Sashe 6
A Jini Take Izzata Part 1 Compleete Hausa Novel · about 7 min read
"Ammi don Allah ki rakani in rarrasheta." Ta faɗa da iya gaskiyarta, dan kuwa tafi kowa sanin halin Didin musamman idan tazo tafiya wani wajen, ta dinga nunƙufurci kenan, kuma ko me za a mata ba za ta bi Lulun ba. Duk da itama Ammin ba son zuwan Lulun take gidan Mamin ba, amma za ta so su je tare da Didi, domin kuwa duk da kasancewarta mahaifiyarsu ita me iya buɗe baki ne ta faɗi cewar Didin tafi Lulu hankali.
"Ni ba inda zan je." Ammi ta faɗa.
"Don Allah, Don Allah, Don Allah." Lulu ta faɗa kamar za tayi kuka. Murmushi Ammi tayi tana miƙewa ta saka hannunta kan kunnen Lulu ta ja lokaci ɗaya tana faɗin
"Ke dai koh!" Se ta saka hannunta ta riƙe kunnen tana ɗan sakin ƙara a hankali gami da murmushi. A kwance take akan gadon na su idanunta a rufe kamar me bacci, se dai ba baccin take ba, amma dai jira take ya ɗauketa. A nutse suka ƙarasa cikin ɗakin. Ammi ta nemi waje ta zauna yayin da Lulu ta zauna a kan gadon, kusa da Didi da ke kwance. Motsin da ta ji a kusa da ita ne ya sanyata saurin buɗe ido, se ta ga Lulu a zaune, ta galla mata harara hadda murguɗa baki. Langaɓar da kai tayi gefe tana ƙiƙƙifta ido, duk Ammi na lura da su hakan ne ya sanyata murmushi tana girgiza kai.
"Didi tashi.." Ammi ta faɗa, itama langaɓar da kan tayi kafin tace
"Ammi bacci fa zan yi."
"Tashi dai." Ammi ta sake faɗa tana riƙota kamar zata ɗagata. Se a lokacin ta miƙe ɗin da taimakon Ammi.
"Ki shirya ku tafi tare zuwa gidan Mamin taku." Ammi ta faɗa bayan ta gama gyara zamanta akan gadon. Girgiza kai tayi da sauri sannan tace
"A'ah ni kam Ammi."
"Pls my Didi" Lulu da ke gefe ta faɗa a narke.
"Na ƙi ɗin" ta faɗa tana jefa mata harara. Dama Ammin ta san ba zuwa za ta yi ba, idan ma aka takura se dai ta dami kanta dan haka se tace
"Toh fushin na meye?" Se da ta ɗan yi shiru sannan tace
"Toh Ammi ba komai fa." Ta ƙare tana cuno baki.
"Kin tabbatar?" Ammi ta faɗa. Kafin ta kai ga cewa komai Lulu tace
"Allah kuwa Ammi ba wani nan, fushi take da ni fa."
"Ni ba wani fushi da nake fa."
"Toh in ga alamar hakan." Ammi ta faɗa tana murmushi. Ba tare da Lulu ta ankara ba se ji tayi Didin ta rungumeta. Cikin farin ciki itama ta rungumeta tana murmushi. Ammi ma da ke gefensu murmushin tayi a ranta tana sake addu'ar Allah ya ƙara haɗe mata kan 'ya'yanta.
... Washegari se bayan sun dawo daga makaranta sannan Abba ya ɗauki Lulu da ta gama shiryawa tsaff da kayanta zuwa gidan Mamin. Tun a ƙaton compound ɗin gidan suka haɗu da Mami sanda ya ida parking ɗin motarsa. Mamin na sanye cikin wata doguwar riga ɗinkin hijab bubu da mayafi fuskarta ɗauke da glass, hannunta kuma ɗauke da wata ƙaramar jaka. Cikin farin cikin ganin nasu tace
"Oyoyo! Sannunku da zuwa." Ta faɗa da murmushi kan fuskarta. Fitowar da Lulu tayi ne sanyata buɗe mata hannu tana faɗin
"Welcome my dear." Babu ɓata lokacin Lulu ta ƙarasa jikin Mamin suka rungume junansu kowaccensu ɗauke da murmushi a kan fuskarta.
