Sashe 63
A Rubuce Take Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kina ina?" Ta tambayeta kanta tsaye ba tare da tabi takan gaisuwar da take mata ba
"Ina daki"
"Wanne dakin?" Ta tambayeta daga can gabanta yana faduwa
"Dakina"
"Abbansu mimi yace baki da lafiya jiya,me ya sameki?" Gabanta ya yanke ya fadi data tuna cewa a dakinsa ta kwana jiya,kuma koda ra farka cikin jikinsa ta ganta,ta fahimci hakanne?,kota gane?
"Ciwon mara" ta amsa mata muryarta nadan rawa kadan,abinda ya sake sanya shakku a zuciyar hafsat din,tsoronta ya ninku
"Kodai wani abun kukayi ke dashi?" Tambayar daketa mata yawo tsakar ka ta subuce ta fito daga bakinta,da sauri ta hau girgiza kai kamar tana a gabanta ne,hawaye kuma suka jiqa mata fuska
"A'ah mommy....wallahi ba komai,ciwon mara ne kawai Allah ki yarda gaskiya na fada miki" boyayyar ajiyar zuciya ta saki,sanin weedad din bata qarya sai hankalinta yadan kwanta,amma saita fuske saboda ta samu nasarar sake dasa tsoron hakan a zuciyarta
"Ohon miki idan ma wani abun kika yarda yayi miki,mutuwa zakiyi.....ina ruwan wani,nima ina gaya miki ne don ina sonki banaso ki mutu"
"Allah mommy ba komai" sai kawai hafsan ta kashe wayar donta qara tsoratata.
Sosai hankalin weedad din ya tashi,tana shirin bin kiran taji ya turo qofar,ta daga kai tana kallonsa,har qasan ranta tana jin haushinsa,ya danji wani iri ganin tana kuka,yana fargabar ko wani abunne ya sameta,yasan yau bai leqota da kyau ba,duka yau ya kulle kansa ne a daki yana aikin tracing din wani criminal a sirrance,abinda yasa ya baro office kenan,bayaso kowa yasan abinda yakeyi
"Yaaya?.....jikinne?" Kai ta girgiza tana turo baki,ta kuma tura masa qeya taqi kallonsa
"To ma sha Allah"ya fada duk da ya fuskanci kamar cikin fushi take,shuru ya ratsa tsakani na sakanni kafin ya miqe
"Ki ajjiye komai ki kwanta" sai ya juya yana shirin barin dakin,binsa tayi da kallo,tana jin kamar ta bishi,amma da ta bishi ya tabata gwara ta zauna a dakinta.
A jikinsa yaji kamar tana kallonsa,don haka ya dakata ya waiwayo,suka hada ido saita dauke kai,kamar xaiyi magana sai kuma ya fasa,ya saka kai ya fita.
Tun bai kai tsakiyar falon ba yaji ihunta,ya juyo da sauri,sai gata sunyi kacibus a hanya har tana fadawa jikinsa,taja baya da sauri jikinta yana rawa
"Mm....mage"
"A ina?"
"Bakin window" ta fada tana duban qofar dakin
"Muje na gani" ya fadi yana sakata a gaba,kafada ta maqale tana sakin kuka,kome zaiyi mata bata jin zata yarda ta bishi,haka tayi tsaye a wajen ya shiga dakin,bai jimaba ya fito
"Bata shigo ba,infact ta wuce ma,zaki iya komawa" waiwaya tayi inda yake,taga da gaske tafiya yake zuwa dakinsa,ta daga qafarta da sauri tabi bayansa.
Batasan ta cimmasa ba sai da suka tsaya suna kallon kallo shi da ita,yana riqe da handle din qofar yana dubanta,itama shi take kallo saidai batace komai ba sai aukin hawayen da take faman zubarwa
"Don Allah...zan karka tafi ka barni"
"Bacci nakeji" ya amsa mata a taqaice,saita sake fashe masa da kuka,hannu ya sanya ya dafe goshinsa
"Oh my goodness" ya furta a hankali,saiya maida manyan idanunsa kanta
"Me kike so?" Shuru tayi kamar ba zata amsa ba,sai kuma tayi qasa da kanta
"Zan kwana a nan" ta fada a hankali gabanta yana faduwa,zuciyarta na gaya mata girman laifinta,ta yaya zata hada dakin kwana dashi?.
