Sashe 105
A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
zuwa dare ta dinga masa kuka saboda yadda wata muguwar tsanar gidan ta shigeta,ta dinga kuka sai sun koma kaduna,ba shiri cikin daren ya soma hada musu kayansu,bai kwanta ba sai daya gama shirin tafiyar tasu.
Da safen ta tashi da 'yar walwalarta saboda jin zasu tafi,kafin ya gama nasa shirin ita tuni ta gama,sanda ya kammala shiryawar kuwa zaije ya sallami su hafsat farfajiyar gidan ta fito ta zauna tana jiransa,sam bata doshi wajen hafsat din ba,haushinta takeji musamman duk sanda zasu kebe da uncle din nata,ko zata ganta kusa dashi,idan wani abu ya kawo ga ta tabashi kuwa saidai tabar wajen tana goge qwalla,ita kanta batasan manufar hakan ba,batasan kuma abinda yake kawo mata jin hakan a zuciyarta ba (kishi😄, Allah sarki,quruci dangin hauka,ta fara kishin uncle din nata ba tare data sani ba).
Tana tsaye daga bakin window din falonta tana hangensu sanda ya gama sallamarta ya fice,bayan ta gama mita da qorafin akwai sauran kwana daya daya rage ai bai cika shi ba,bai biyewa qorafin ta ba,don koma yaya yayi dai sai ta yishi,ya zama kamar cikin jininta abun yake.
Murmushi ta sauke sanda suka fice din,cikin wata walwala da jin dadi ta fada saman kujera tana tunano abubuwa masu yawa a zuciyarta,lallai a baya ita taso har aka kai wannan matsayin ma da ake kai yanzu kamar yadda ummanta ta gaya mata,ashe wannan hanyar itace hanya mafi sauqi da sauri ta maganin matsalar ta ta tsaya tana biyewa hasashe da hanyoyin anty ummee masu tsauri?.
Assalamualaikum
Yanzu an wuce lokacin da za'a dinga novel na qaryar soyayya tsura kawai a ciki da uban tarin dukiya daga qasa zuwa qasa,dole mu fuskanci reality na abubuwan da suke faruwa yanzu suke damunmu,akwai darasi sosai da nakeso mu cimma cikin labarin nan,kuyi haquri muje harmu cimma gaci
Sannan tun asali duk wanda ya sanni labaraina ba gajeru bane,daga bayan nan ne nake gajeru,to wanann salon labarin yazo a haka ne,sanann raguwar tsahon pages din yasa numbers din sukayi yawa,amma in sha Allah i will try my best naga pages din sun dan qara tsaho ta yadda numbers din zasu ragu, thanks for choosing me.
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks: Huguma*
Page 96
Wata wawiyar ajiyar zuciya ta saki tana samun nutsuwar ruhi da gangar jiki sanda taga sun dauki hanyar kaduna,duk da jikinta babu wani qwari sosai saboda zazzabin daya gallabeta,amma at least ta samu wani sassaucin.
Dan waiwayo yayi kadan ya dubeta,sannan ya cire hannunsa guda daya daga kan motar ya kama dogon hancinta yadan ja
"Hankalinki ya kwanta ko?" Saita sakar masa murmushi, murmushin da yayi masifar kewarsa,yaketa kuma struggling na ganin tayi shin amma bai sameshi ba sai yau.
Tun basuyi nisa ba ta soma bacci,wani irin nannauyan bacci da shi kansa abbas din ya dinga kallonta,ko sau daya baiyi.marmarin tashinta ba,baccin ma datayin dadi yayi masa,aqalla yasan zata rama bashin baccin da batyi ba kwana biyu,sai ya kunna radio station yana sauraren labarai,da sauran programs da suka jibanci harkokin tsaro,da ya gaji ya maida karatun qur'ani,wanda ya qarawa baccinta dadi sosai,baccin da bata farka ba sai da suka isa kaduna.
Tun daga wannan ranar bata sake binsa bauchi ba,don ko cewa yayi zasu weekend yanzu zata rage walwala,gaba daya garin ya fita a ranta,shima bai takurawa, don asalinsa ba mutum bane mai takura da tsanani akan abu bane,sai ya barta yaje yayi kwana biyu ya dawo,har kusan watanni uku.