"Toh ko dai na koma ne?" Abba ya faɗa yana murmushi. Itama murmushin Mami tayi tana sakin Lulu kafin tace
"Haba dai Yaya. Barkanka da zuwa, ka zo mu ƙarasa ciki mana." Girgiza kai Abba yayi yana ƙarasowa inda suke lokaci ɗaya yace
"A'ah akwai inda zan je, naga kuma kema fita za ki yi. Saboda haka mu gaisa anan."
"Kai Yaya haka za a yi?"
"Hakan kuwa za a yi" Abba ya faɗa yana murmushi. Gaisawar kuwa suka shiga yi, saboda Abban sauri yake ya sanya babu daɗewa ya wuce. Ita kuma Ammin ta saka hannu ta ɗauki jakar Lulu sannan suka soma takawa zuwa cikin gidan.
"Mami da kin bari na ɗauka." Lulu ta faɗa. Hararar wasa Mamin ta jefa mata kafin tace
"Ke ban son iyayi." Dariya suka yi kusan a tare daidai lokacin da suka shiga cikin parlourn. Har ɗakin Jadwa Mamin ta kai jakar Lulu. Jadwan na kwance kan gadon tana danna waya, kamar ko da yaushe kunnenta ɗauke da ear piece. Sam bata ji shigowarsu ba, se da Mami ta saka hannu ta karɓe wayar sannan ta juyo da sauri dan ta san dai sun riga sun yi sallama da Mamin kafin ta fita. Tana juyowa se taga Lulu a tsaye tana murmushi, da sauri ta diro daga kan gadon lokaci ɗaya tana faɗin
"Oyoyo.." ta faɗa tana rungumeta. Murmushi Mami tayi tace tana kallansu su duka bayan sun saki junansu, se kuma ta maida dubanta kan Lulu tace
"Lulu za ki je makaranta ne yau ɗin?" Girgiza kai tayi tana tura baki, tace a hankali
"A'ah Mami, daga zuwana kuma?" Dafa kafaɗarta Mami tayi tana faɗin
"Kwantar da hankalinki my dear, ba wanda ze miki dole. Nemi waje ki kwanta ki huta, gobe se ki je." Cikin farin ciki tace
"Yawwah Mamina." Itama murmushin tayi kana tace
"Jadwa ki kula da ita kafin na dawo. Duk abin da take so a sama mata shi, ina dawowa kuma zan ɗora daga inda kika tsaya." Sunkuya wa Jadwa tayi irin alamar girmamawan nan sannan tace
"An gama Mami." Tayi maganar tana dariya. Dukansu dariyar suka yi. Mami ta sake yi musu sallama ta fice daga gidan.
.. A ranar da Didi taje makaranta tana ta jiran zuwan Lulu amma shiru bata zo ba, bata damu ba tunda ta ga yau ta je gidan Mamin, dan kuwa ze yi wuya idan ba Mamin ce za tace yau ɗin su yi hira ba tunda dai yau ta zo. Aikuwa ta sha tambaya a wajen Abida, har se da ta gaji. Dan haka kawai ta ji yarinyar ba ta birgeta ba, rawar kanta ya fiya yawa, se wani rawar kai take akan Lulun da sau 1 ta taɓa ganinta. Idan ma da ta san halin Lulun da bata din ga zaƙewa haka ba, dan ba abu ne me wahala a wajen Lulun ta dizgata ba, dan wani lokacin halinta se ita.
... "Kin gama shiryawa?" Mami ta faɗa tana kallan Lulu da ta fito cikin Uniform ɗin da kamar kodayaushe ana ƙara mata kyau ne idan ta sakasu.
"Ehh Mami."
