Sashe 37
A Jini Take Izzata Part 1 Compleete Hausa Novel · about 6 min read
"Wai ina yarinyar nan ta shiga ne?" Ta faɗa sanda ta buɗe ƙofar toilet. Ganin nan ma babu ita ne ya sanyata sake fitowa parlour inda Lulu ke zaune. Tana shirin yin magana Abba ya yi sallama cikin ɗakin shi da Didi. Ajiyar zuciya Ammi ta sauke tana faɗin
"Yallaɓai na shiga tashin hankali fa. Na kira wayarka ba ka ɗauka ba, na yi duban duniya ban ga yarinyar nan ba. Ashe fita kuka yi ." Ta ƙare tana kallan Didi. A hankali Didi ta nemi kusa da inda Ammi ta tashi ta zauna a sanyaye. Abba ma neman waje ya yi ya zauna daidai lokacin da Ammi ta sake faɗin
"Lafiya kuwa?"
"Nemi waje ki zauna.." Abba ya faɗa yana nuna mata kusa da shi. Babu musu ta zauna, se dai haka kawai ta ji jikinta ya ɗan yi sanyi. Kallan Lulu da ke kwance kan kujera ya yi fuskarsa a haɗe yace
"Afaaf tashi ki zauna.." A hankali ta ɗan fara ƙoƙarin tashi irin da gasken bata da lafiya. Abba be ce mata komai ba har ta sauko ta nemi kusa da inda Didi ta zauna a ƙasa tun zaman su Abba a kan kujera. Bayan shuɗewar wasu sakanni ba tare da kowa yace komai ba Abba ya soma faɗin
"Ashe suspension aka baki?" Ya yi maganar ba tare da ya ambaci suna ba. Da sauri Lulu ta ɗaga kai ta kalli Abba ƙirjinta na bugawa. Ganin shi ma itan yake kalla ya sanyata yin ƙasa da kai sannan ta soma haɗo maganganu tana inda inda.
"Suspension kuma?" Ammi ta faɗa cike da mamaki. Jinjina kai Abba ya yi kafin yace
"Ƙwarai kuwa,. Ta sake fusata malamin da rashin ɗa'a irin nata, shi ya sa ya bata hutun kwanaki, se dai be sani ba a shashanci irin na yarinyar nan daɗin hakan za ta ji.. Se dai wannan ɗin ba abin damuwa bane, dan kuwa ba ma bada kwanaki da aka yi ba, dama ko ba a yi hakan ba, daga yau kowaccensu ta gama zuwa makaranta se da izinin mijinta.." Ammi, Lulu, Didi gaba ɗaya kallan Abba suka yi jin wani saɓo da ya yi. Cike da mamakin furucinsa duka suke kallansa, se suke ganin kamar Abban be san abin da ya faɗa ba. Ganin kallan da suke binsa da shi ne ya sanya shi kallan Ammi da mamakinta yafi na kowa bayyana yace
"Ƙwarai kuwa a yau ɗin nan na aurar da Afaaf da kuma Afrah.." Cikin matuƙar tashin hankali Ammi tace ƙirjinta na bugawa
"Aure kuma? Aure na gaske kake nufi ko kuwa wanne Abbansu?" Ta tambaya fuskarta ɗauke da zallar mamaki da tashin hankali. Ajiyar zuciya Abba ya sauke dan ya ga alamar Ammin ta gama rikicewa, yace
"Aure dai kamar yadda muka yi ni dake.." Numfashi Ammi ta sauke da ƙarfi tana ɗauke kai a kan laɓɓanta ta furta
"Ya ilahy!" Se kuma ta kalli Abban a nutse tace
"Wa ka aurawa su Abba?" Ammi ta faɗa bugun zuciyarta na ƙaruwa. Kallan Twins Abba ya yi waɗanda kowaccensu su take kalla, jin abin suke kamar a mafarki, bama su yadda da gaske Abban yake ba. Kawai sun ɗauki hakan a matsayin wasa ne yau Abban yake musu. Wasan da idan dai har ba a yi saurin ƙarƙare shi ba zuciyoyi biyu na dab da bugawa.
"Na aurar dasu ne ga waɗanda suka dace, don kuwa ina fatan ko kuma nace idan Allah ya yadda ta silar auren nan wasu ɓangaren za su taimaki wasu ɓangaren, har su yi amfani da damar da Allah ya ba su wajen gyara abokanan zamansu, wanda kai tsaye zan iya kiran hakan da jihadi. Ki bari zan miki bayanin komai, kada ki tayar da hankalinki, dan kin riga da kin san uba ba ze taɓa zaɓarwa 'ya'yansa abin da ze cutar dasu ba. Dan haka ki kwantar da hankalinki.." Ita gaba ɗaya ma wasu maganganun na Abban ba fahimtar su take ba, dan haka ta ɗan girgiza kanta sannan tace
"Zan kwantar da hankalina Abbansu, amma bayan ka faɗa min wanda ka aura musu. Sannan kuma ka tabbatar min ni da 'ya'yana da gaske abin da kake faɗa gaskiya ne?"