Qaramin murmushi ya saki
"Silly girl" ya fada qasa qasa,ga dan banzan tsoro ga shagwaba da sakarci harda na siyarwa,sai ya matsa gefe daya
"Bismillah" ya furta a hankali,ta rabeshi sosai ta shige dakin,ya rufe qofar ya sanya key sannan yabi bayanta.
Ta jima a zaune har ya gama komai na shirin kwanciya bacci tana binsa da idanu,pillow ya dauka ya jefar a qasa sannan yabi pillow din ya kwanta idanuwansa a rufe yana karanto addu'an bacci,ya gama ya shafe jikinsa,ba tare daya bude idanun ko ya dubeta ba yace
"Ki kwanta kiyi kuma addu'a" a takure take sosai saman gadon,duk kuwa da cewa ita daya ce,duk juyin da zatayi idanunta a kansa,har sai data ji saukar numfashinsa a hankali alamun bacci yayi awon gaba dashi,sannu a hankali itama jikinta ya saki,wani bacci me dadi wanda babu fargaba a ciki ya sureta.
KI KULANI miss xoxo
DAUDAR GORA Billynabdul
RUMBUN K'AYA hafsat rano
IDON NERA Mamuhghee
A RUBUCE TAKE huguma
_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_
_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_
0022419171
Maryam sani
Access bank
Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070
*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261
*Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number*
+227 96 09 67 63
*Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:huguma*
Page 57
To tun daga wannan rana kwananta ya dawo dakinsa,saidai tana kammala sallar asuba take komawa dakinta ta shirya shirin makaranta,wani lokaci shike kaita,wani lokacin kuma samuel ko daya daga cikin yaran dake qarqashinsa.
Aikin da yakeyi yasa a yanzun zamansa a gida yafi yawa,wannan ya fara haifar da shaquwa a tsakaninsu,duk da baya barin kowa ya rabi inda yake wannan aikin amma yawancin lokuta suna tare,badai hira sukeyi da ita ba,amma zata dauki littafinta ta zauna a wajen,ko ba komai tana jin motsinsa bata da kewa,lokaci bayan lokaci tana barin karatunta tadan zuba idanu tana kallonsa,idan sun hada ido kuma sai ta basar,murmushi kawai yakeyi ko yayi kamar bai gani ba yaci gaba da abinda yakeyi,aikin nasa ke bata sha'awa yake kuma burgeta,tanason masa tambaya amma kuma tana jin nauyi,don har yanzu bata gama sakewa dashi ba.
A lokacin yayi qoqari matuqa ya koya mata abubuwa da dama,har ya fara sakar mata,don majority ita ke dafa musu abincin rana,kuma ya ciyu saboda gyaran bashi da wani yawa.
Wannan karon ma bai samu zuwa bauchin ba sai bayan sati biyu,tanata hada kaya ta zaci da ita zaya je,sai yace a'ah,tayi zamanta,ta dinga masa kuka amma daga baya dole ta haqura,ya yiwa mai gidan magana matar gidan ta bata 'yar tayin kwana suke kwana tare,friday ya tafi ya dawo sunday da magariba,saita samu kanta cikin murna da farinciki ranar daya dawo din,wanda ita kanta batasan dalili ba,tunda dai ya tafi taji gaba daya bata da sukuni.
Zuwansa bauchi a yawancin lokuta bacin raine,yana zuwa ne kawai don ya sauke nauyin da Allah ya dora masa,ya kuma kwatanta adalci,amma baya ga haka baiga wani alfanu da yake samu ba,hafsat din ta yita mita da nunqufurcin bai taho da weedad ba,don ta tara ayyukanta jingim suna jiranta,gidan ya hada mugun datti da qura yadda ya kamata,to koda yaje ma kusan washegarin ranar a aikin kintsa gidan ya qarar dashi,daga qarshe sassan weedad din ya bude ya kwanta yayi baccin gajiya a falonta,ki sashen nata da babu dan adam baiyi wannan qazancewar ba,da yamma ya fice wajen hajiyarsa,wadda ta dinga jajjabin abinda yasa baizo da weedad din ba,a haka dai ya qare weekend din nasa a gantale babu wata kyakkyawar maraba.