"Toh mu je!" Mami ta faɗa tana yin gaba yayin da Lulu ta bi bayanta. Compound ɗin gidan suka nufa kai tsaye suka hau motar da zata kaisu inda zasu je. Har bakin makarantar driver ya kaita ta sauka sannan ya ja Mami da ze kai unguwa. Kai tsaye ita kuma Lulu ajinsu ta wuce cike da zumuɗin ganin twinnynta. Aikuwa tana shiga ta sameta zaune kamar kodayaushe a inda suka saba zama. Da sauri ta rungumeta tana faɗin
"Didina" Cike da farin ciki itama Didin tace
"Luluna" se ta koma ta zauna tana ɗage niƙab ɗin fuskar Didin lokaci ɗaya tana faɗin
"Bari na ga ko kin rame saboda bana nan." Hannunta ta bige kafin tace
"See u. Kwana ɗayan koh?" Kafin Lulu tace komai se ga sallamar wani Malami nan ya shigo cikin ajin, hakan ne ya sanyasu yin shiru bayan amsa sallamarsa.
"Masoyiya fa?" Lulu ta tambaya ƙasa_ƙasa.
"Ba ta zo ba, itama mutuniyarki bata zo ba" Didin ta bata amsa itama ƙasa_ƙasa. Cikin rashin fahimta tace
"Wace mutuniyata?" A hankali Didi tace
"Ki yi shiru zan faɗa miki" Daga haka babu wadda ta sake magana. Se dab da za a tashi sannan aka aiko cewar duk wanda be bayar da hadda ba jiya ya je ya bada, wanda ma yayi fashi shi ma ya je. Kallan juna Lulu da Didi suka yi, cikin sarewa ita dai Lulu tayi shiru tana jiran ganin wasu sun miƙe, se dai shiru bata ga kowa ya miƙe ba. A'ah abin dai kamar haɗa baki se ya kasance ita kaɗai ce wadda bata bayar da haddar ba, haushi kamar ya kasheta, takaici kamar ta yi kuka. Se kawai ta gyara zama a inda take zaune fuskarta a haɗe
"Lulu ki tashi ki je, meye amfanin abin da kike yi? Haddar ce baki iya ba ko me?" Didi ta faɗa tana kallanta. Se da ta sauke numfashi sannan tace
"A'ah fa Didi kawai dai.."
"Ni ba inda zan je." Ammi ta faɗa.
"Don Allah, Don Allah, Don Allah." Lulu ta faɗa kamar za tayi kuka. Murmushi Ammi tayi tana miƙewa ta saka hannunta kan kunnen Lulu ta ja lokaci ɗaya tana faɗin
"Ke dai koh!" Se ta saka hannunta ta riƙe kunnen tana ɗan sakin ƙara a hankali gami da murmushi. A kwance take akan gadon na su idanunta a rufe kamar me bacci, se dai ba baccin take ba, amma dai jira take ya ɗauketa. A nutse suka ƙarasa cikin ɗakin. Ammi ta nemi waje ta zauna yayin da Lulu ta zauna a kan gadon, kusa da Didi da ke kwance. Motsin da ta ji a kusa da ita ne ya sanyata saurin buɗe ido, se ta ga Lulu a zaune, ta galla mata harara hadda murguɗa baki. Langaɓar da kai tayi gefe tana ƙiƙƙifta ido, duk Ammi na lura da su hakan ne ya sanyata murmushi tana girgiza kai.
"Didi tashi.." Ammi ta faɗa, itama langaɓar da kan tayi kafin tace
"Ammi bacci fa zan yi."
"Tashi dai." Ammi ta sake faɗa tana riƙota kamar zata ɗagata. Se a lokacin ta miƙe ɗin da taimakon Ammi.
"Ki shirya ku tafi tare zuwa gidan Mamin taku." Ammi ta faɗa bayan ta gama gyara zamanta akan gadon. Girgiza kai tayi da sauri sannan tace
"A'ah ni kam Ammi."