Cikin hakan bikin diyar yaaya bara'atu ya taso,ya gaya mata,duk da bataso amma ta gaza nuna masa,yana da tsananin kirki da karamci,yana mata kyautatawar da duk duniya baya ga ummu bata ganta a wajen kowa ba,wannan ya sanya duk wani abu da tasan bayaso ko zaiji babu dadi take nisantarsa(bawai don tasan muhimmancin hakan ba,kawai saboda yadda kyautatawarsa taje da nauyi a idanunta).
Kaya ta fitar ta bayar akayi mata dinkuna masu kyau, zuciyarta duka babu dadi,cike da tsanar bauchin amma haka ta dinga shirya,duk da tana boyewar amma ya karanci akwai abinda ke faruwa,don kuzarinta ya ragu,a sanyaye take komai.
Ana gobe zasu tafi da daddare,yana zaune kan sofa bed yana shan black tea din data hada masa ita kuma tana rufe wata qaramar jakarta data zuba qananun abubuwan amfaninsa da tasan zai buqata,duk inda ta gifta idanunsa yana biye da ita,baya gajiya da kallonta,barin yau din da tayi kwalliya ciki wani mini skert da wata riga da sukayi matuqar karbarta,zuwa lokacin komai nata ya cika yayi yadda akeso ya zamana a jikin diya mace,ta zama wata 'yar duma duma da ita,haske da laushin fatarta ya qaru,hakanan tsahon gashinta cikarsa dama baqinta,lips dinta ya qara zama pink sosai haka idanunta sun sake fitowa,ta fannin mu'amalarsu ya sake zama wani mayenta,shi kansa baisan yadda akayi ya sake horancewa ba,baiqi duka dare ya dinga kasancewa da ita ba,baya gajiya da ita,wata baiwa ke gareta ta musamman mai dimauta tunanin mutum,saidai widad din tashi har yanzu raguwa ce,batayi qwarewar da yakeso tayi ba,kullum hakan ta kasance sai yayi zaman lallashi,shagwabarta da sangarta take zube masa,shima sai ya biye mata.
Ajjiye mug din hannunsa yayi yana fakon isowarta,aikuwa tana zuwa giftashi ya sanya hannu ya fincikota jikinsa,yayi mata kyakkyawan masauki saman cinyarsa dake bayyane a waje cike da gargasa,hannuwansa ya saka ya zagaye qugunta dasu ya sake matso da ita sosai,ya saka fuskarsa a tsakiyar dukiyar fulaninta yana shaqar qamshin dake fita a wajen.
Hannu ta saka ta riqe kansa,tana jin tsigar jikinta tana tashi saboda yadda labbansa suka sauka a wajen,ta saki dariya tana janye jikinta baya,ya daga idanunsa da suka fara sauya launi yana murmushin shima ya kalleta
"Kamar baki shiryawa zuwa bauchin nan ba" kanta ta langabar gefe,a zahiri batason zuwan,amma bai kyautu ta nuna masa ba,saita girgiza kai
"Aah,kawai kasala nakeji kwana biyun"
"Nayi noticing canji da yawa,kin koyi bacci,sannan ga overdose kyau baby da kike qarawa,overdose dad......" Hade bakinsu tayi waje daya yau da kanta,don batason ya qarasa fadin kalmar,bala'in sakata jin kunya takeyi,hakan da tayin saita tafi dashi wata duniyar ta daban,tasa ya dimauce ya mance dukka maganar da zai fada din,sanda zata qwace kanta kuma yace baisan zance ba,sai da ya cimma gaci sannan ya samu nutsuwa.
Washegari da wuri suka isa,don sha biyun rana ma a can tayi musu,sassanta ta wuce kai tsaye,gidan duk bai mata dadi ba saboda su mimi basa nan,hajiya tasa anzo an daukesu,an musu kitso da qunshi kamar yaran kowa,an kuma dauki kayansu sai bayan biki zasu dawo.
Wannan karon hafsat din bata hana ba,bata ma isa ta hana din ba don tasan abbas din ko zai jure komai banda wannan,kuma kai tsaye shi yayi kiranta yace ta bada yaran,ta hada musu tarkacen kayansu,gasu dai a ido masu kyau da tsada ne,amma dauda da rashin kula duk sunci mutuncinsu.