Haka kawai ta samu kanta da son masa gwaninta,yana fita sallar magariba din a gurguje ta shiga kitchen,ta hada masa simple spaghetti jallop,da murmushi yake kallonta sanda ta dire masa ita,taliya ba cimarsa bace,amma kuma sai yaji ta burgeshi dari bisa dari,ko babu komai tafi hafsat din wadda a qalla nata shekarun sun ninka na weedad din,amma ko irin hakan batasan tayi masa ba,don haka yaji bazai iya watsa mata qasa a ido ba,yaja taliyar ya soma ci,taste dinta sai ya bashi mamaki qwarai,har ya kasa jurewa
"Yammata irin wannan abincin fa?,a ina kika koyo shi?" Sunan daya kirata dashi ya bata kunya,saita kifa kanta saman pillow tana dariya,batasan sanda suka fara irin wannan wasan dashi ba
"Kaine ka koyamin" kai ya girgiza yana sakin murmushi
"Wannan kaman ba aiki na ba" kuma ya fada dinne har zuciyarsa,saboda dandanon ya zarta yadda ya koya mata din.
Daya tashi komawa bauchi da ita ya tafi saboda hajiyarsa dake ta tambaya,hakan ya yiwa hafsat dadi,ta sake miqa dukka wasu ayyukan gida ga weedad din,bata samun zama ko hutu saita gama dukka wasu aiki na sassan hafsat din,hakanan hidimar yaran gaba daya ta dawo hannunta,wankansu wanki cire pampers,basu abinci da sauransu,tun tana jin gajiya da wahala har ya soma zame mata jiki ta saba.
Wani zuwa da sukayi,ranar asabar da azahar,tana kitchen din hafsat din tana gogeshi bayan ta gama wanke kwanukan da suka cika babban sink din kitchen din,cikin ranta cike fal da mamakin yadda take barin kitchen ya hada wannan uban datti da kayan wanke wanken kamar na gidan biki ko suna,mimi da nawwara na falon data gama gyarawa suna wasa,ta kadasu can don su barta ta gyara nan din a nutse,a dole ta sake qwarewa ta samu kuma experience sosai akan harkar kitchen da kula da yara.
Sau biyu anty ummee na sallama sai surutansu mimi,har sai data bude qofar falon ta shigo,tabi falon da kallo zuciyarta cike fal da mamakin yaushe hafsta ta koyo tsafta?,yaran da suka ankare da shigowarta suka watsar da kayan wasan suka taho da gudu suka rungumeta
"Ina babarku?"
"Tana dakinta,ta kwanta tace kada a tasheta"
"Babanku yana nan ne?" Kai ta girgiza
"Ya fita a mota"
"Muje cikin" ta fada tana kama hannunsu,har yanzu tana mamakin kintsuwar falon,duk da tazo kwana hudu da suka wuce amma ba haka ta samu falon ba.
Tana kwance male male saman gadonta tana sana'artata wato chart,harta bude baki data ji an bude qofar zata hau masifa,a zatonta weedad ko yaran ne saita maida maganar dake cikinta tana murmushi ta miqe ta zauna saman gadon ganin anty ummee ce
"Daga ina haka ba kira ba sanarwa?" Harara ta balla mata tana samun gefan gadon ta zauna
"Kedai baki da hali,don zanzo gidanki saina gaya miki?" Dariya tayi
"Allah ya baki haquri ba haka nake nufi ba" bedroom din nata anty ummen ta sake kalla
"Nace ba,wai yaushe kika fara tsafta ne?,don nidai banga haka a jikinki ba" tafadi tana kallon jikin hafsat din,wadda ko brassiere babu,sai wata t-shirt data mata yawa da zanin atamfa,kanta kuma tsifa ce rabi da rabi.
Fuska ta tsuke tana kallonta,tasan halin anty ummee idan ya motsa in ba cin mutunci tataba mata ba bata jin dadi
"Ni dadina dake wlh cin fuska,aidai jikin nawa babu qazanta ko?"