"Pls my Didi" Lulu da ke gefe ta faɗa a narke.
"Na ƙi ɗin" ta faɗa tana jefa mata harara. Dama Ammin ta san ba zuwa za ta yi ba, idan ma aka takura se dai ta dami kanta dan haka se tace
"Toh fushin na meye?" Se da ta ɗan yi shiru sannan tace
"Toh Ammi ba komai fa." Ta ƙare tana cuno baki.
"Kin tabbatar?" Ammi ta faɗa. Kafin ta kai ga cewa komai Lulu tace
"Allah kuwa Ammi ba wani nan, fushi take da ni fa."
"Ni ba wani fushi da nake fa."
"Toh in ga alamar hakan." Ammi ta faɗa tana murmushi. Ba tare da Lulu ta ankara ba se ji tayi Didin ta rungumeta. Cikin farin ciki itama ta rungumeta tana murmushi. Ammi ma da ke gefensu murmushin tayi a ranta tana sake addu'ar Allah ya ƙara haɗe mata kan 'ya'yanta.
... Washegari se bayan sun dawo daga makaranta sannan Abba ya ɗauki Lulu da ta gama shiryawa tsaff da kayanta zuwa gidan Mamin. Tun a ƙaton compound ɗin gidan suka haɗu da Mami sanda ya ida parking ɗin motarsa. Mamin na sanye cikin wata doguwar riga ɗinkin hijab bubu da mayafi fuskarta ɗauke da glass, hannunta kuma ɗauke da wata ƙaramar jaka. Cikin farin cikin ganin nasu tace
"Oyoyo! Sannunku da zuwa." Ta faɗa da murmushi kan fuskarta. Fitowar da Lulu tayi ne sanyata buɗe mata hannu tana faɗin
"Welcome my dear." Babu ɓata lokacin Lulu ta ƙarasa jikin Mamin suka rungume junansu kowaccensu ɗauke da murmushi a kan fuskarta.
"Toh ko dai na koma ne?" Abba ya faɗa yana murmushi. Itama murmushin Mami tayi tana sakin Lulu kafin tace
"Haba dai Yaya. Barkanka da zuwa, ka zo mu ƙarasa ciki mana." Girgiza kai Abba yayi yana ƙarasowa inda suke lokaci ɗaya yace
"A'ah akwai inda zan je, naga kuma kema fita za ki yi. Saboda haka mu gaisa anan."
"Kai Yaya haka za a yi?"
"Hakan kuwa za a yi" Abba ya faɗa yana murmushi. Gaisawar kuwa suka shiga yi, saboda Abban sauri yake ya sanya babu daɗewa ya wuce. Ita kuma Ammin ta saka hannu ta ɗauki jakar Lulu sannan suka soma takawa zuwa cikin gidan.
"Mami da kin bari na ɗauka." Lulu ta faɗa. Hararar wasa Mamin ta jefa mata kafin tace
"Ke ban son iyayi." Dariya suka yi kusan a tare daidai lokacin da suka shiga cikin parlourn. Har ɗakin Jadwa Mamin ta kai jakar Lulu. Jadwan na kwance kan gadon tana danna waya, kamar ko da yaushe kunnenta ɗauke da ear piece. Sam bata ji shigowarsu ba, se da Mami ta saka hannu ta karɓe wayar sannan ta juyo da sauri dan ta san dai sun riga sun yi sallama da Mamin kafin ta fita. Tana juyowa se taga Lulu a tsaye tana murmushi, da sauri ta diro daga kan gadon lokaci ɗaya tana faɗin
"Oyoyo.." ta faɗa tana rungumeta. Murmushi Mami tayi tace tana kallansu su duka bayan sun saki junansu, se kuma ta maida dubanta kan Lulu tace
"Lulu za ki je makaranta ne yau ɗin?" Girgiza kai tayi tana tura baki, tace a hankali
"A'ah Mami, daga zuwana kuma?" Dafa kafaɗarta Mami tayi tana faɗin
"Kwantar da hankalinki my dear, ba wanda ze miki dole. Nemi waje ki kwanta ki huta, gobe se ki je." Cikin farin ciki tace
"Yawwah Mamina." Itama murmushin tayi kana tace
"Jadwa ki kula da ita kafin na dawo. Duk abin da take so a sama mata shi, ina dawowa kuma zan ɗora daga inda kika tsaya." Sunkuya wa Jadwa tayi irin alamar girmamawan nan sannan tace
"An gama Mami." Tayi maganar tana dariya. Dukansu dariyar suka yi. Mami ta sake yi musu sallama ta fice daga gidan.