"Ki dena tantama da wannan maganar, ba wasa bace. Da gaske na aurar da yaran nan a yau ɗin nan.." ya ƙare maganar yana kallan Twins da ke zaune kamar wasu shashashu ko waɗanda ba sa hayyacinsu. Gyara zama Abba ya yi sannan ya kalli Lulu ya ɗan yi murmushi kafin ya soma faɗin
"Shi dai wannan malamin naki da kika ɗauke shi ba a matsayin malaminki ba. Ki ke masa kallan wanda kike taimakawa kina zuwa makaranta bayan shi yake koyar dake. Ki ke masa kallan wulaƙantacce dan yana Malamin Addini. Ki ka yi watsi da tarbiyyar da muka baki ki ke rashin daraja gare shi. A yau ɗin kuma cikin ikon Allah na ba shi auranki... Ma'ana dai na aura masa ke, yanzu haka kin koma ƙarƙashinsa ne, dan kuwa ya zama mijinki.." Ɗan runtse idanunta Lulu ta yi sanda gaba ɗaya kanta ya buga. A hankali kuma ta ji wani jiri jiri na kwasarta duk da a zaune take, se ta ɗan yi gefe sannan ta kai hannunta ta riƙo kanta, daidai lokacin da take sake tuno maganganun da Abban ya faɗa, dan sake tabbatar da abin da kunnuwanta suka ji.
"Malam Affan!" Abba ya bawa Ammi da ta masa magana amsa. Wata ƙara Lulu ta saki sanda ta gama fahimtar inda zancen Abban ya dosa, gaba ɗaya idanunta suka makance a lokacin, kunnuwanta suka yi wani dumm, gangar jikinta ta kasa riƙeta, ƙirjinta ya cigaba da bugawa da gudun da ya mugun wuce na ƙa'ida. Saboda yanda ta ji kanta ya ɗaure tamau kamar wadda aka ɗorawa wani ƙaton abu akai, ya sanyata riƙo kan lokaci ɗaya tana faɗin
"Na shiga uku..." Tun kafin ta ida faɗar hakan ta yi wani baya kamar wadda aka ja, se kawai ta zube a wajen sumammiya. Abba, Ammi har ma da Didi duka kanta suka yi. Ammi na kiran sunanta cikin tsananin tashin hankali. Da ƙyar Didi ta iya ƙarasawa inda Lulun take, se dai ta kasa aikata komai, dan gaba ɗaya jikinta wani irin rawa yake kamar mazari. Haka zalika idanunta sun cika fall da ƙwalla, ita kaɗai kuma ta san yanda take jinta a cikin tashin hankali, har taso ta ɗan dena fahimtar wasu abubuwan saboda yanda ƙwaƙwalwarta ta toshe a lokacin. Tunda Abba ya ambaci sunan Gwani Affan a matsayin wanda ya aurawa Lulu, jikinta ya ɗauki zafi, ba ta taɓa zata ba, ba ta taɓa tsammani ba. Ga kuma er uwa rabin jiki a kwance kamar matacciya. Wannan tashin hankalin shi ne ya sanya ƙwalla zubowa daga cikin idanunta, se kuma wanda yafi kowanne, wato jiran jin sunan wanda Abba ze faɗa a matsayin wanda ya aura mata itama...
ALHAMDULILLAH! Anan na kawo ƙarshen A JINI TAKE Chapter one. Me son cigaba da karanta littafin A JINI TAKE Chapter two, ze tura ₦300 ne ta 8124818273, Zahra'u Yusuf Ishaq, Opay. Shedar biya ta 08124818273.
Don neman ƙarin bayani za a iya tuntuɓata ta 08124818273.
"Yallaɓai na shiga tashin hankali fa. Na kira wayarka ba ka ɗauka ba, na yi duban duniya ban ga yarinyar nan ba. Ashe fita kuka yi ." Ta ƙare tana kallan Didi. A hankali Didi ta nemi kusa da inda Ammi ta tashi ta zauna a sanyaye. Abba ma neman waje ya yi ya zauna daidai lokacin da Ammi ta sake faɗin
"Lafiya kuwa?"
"Nemi waje ki zauna.." Abba ya faɗa yana nuna mata kusa da shi. Babu musu ta zauna, se dai haka kawai ta ji jikinta ya ɗan yi sanyi. Kallan Lulu da ke kwance kan kujera ya yi fuskarsa a haɗe yace
"Afaaf tashi ki zauna.." A hankali ta ɗan fara ƙoƙarin tashi irin da gasken bata da lafiya. Abba be ce mata komai ba har ta sauko ta nemi kusa da inda Didi ta zauna a ƙasa tun zaman su Abba a kan kujera. Bayan shuɗewar wasu sakanni ba tare da kowa yace komai ba Abba ya soma faɗin
"Ashe suspension aka baki?" Ya yi maganar ba tare da ya ambaci suna ba. Da sauri Lulu ta ɗaga kai ta kalli Abba ƙirjinta na bugawa. Ganin shi ma itan yake kalla ya sanyata yin ƙasa da kai sannan ta soma haɗo maganganu tana inda inda.