"Nima bance akwai ba" ta amsa mata tana boye dariya,sai hafsat din ta gyara zama tana cewa
"Ina daki"
"Wanne dakin?" Ta tambayeta daga can gabanta yana faduwa
"Dakina"
"Abbansu mimi yace baki da lafiya jiya,me ya sameki?" Gabanta ya yanke ya fadi data tuna cewa a dakinsa ta kwana jiya,kuma koda ra farka cikin jikinsa ta ganta,ta fahimci hakanne?,kota gane?
"Ciwon mara" ta amsa mata muryarta nadan rawa kadan,abinda ya sake sanya shakku a zuciyar hafsat din,tsoronta ya ninku
"Kodai wani abun kukayi ke dashi?" Tambayar daketa mata yawo tsakar ka ta subuce ta fito daga bakinta,da sauri ta hau girgiza kai kamar tana a gabanta ne,hawaye kuma suka jiqa mata fuska
"A'ah mommy....wallahi ba komai,ciwon mara ne kawai Allah ki yarda gaskiya na fada miki" boyayyar ajiyar zuciya ta saki,sanin weedad din bata qarya sai hankalinta yadan kwanta,amma saita fuske saboda ta samu nasarar sake dasa tsoron hakan a zuciyarta
"Ohon miki idan ma wani abun kika yarda yayi miki,mutuwa zakiyi.....ina ruwan wani,nima ina gaya miki ne don ina sonki banaso ki mutu"
"Allah mommy ba komai" sai kawai hafsan ta kashe wayar donta qara tsoratata.
Sosai hankalin weedad din ya tashi,tana shirin bin kiran taji ya turo qofar,ta daga kai tana kallonsa,har qasan ranta tana jin haushinsa,ya danji wani iri ganin tana kuka,yana fargabar ko wani abunne ya sameta,yasan yau bai leqota da kyau ba,duka yau ya kulle kansa ne a daki yana aikin tracing din wani criminal a sirrance,abinda yasa ya baro office kenan,bayaso kowa yasan abinda yakeyi
"Yaaya?.....jikinne?" Kai ta girgiza tana turo baki,ta kuma tura masa qeya taqi kallonsa
"To ma sha Allah"ya fada duk da ya fuskanci kamar cikin fushi take,shuru ya ratsa tsakani na sakanni kafin ya miqe
"Ki ajjiye komai ki kwanta" sai ya juya yana shirin barin dakin,binsa tayi da kallo,tana jin kamar ta bishi,amma da ta bishi ya tabata gwara ta zauna a dakinta.
A jikinsa yaji kamar tana kallonsa,don haka ya dakata ya waiwayo,suka hada ido saita dauke kai,kamar xaiyi magana sai kuma ya fasa,ya saka kai ya fita.
Tun bai kai tsakiyar falon ba yaji ihunta,ya juyo da sauri,sai gata sunyi kacibus a hanya har tana fadawa jikinsa,taja baya da sauri jikinta yana rawa
"Mm....mage"
"A ina?"
"Bakin window" ta fada tana duban qofar dakin
"Muje na gani" ya fadi yana sakata a gaba,kafada ta maqale tana sakin kuka,kome zaiyi mata bata jin zata yarda ta bishi,haka tayi tsaye a wajen ya shiga dakin,bai jimaba ya fito
"Bata shigo ba,infact ta wuce ma,zaki iya komawa" waiwaya tayi inda yake,taga da gaske tafiya yake zuwa dakinsa,ta daga qafarta da sauri tabi bayansa.
Batasan ta cimmasa ba sai da suka tsaya suna kallon kallo shi da ita,yana riqe da handle din qofar yana dubanta,itama shi take kallo saidai batace komai ba sai aukin hawayen da take faman zubarwa
"Don Allah...zan karka tafi ka barni"
"Bacci nakeji" ya amsa mata a taqaice,saita sake fashe masa da kuka,hannu ya sanya ya dafe goshinsa
"Oh my goodness" ya furta a hankali,saiya maida manyan idanunsa kanta
"Me kike so?" Shuru tayi kamar ba zata amsa ba,sai kuma tayi qasa da kanta
"Zan kwana a nan" ta fada a hankali gabanta yana faduwa,zuciyarta na gaya mata girman laifinta,ta yaya zata hada dakin kwana dashi?.