.. A ranar da Didi taje makaranta tana ta jiran zuwan Lulu amma shiru bata zo ba, bata damu ba tunda ta ga yau ta je gidan Mamin, dan kuwa ze yi wuya idan ba Mamin ce za tace yau ɗin su yi hira ba tunda dai yau ta zo. Aikuwa ta sha tambaya a wajen Abida, har se da ta gaji. Dan haka kawai ta ji yarinyar ba ta birgeta ba, rawar kanta ya fiya yawa, se wani rawar kai take akan Lulun da sau 1 ta taɓa ganinta. Idan ma da ta san halin Lulun da bata din ga zaƙewa haka ba, dan ba abu ne me wahala a wajen Lulun ta dizgata ba, dan wani lokacin halinta se ita.
... "Kin gama shiryawa?" Mami ta faɗa tana kallan Lulu da ta fito cikin Uniform ɗin da kamar kodayaushe ana ƙara mata kyau ne idan ta sakasu.
"Ehh Mami."
"Toh mu je!" Mami ta faɗa tana yin gaba yayin da Lulu ta bi bayanta. Compound ɗin gidan suka nufa kai tsaye suka hau motar da zata kaisu inda zasu je. Har bakin makarantar driver ya kaita ta sauka sannan ya ja Mami da ze kai unguwa. Kai tsaye ita kuma Lulu ajinsu ta wuce cike da zumuɗin ganin twinnynta. Aikuwa tana shiga ta sameta zaune kamar kodayaushe a inda suka saba zama. Da sauri ta rungumeta tana faɗin
"Didina" Cike da farin ciki itama Didin tace
"Luluna" se ta koma ta zauna tana ɗage niƙab ɗin fuskar Didin lokaci ɗaya tana faɗin
"Bari na ga ko kin rame saboda bana nan." Hannunta ta bige kafin tace
"See u. Kwana ɗayan koh?" Kafin Lulu tace komai se ga sallamar wani Malami nan ya shigo cikin ajin, hakan ne ya sanyasu yin shiru bayan amsa sallamarsa.
"Masoyiya fa?" Lulu ta tambaya ƙasa_ƙasa.
"Ba ta zo ba, itama mutuniyarki bata zo ba" Didin ta bata amsa itama ƙasa_ƙasa. Cikin rashin fahimta tace
"Wace mutuniyata?" A hankali Didi tace
"Ki yi shiru zan faɗa miki" Daga haka babu wadda ta sake magana. Se dab da za a tashi sannan aka aiko cewar duk wanda be bayar da hadda ba jiya ya je ya bada, wanda ma yayi fashi shi ma ya je. Kallan juna Lulu da Didi suka yi, cikin sarewa ita dai Lulu tayi shiru tana jiran ganin wasu sun miƙe, se dai shiru bata ga kowa ya miƙe ba. A'ah abin dai kamar haɗa baki se ya kasance ita kaɗai ce wadda bata bayar da haddar ba, haushi kamar ya kasheta, takaici kamar ta yi kuka. Se kawai ta gyara zama a inda take zaune fuskarta a haɗe
"Lulu ki tashi ki je, meye amfanin abin da kike yi? Haddar ce baki iya ba ko me?" Didi ta faɗa tana kallanta. Se da ta sauke numfashi sannan tace
"A'ah fa Didi kawai dai.."