Tsaye hajiya tayi kawai cikin takaici tana qarewa kayan kallo,banda ma gidan yana samun feshin maganin qwari da kuma gyaran da uban kewa dakin nasu duk sanda ya samu chance....ta tabbatar ba za'a rasa wani qwaron a ciki ba,hajiyan nada masifar tsafta,sai tattara kayan tasa akayi aka bayar,banda ma masu tsada ne da kuma sauran qwarinsu qazanta ce ta cinyesu,a wajen hajiyan bola ce tafi kamata dasu.
Har ta fitar da kudi ta bayar za'a sake musu sabuwar siyayya mimi tace akwai wasu kayansu a wajen anty widad.
Hajiyan da kanta ta kira widad din tace mimi tace suna da kaya a wajenta,ta fiddo musu dasu umar zaizo ya karba,tana shiga sassanta kayan ta fara hadawa,a killace a tsaftace a kuma goge,umar din ya karba ya tafi dasu.
Tunda ta sauka gidan ranta yayita baci,gaba daya kamar an tattaro dukka bacin rai an aza mata,haka ta dinga dannewa,ta hau gyaran sashen nata,sai data tabbatar komai yayi neat din ta sake wanka ta canza kaya,ta dauki wayarta ta kira abbas don tanason zuwa saloon da qunshi,na qafafunta duka sun fita,kuma batason shiga mutane haka,abinka da farar fata, babban adon hannayensa da kyan ganinsu ayi musu qunshi.
Lokacin yana tsaye a qofar toilet yana amsa wayar Jasmin yana jiran hafsat dake ciki ta gama wanke masa zai shiga saboda dan uban qurar daya hada,bata damu ta shiga ta gyara ba,sai ya bawa Jasmin excuse ya katse kiran nata ya daga na widad din.
Cikin shagwabar nan tata dake sake narkar dashi tace
"Uncle"
"Babyn uncle" ya amsa mata tattausan murmushi yana subuce masa,sunan da hafsat taji ya kira saita miqe tsaye dafe da cikinta ta kasa kunne tana sauraren hirar
"Zanje saloon da qunshi,kaina da hannuwana duka ba dadi"
"Ba laifi,amma baby......ina kishi fa gaskiya,ki zaba duk inda kikeso zan sa a kira miki su har gida special services mana" kafada ta noqe,ita zaman gidan ne bataso har ga Allah
"Don Allah uncle,yaushe rabon da nazo bauchi" ta fada da wata irin narkakkiyar shagwaba da har data sakashi lumshe ido ba tare daya shirya ba
"Shikenan,ki shirya zan fita headquarter yanzu,sai mu biya"
"Thank youuuuuuu" ta fada tana dariya
"You are welcome" ya amsa yana sauke wayar sannan ya sake kiran Jasmin yace mata zai shigo nan da minti talatin.
Sauri sauri tayi ta gama wankewa ta fice ta bashi waje,ya shiga ya hada ruwan wankansa da kansa,abinda bai sani ba kenan muddin suna tare da widad.
Sassanta ta nufa tana sakin ashar cikin zuciyarta,ita ta dauka ma wannan karon shi kadai yazo,ashe sai data sake biyoshi,akwai sauran rina a kaba kenan?,saita jinjina kai,ta buda wardrobe dinta ta fiddo kayan sawa,sannan ta buda bandakinta ta shiga ta fara kwaskwarima.
Cikin wata doguwar rigar atamfa da tayi mugun budewa daga qasa ta shirya,brown ce mai adon blue black,tayi amfani da blue black hand bag veil da kuma takalmi,kalar ta haska farar fatarta da kyau, daurin da tayi wanda ta kawoshi gaban goshi ta fidda gashinta ta qasan daurin ya qara mata wani irin kwarjini,ko yaya ta motsa jikinta qamshi yake fitarwa.
Saboda saurin da take ta fita a gidan ta rigashi isa parking lot,tayi tsaye jikin motar tana jiran fitowarsa,wayarta sabuwa da ummu ta aiko mata da ita a hannunta suna hira da bilkisa ta watsapp,tana ta kwasan dariya,don bikisa din ba daga baya ba,ko yaushe qoqarinta taga ta dora widad din kan hanya,ta kuma ganar da ita wace hafsat.