Qaramin murmushi ya saki
"Silly girl" ya fada qasa qasa,ga dan banzan tsoro ga shagwaba da sakarci harda na siyarwa,sai ya matsa gefe daya
"Bismillah" ya furta a hankali,ta rabeshi sosai ta shige dakin,ya rufe qofar ya sanya key sannan yabi bayanta.
Ta jima a zaune har ya gama komai na shirin kwanciya bacci tana binsa da idanu,pillow ya dauka ya jefar a qasa sannan yabi pillow din ya kwanta idanuwansa a rufe yana karanto addu'an bacci,ya gama ya shafe jikinsa,ba tare daya bude idanun ko ya dubeta ba yace
"Ki kwanta kiyi kuma addu'a" a takure take sosai saman gadon,duk kuwa da cewa ita daya ce,duk juyin da zatayi idanunta a kansa,har sai data ji saukar numfashinsa a hankali alamun bacci yayi awon gaba dashi,sannu a hankali itama jikinta ya saki,wani bacci me dadi wanda babu fargaba a ciki ya sureta.
KI KULANI miss xoxo
DAUDAR GORA Billynabdul
RUMBUN K'AYA hafsat rano
IDON NERA Mamuhghee
A RUBUCE TAKE huguma
_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_
_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_
0022419171
Maryam sani
Access bank
Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070
*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261
*Al'ummar nijer🇳🇪🇳🇪🇳🇪 zaku tuntubi wannan number*
+227 96 09 67 63
*Thanks for choosing us*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:huguma*
Page 57
To tun daga wannan rana kwananta ya dawo dakinsa,saidai tana kammala sallar asuba take komawa dakinta ta shirya shirin makaranta,wani lokaci shike kaita,wani lokacin kuma samuel ko daya daga cikin yaran dake qarqashinsa.
Aikin da yakeyi yasa a yanzun zamansa a gida yafi yawa,wannan ya fara haifar da shaquwa a tsakaninsu,duk da baya barin kowa ya rabi inda yake wannan aikin amma yawancin lokuta suna tare,badai hira sukeyi da ita ba,amma zata dauki littafinta ta zauna a wajen,ko ba komai tana jin motsinsa bata da kewa,lokaci bayan lokaci tana barin karatunta tadan zuba idanu tana kallonsa,idan sun hada ido kuma sai ta basar,murmushi kawai yakeyi ko yayi kamar bai gani ba yaci gaba da abinda yakeyi,aikin nasa ke bata sha'awa yake kuma burgeta,tanason masa tambaya amma kuma tana jin nauyi,don har yanzu bata gama sakewa dashi ba.
A lokacin yayi qoqari matuqa ya koya mata abubuwa da dama,har ya fara sakar mata,don majority ita ke dafa musu abincin rana,kuma ya ciyu saboda gyaran bashi da wani yawa.
Wannan karon ma bai samu zuwa bauchin ba sai bayan sati biyu,tanata hada kaya ta zaci da ita zaya je,sai yace a'ah,tayi zamanta,ta dinga masa kuka amma daga baya dole ta haqura,ya yiwa mai gidan magana matar gidan ta bata 'yar tayin kwana suke kwana tare,friday ya tafi ya dawo sunday da magariba,saita samu kanta cikin murna da farinciki ranar daya dawo din,wanda ita kanta batasan dalili ba,tunda dai ya tafi taji gaba daya bata da sukuni.
Zuwansa bauchi a yawancin lokuta bacin raine,yana zuwa ne kawai don ya sauke nauyin da Allah ya dora masa,ya kuma kwatanta adalci,amma baya ga haka baiga wani alfanu da yake samu ba,hafsat din ta yita mita da nunqufurcin bai taho da weedad ba,don ta tara ayyukanta jingim suna jiranta,gidan ya hada mugun datti da qura yadda ya kamata,to koda yaje ma kusan washegarin ranar a aikin kintsa gidan ya qarar dashi,daga qarshe sassan weedad din ya bude ya kwanta yayi baccin gajiya a falonta,ki sashen nata da babu dan adam baiyi wannan qazancewar ba,da yamma ya fice wajen hajiyarsa,wadda ta dinga jajjabin abinda yasa baizo da weedad din ba,a haka dai ya qare weekend din nasa a gantale babu wata kyakkyawar maraba.
