning nawwara cikin wasa kan kada ta sake ta taba musu.

Tsantsar baqinciki da bacin rai ya hana hafsat din magana har suka isa asibitin aka sauketa,taso bar musu yaran duka amma nawwara taqi sai mimi ce tabi widad din.

Abinda bata sani ba kwata kwata yara basa damun widad,hasalima ita din mayyar yara ce,ko hana mimi zuwa tayata kwana da takeyi hakan baya mata dadi kwata kwata,ita kadai tasan yadda taji,baya ga dan uban tsoron dake bibiyarta harda kewar yaran.

Kamar ko yaushe zama yayi a waje ya jirasu har aka gama,wannan karonma mimi ta samu albarkacin widad din,an wanke mata kan tsaf,yarinyar sai murna take tana shafa sumartata tana kallon widad

"Anty ashe da dadi" sarai widad ta fahimci me take nufi,tana nufin kanta yayi mata sawai,kuma ta tabbatar iska mai dadi yanzu tana shiga kan.

Tunda suka iso gidan,tun basu shiga ba gaba daya aka saukar mata da bacin rai da baqinciki,taji kamar ta cewa abbas don Allah kada ya shiga ya koma da ita,haka ta dinga qoqarin dannewa har ya saka kan motarsa cikin gidan.

Tana tsaye daga bakin window tana hangen komai dake faruwa cikin gidan,don haka tana hangen sanda ya ajjiyeta ya koma,ta jijjiga kai tana sakin labulen falon.

Da daren ranar ta dinga tsoron kada abinda ya faru xuwanta na qarshe bauchi ya sake maimaita kansa,idan ta runtse ido saita bude,ba motsin komai ko alamu na faruwar wani abu,daga baya tayi dukka addu'o'inta don haka ta samu relief sosai,saidai gidan gaba daya taji ta tsaneshi,tsananin tsana ta gasken gaske,a lokacin taji bata da wata buqata data wuce tabar gidan,bata da wata buqata data wuce ta ganta ba cikin gidan ba,haka ta dinga yawo tsakanin falonta zuwa bedroom,sai tayi kamar zata fita saita koma bakin qofa ta zauna ta fashe da kuka,kusan awa uku tana a wannan halin kafin daga bisani bacci yayi awon gaba da ita a nan bakin qofar a yashe a qasa.

*W A S H E G A R I*

Yadda parlor din yake fitar da sassanyan qamshi mai dadi,hakanan jikinta yake fidda nashi salon qamshin daban,girkinta ne ko ba girkinta ba,wannan duka bai dameta ba,kusan qamshi da tsafta sun zame mata gaado idan ana gadonsu,tun daga hannun ummu kawo yanzu.

Ita daya ce a parlor din,kwance cikin doguwar kujera mai cin mutum biyu,wani doguwar rigar material onion color ne a jikinta mai gajeran hannu,kanta babu dankwali sai sassalkar sumarta mai tsaho baqi da santsi data dameta cikin robber band,sai qyalli take saboda gyaran kan da taje shekaran jiya, hannunta wayarta ce,sunata hira da balkisa,bata jin dadin zaman ita daya,yau gaba daga ko dauriyarsa mimi ba,abinda bata sani ba hafsat dince ta hanata shigowa kwata kwata,ita kuwa koda wasa batayi gefan hafsat din ba,indai ba dalili bane ya hadasu a farfajiyar gidan,suna iya gama kwanakinsu duka basu hadu ba,hatta da gaisuwa da take zuwa mata a yanzun ta ajjiyeta gefe,idan sun hadu su gaisa,idan basu hadu ba fine,ta bawa bilkisa labari, bilkisan tana ta tsokanarta

"Sanda nace ki daina gani kikayi kamar sabo nayi ko?,yanzu fa?" Dariya kawai tayi,its har ga Allah zafin hafsat takeji,batason ma su faye haduwa,data gayawa balkisa dalili sai da tayi dariya sosai

"Anya widad,anya kuwa?,wannan zazzafar soyayya mai cike da kishin tsiya da akewa uncle?"

"Kishi kuma anty?"

"Qwarai da gaske" ta jima a ranar tana son gane banbanci tsakanin kishi da kuma abinda takeji akan hafsat din.

Sake gyara kwanciyarta tayi tana jin yadda gaba daya cikinta yake a cushe,duka cikin kwanakin nan bata jin dadin cikinta da jikinta sam,sai tajishi kamar a kushe,mararta babu dadi,amma saita danganta hakan da rashin zuwan period dinta da take saka ran ko yaushe zata iya ganinsa,tun tana lissafi da xuba ido harma ta share taci gaba da harkokinta hadi da cewa cikin ranta

"Wai meye ma don baizo ba zan damu?,nima na huta da takurarsa" har zata gayama abbas saita fasa,tana tsoron kada yace suje asibiti,daga nan ace sai anyi allura.

Tsayawa tayi da replying massage din da takeyi sanda sassanyan sound din data sama wayarta na musamman saboda shi ya shigo

"Baby uncle" shine sunan da tayi saving dashi, qaramin murmushi ya kubce mata saman fuskarta,bata gajiya da ganinsa,duk sanda zata bar kwana sassansa hafsat ta karba tana jin raunin zuciya sosai,tana jin kamar ta riqeshi ya barta tayita kwana,amma bata iya hakan.

Karbar jakarsa data gani daxun hafsat tayi ta kuma bishi sassansa ya fado mata a rai,saita tura baki sannan ta daga wayar a shagwabe tayi masa sallama.
Chapter 106 · 0% Book details