Da safen ta tashi da 'yar walwalarta saboda jin zasu tafi,kafin ya gama nasa shirin ita tuni ta gama,sanda ya kammala shiryawar kuwa zaije ya sallami su hafsat farfajiyar gidan ta fito ta zauna tana jiransa,sam bata doshi wajen hafsat din ba,haushinta takeji musamman duk sanda zasu kebe da uncle din nata,ko zata ganta kusa dashi,idan wani abu ya kawo ga ta tabashi kuwa saidai tabar wajen tana goge qwalla,ita kanta batasan manufar hakan ba,batasan kuma abinda yake kawo mata jin hakan a zuciyarta ba (kishi😄, Allah sarki,quruci dangin hauka,ta fara kishin uncle din nata ba tare data sani ba).
Tana tsaye daga bakin window din falonta tana hangensu sanda ya gama sallamarta ya fice,bayan ta gama mita da qorafin akwai sauran kwana daya daya rage ai bai cika shi ba,bai biyewa qorafin ta ba,don koma yaya yayi dai sai ta yishi,ya zama kamar cikin jininta abun yake.
Murmushi ta sauke sanda suka fice din,cikin wata walwala da jin dadi ta fada saman kujera tana tunano abubuwa masu yawa a zuciyarta,lallai a baya ita taso har aka kai wannan matsayin ma da ake kai yanzu kamar yadda ummanta ta gaya mata,ashe wannan hanyar itace hanya mafi sauqi da sauri ta maganin matsalar ta ta tsaya tana biyewa hasashe da hanyoyin anty ummee masu tsauri?.
Assalamualaikum
Yanzu an wuce lokacin da za'a dinga novel na qaryar soyayya tsura kawai a ciki da uban tarin dukiya daga qasa zuwa qasa,dole mu fuskanci reality na abubuwan da suke faruwa yanzu suke damunmu,akwai darasi sosai da nakeso mu cimma cikin labarin nan,kuyi haquri muje harmu cimma gaci
Sannan tun asali duk wanda ya sanni labaraina ba gajeru bane,daga bayan nan ne nake gajeru,to wanann salon labarin yazo a haka ne,sanann raguwar tsahon pages din yasa numbers din sukayi yawa,amma in sha Allah i will try my best naga pages din sun dan qara tsaho ta yadda numbers din zasu ragu, thanks for choosing me.
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks: Huguma*
Page 96
Wata wawiyar ajiyar zuciya ta saki tana samun nutsuwar ruhi da gangar jiki sanda taga sun dauki hanyar kaduna,duk da jikinta babu wani qwari sosai saboda zazzabin daya gallabeta,amma at least ta samu wani sassaucin.
Dan waiwayo yayi kadan ya dubeta,sannan ya cire hannunsa guda daya daga kan motar ya kama dogon hancinta yadan ja
"Hankalinki ya kwanta ko?" Saita sakar masa murmushi, murmushin da yayi masifar kewarsa,yaketa kuma struggling na ganin tayi shin amma bai sameshi ba sai yau.
Tun basuyi nisa ba ta soma bacci,wani irin nannauyan bacci da shi kansa abbas din ya dinga kallonta,ko sau daya baiyi.marmarin tashinta ba,baccin ma datayin dadi yayi masa,aqalla yasan zata rama bashin baccin da batyi ba kwana biyu,sai ya kunna radio station yana sauraren labarai,da sauran programs da suka jibanci harkokin tsaro,da ya gaji ya maida karatun qur'ani,wanda ya qarawa baccinta dadi sosai,baccin da bata farka ba sai da suka isa kaduna.
Tun daga wannan ranar bata sake binsa bauchi ba,don ko cewa yayi zasu weekend yanzu zata rage walwala,gaba daya garin ya fita a ranta,shima bai takurawa, don asalinsa ba mutum bane mai takura da tsanani akan abu bane,sai ya barta yaje yayi kwana biyu ya dawo,har kusan watanni uku.