Haka kawai ta samu kanta da son masa gwaninta,yana fita sallar magariba din a gurguje ta shiga kitchen,ta hada masa simple spaghetti jallop,da murmushi yake kallonta sanda ta dire masa ita,taliya ba cimarsa bace,amma kuma sai yaji ta burgeshi dari bisa dari,ko babu komai tafi hafsat din wadda a qalla nata shekarun sun ninka na weedad din,amma ko irin hakan batasan tayi masa ba,don haka yaji bazai iya watsa mata qasa a ido ba,yaja taliyar ya soma ci,taste dinta sai ya bashi mamaki qwarai,har ya kasa jurewa
"Yammata irin wannan abincin fa?,a ina kika koyo shi?" Sunan daya kirata dashi ya bata kunya,saita kifa kanta saman pillow tana dariya,batasan sanda suka fara irin wannan wasan dashi ba
"Kaine ka koyamin" kai ya girgiza yana sakin murmushi
"Wannan kaman ba aiki na ba" kuma ya fada dinne har zuciyarsa,saboda dandanon ya zarta yadda ya koya mata din.
Daya tashi komawa bauchi da ita ya tafi saboda hajiyarsa dake ta tambaya,hakan ya yiwa hafsat dadi,ta sake miqa dukka wasu ayyukan gida ga weedad din,bata samun zama ko hutu saita gama dukka wasu aiki na sassan hafsat din,hakanan hidimar yaran gaba daya ta dawo hannunta,wankansu wanki cire pampers,basu abinci da sauransu,tun tana jin gajiya da wahala har ya soma zame mata jiki ta saba.
Wani zuwa da sukayi,ranar asabar da azahar,tana kitchen din hafsat din tana gogeshi bayan ta gama wanke kwanukan da suka cika babban sink din kitchen din,cikin ranta cike fal da mamakin yadda take barin kitchen ya hada wannan uban datti da kayan wanke wanken kamar na gidan biki ko suna,mimi da nawwara na falon data gama gyarawa suna wasa,ta kadasu can don su barta ta gyara nan din a nutse,a dole ta sake qwarewa ta samu kuma experience sosai akan harkar kitchen da kula da yara.
Sau biyu anty ummee na sallama sai surutansu mimi,har sai data bude qofar falon ta shigo,tabi falon da kallo zuciyarta cike fal da mamakin yaushe hafsta ta koyo tsafta?,yaran da suka ankare da shigowarta suka watsar da kayan wasan suka taho da gudu suka rungumeta
"Ina babarku?"
"Tana dakinta,ta kwanta tace kada a tasheta"
"Babanku yana nan ne?" Kai ta girgiza
"Ya fita a mota"
"Muje cikin" ta fada tana kama hannunsu,har yanzu tana mamakin kintsuwar falon,duk da tazo kwana hudu da suka wuce amma ba haka ta samu falon ba.
Tana kwance male male saman gadonta tana sana'artata wato chart,harta bude baki data ji an bude qofar zata hau masifa,a zatonta weedad ko yaran ne saita maida maganar dake cikinta tana murmushi ta miqe ta zauna saman gadon ganin anty ummee ce
"Daga ina haka ba kira ba sanarwa?" Harara ta balla mata tana samun gefan gadon ta zauna
"Kedai baki da hali,don zanzo gidanki saina gaya miki?" Dariya tayi
"Allah ya baki haquri ba haka nake nufi ba" bedroom din nata anty ummen ta sake kalla
"Nace ba,wai yaushe kika fara tsafta ne?,don nidai banga haka a jikinki ba" tafadi tana kallon jikin hafsat din,wadda ko brassiere babu,sai wata t-shirt data mata yawa da zanin atamfa,kanta kuma tsifa ce rabi da rabi.
Fuska ta tsuke tana kallonta,tasan halin anty ummee idan ya motsa in ba cin mutunci tataba mata ba bata jin dadi
"Ni dadina dake wlh cin fuska,aidai jikin nawa babu qazanta ko?"
"Nima bance akwai ba" ta amsa mata tana boye dariya,sai hafsat din ta gyara zama tana cewa