Cikin hakan bikin diyar yaaya bara'atu ya taso,ya gaya mata,duk da bataso amma ta gaza nuna masa,yana da tsananin kirki da karamci,yana mata kyautatawar da duk duniya baya ga ummu bata ganta a wajen kowa ba,wannan ya sanya duk wani abu da tasan bayaso ko zaiji babu dadi take nisantarsa(bawai don tasan muhimmancin hakan ba,kawai saboda yadda kyautatawarsa taje da nauyi a idanunta).
Kaya ta fitar ta bayar akayi mata dinkuna masu kyau, zuciyarta duka babu dadi,cike da tsanar bauchin amma haka ta dinga shirya,duk da tana boyewar amma ya karanci akwai abinda ke faruwa,don kuzarinta ya ragu,a sanyaye take komai.
Ana gobe zasu tafi da daddare,yana zaune kan sofa bed yana shan black tea din data hada masa ita kuma tana rufe wata qaramar jakarta data zuba qananun abubuwan amfaninsa da tasan zai buqata,duk inda ta gifta idanunsa yana biye da ita,baya gajiya da kallonta,barin yau din da tayi kwalliya ciki wani mini skert da wata riga da sukayi matuqar karbarta,zuwa lokacin komai nata ya cika yayi yadda akeso ya zamana a jikin diya mace,ta zama wata 'yar duma duma da ita,haske da laushin fatarta ya qaru,hakanan tsahon gashinta cikarsa dama baqinta,lips dinta ya qara zama pink sosai haka idanunta sun sake fitowa,ta fannin mu'amalarsu ya sake zama wani mayenta,shi kansa baisan yadda akayi ya sake horancewa ba,baiqi duka dare ya dinga kasancewa da ita ba,baya gajiya da ita,wata baiwa ke gareta ta musamman mai dimauta tunanin mutum,saidai widad din tashi har yanzu raguwa ce,batayi qwarewar da yakeso tayi ba,kullum hakan ta kasance sai yayi zaman lallashi,shagwabarta da sangarta take zube masa,shima sai ya biye mata.
Ajjiye mug din hannunsa yayi yana fakon isowarta,aikuwa tana zuwa giftashi ya sanya hannu ya fincikota jikinsa,yayi mata kyakkyawan masauki saman cinyarsa dake bayyane a waje cike da gargasa,hannuwansa ya saka ya zagaye qugunta dasu ya sake matso da ita sosai,ya saka fuskarsa a tsakiyar dukiyar fulaninta yana shaqar qamshin dake fita a wajen.
Hannu ta saka ta riqe kansa,tana jin tsigar jikinta tana tashi saboda yadda labbansa suka sauka a wajen,ta saki dariya tana janye jikinta baya,ya daga idanunsa da suka fara sauya launi yana murmushin shima ya kalleta
"Kamar baki shiryawa zuwa bauchin nan ba" kanta ta langabar gefe,a zahiri batason zuwan,amma bai kyautu ta nuna masa ba,saita girgiza kai
"Aah,kawai kasala nakeji kwana biyun"
"Nayi noticing canji da yawa,kin koyi bacci,sannan ga overdose kyau baby da kike qarawa,overdose dad......" Hade bakinsu tayi waje daya yau da kanta,don batason ya qarasa fadin kalmar,bala'in sakata jin kunya takeyi,hakan da tayin saita tafi dashi wata duniyar ta daban,tasa ya dimauce ya mance dukka maganar da zai fada din,sanda zata qwace kanta kuma yace baisan zance ba,sai da ya cimma gaci sannan ya samu nutsuwa.
Washegari da wuri suka isa,don sha biyun rana ma a can tayi musu,sassanta ta wuce kai tsaye,gidan duk bai mata dadi ba saboda su mimi basa nan,hajiya tasa anzo an daukesu,an musu kitso da qunshi kamar yaran kowa,an kuma dauki kayansu sai bayan biki zasu dawo.
Wannan karon hafsat din bata hana ba,bata ma isa ta hana din ba don tasan abbas din ko zai jure komai banda wannan,kuma kai tsaye shi yayi kiranta yace ta bada yaran,ta hada musu tarkacen kayansu,gasu dai a ido masu kyau da tsada ne,amma dauda da rashin kula duk sunci mutuncinsu.
Tsaye hajiya tayi kawai cikin takaici tana qarewa kayan kallo,banda ma gidan yana samun feshin maganin qwari da kuma gyaran da uban kewa dakin nasu duk sanda ya samu chance....ta tabbatar ba za'a rasa wani qwaron a ciki ba,hajiyan nada masifar tsafta,sai tattara kayan tasa akayi aka bayar,banda ma masu tsada ne da kuma sauran qwarinsu qazanta ce ta cinyesu,a wajen hajiyan bola ce tafi kamata dasu.
Har ta fitar da kudi ta bayar za'a sake musu sabuwar siyayya mimi tace akwai wasu kayansu a wajen anty widad.
Hajiyan da kanta ta kira widad din tace mimi tace suna da kaya a wajenta,ta fiddo musu dasu umar zaizo ya karba,tana shiga sassanta kayan ta fara hadawa,a killace a tsaftace a kuma goge,umar din ya karba ya tafi dasu.
Tunda ta sauka gidan ranta yayita baci,gaba daya kamar an tattaro dukka bacin rai an aza mata,haka ta dinga dannewa,ta hau gyaran sashen nata,sai data tabbatar komai yayi neat din ta sake wanka ta canza kaya,ta dauki wayarta ta kira abbas don tanason zuwa saloon da qunshi,na qafafunta duka sun fita,kuma batason shiga mutane haka,abinka da farar fata, babban adon hannayensa da kyan ganinsu ayi musu qunshi.
Lokacin yana tsaye a qofar toilet yana amsa wayar Jasmin yana jiran hafsat dake ciki ta gama wanke masa zai shiga saboda dan uban qurar daya hada,bata damu ta shiga ta gyara ba,sai ya bawa Jasmin excuse ya katse kiran nata ya daga na widad din.
Cikin shagwabar nan tata dake sake narkar dashi tace
"Uncle"
"Babyn uncle" ya amsa mata tattausan murmushi yana subuce masa,sunan da hafsat taji ya kira saita miqe tsaye dafe da cikinta ta kasa kunne tana sauraren hirar
"Zanje saloon da qunshi,kaina da hannuwana duka ba dadi"
"Ba laifi,amma baby......ina kishi fa gaskiya,ki zaba duk inda kikeso zan sa a kira miki su har gida special services mana" kafada ta noqe,ita zaman gidan ne bataso har ga Allah
"Don Allah uncle,yaushe rabon da nazo bauchi" ta fada da wata irin narkakkiyar shagwaba da har data sakashi lumshe ido ba tare daya shirya ba
"Shikenan,ki shirya zan fita headquarter yanzu,sai mu biya"
"Thank youuuuuuu" ta fada tana dariya
"You are welcome" ya amsa yana sauke wayar sannan ya sake kiran Jasmin yace mata zai shigo nan da minti talatin.
Sauri sauri tayi ta gama wankewa ta fice ta bashi waje,ya shiga ya hada ruwan wankansa da kansa,abinda bai sani ba kenan muddin suna tare da widad.
Sassanta ta nufa tana sakin ashar cikin zuciyarta,ita ta dauka ma wannan karon shi kadai yazo,ashe sai data sake biyoshi,akwai sauran rina a kaba kenan?,saita jinjina kai,ta buda wardrobe dinta ta fiddo kayan sawa,sannan ta buda bandakinta ta shiga ta fara kwaskwarima.
Cikin wata doguwar rigar atamfa da tayi mugun budewa daga qasa ta shirya,brown ce mai adon blue black,tayi amfani da blue black hand bag veil da kuma takalmi,kalar ta haska farar fatarta da kyau, daurin da tayi wanda ta kawoshi gaban goshi ta fidda gashinta ta qasan daurin ya qara mata wani irin kwarjini,ko yaya ta motsa jikinta qamshi yake fitarwa.
Saboda saurin da take ta fita a gidan ta rigashi isa parking lot,tayi tsaye jikin motar tana jiran fitowarsa,wayarta sabuwa da ummu ta aiko mata da ita a hannunta suna hira da bilkisa ta watsapp,tana ta kwasan dariya,don bikisa din ba daga baya ba,ko yaushe qoqarinta taga ta dora widad din kan hanya,ta kuma ganar da ita wace hafsat.