"Suspension kuma?" Ammi ta faɗa cike da mamaki. Jinjina kai Abba ya yi kafin yace
"Ƙwarai kuwa,. Ta sake fusata malamin da rashin ɗa'a irin nata, shi ya sa ya bata hutun kwanaki, se dai be sani ba a shashanci irin na yarinyar nan daɗin hakan za ta ji.. Se dai wannan ɗin ba abin damuwa bane, dan kuwa ba ma bada kwanaki da aka yi ba, dama ko ba a yi hakan ba, daga yau kowaccensu ta gama zuwa makaranta se da izinin mijinta.." Ammi, Lulu, Didi gaba ɗaya kallan Abba suka yi jin wani saɓo da ya yi. Cike da mamakin furucinsa duka suke kallansa, se suke ganin kamar Abban be san abin da ya faɗa ba. Ganin kallan da suke binsa da shi ne ya sanya shi kallan Ammi da mamakinta yafi na kowa bayyana yace
"Ƙwarai kuwa a yau ɗin nan na aurar da Afaaf da kuma Afrah.." Cikin matuƙar tashin hankali Ammi tace ƙirjinta na bugawa
"Aure kuma? Aure na gaske kake nufi ko kuwa wanne Abbansu?" Ta tambaya fuskarta ɗauke da zallar mamaki da tashin hankali. Ajiyar zuciya Abba ya sauke dan ya ga alamar Ammin ta gama rikicewa, yace
"Aure dai kamar yadda muka yi ni dake.." Numfashi Ammi ta sauke da ƙarfi tana ɗauke kai a kan laɓɓanta ta furta
"Ya ilahy!" Se kuma ta kalli Abban a nutse tace
"Wa ka aurawa su Abba?" Ammi ta faɗa bugun zuciyarta na ƙaruwa. Kallan Twins Abba ya yi waɗanda kowaccensu su take kalla, jin abin suke kamar a mafarki, bama su yadda da gaske Abban yake ba. Kawai sun ɗauki hakan a matsayin wasa ne yau Abban yake musu. Wasan da idan dai har ba a yi saurin ƙarƙare shi ba zuciyoyi biyu na dab da bugawa.
"Na aurar dasu ne ga waɗanda suka dace, don kuwa ina fatan ko kuma nace idan Allah ya yadda ta silar auren nan wasu ɓangaren za su taimaki wasu ɓangaren, har su yi amfani da damar da Allah ya ba su wajen gyara abokanan zamansu, wanda kai tsaye zan iya kiran hakan da jihadi. Ki bari zan miki bayanin komai, kada ki tayar da hankalinki, dan kin riga da kin san uba ba ze taɓa zaɓarwa 'ya'yansa abin da ze cutar dasu ba. Dan haka ki kwantar da hankalinki.." Ita gaba ɗaya ma wasu maganganun na Abban ba fahimtar su take ba, dan haka ta ɗan girgiza kanta sannan tace
"Zan kwantar da hankalina Abbansu, amma bayan ka faɗa min wanda ka aura musu. Sannan kuma ka tabbatar min ni da 'ya'yana da gaske abin da kake faɗa gaskiya ne?"
"Ki dena tantama da wannan maganar, ba wasa bace. Da gaske na aurar da yaran nan a yau ɗin nan.." ya ƙare maganar yana kallan Twins da ke zaune kamar wasu shashashu ko waɗanda ba sa hayyacinsu. Gyara zama Abba ya yi sannan ya kalli Lulu ya ɗan yi murmushi kafin ya soma faɗin
"Shi dai wannan malamin naki da kika ɗauke shi ba a matsayin malaminki ba. Ki ke masa kallan wanda kike taimakawa kina zuwa makaranta bayan shi yake koyar dake. Ki ke masa kallan wulaƙantacce dan yana Malamin Addini. Ki ka yi watsi da tarbiyyar da muka baki ki ke rashin daraja gare shi. A yau ɗin kuma cikin ikon Allah na ba shi auranki... Ma'ana dai na aura masa ke, yanzu haka kin koma ƙarƙashinsa ne, dan kuwa ya zama mijinki.." Ɗan runtse idanunta Lulu ta yi sanda gaba ɗaya kanta ya buga. A hankali kuma ta ji wani jiri jiri na kwasarta duk da a zaune take, se ta ɗan yi gefe sannan ta kai hannunta ta riƙo kanta, daidai lokacin da take sake tuno maganganun da Abban ya faɗa, dan sake tabbatar da abin da kunnuwanta suka ji.
"Malam Affan!" Abba ya bawa Ammi da ta masa magana amsa. Wata ƙara Lulu ta saki sanda ta gama fahimtar inda zancen Abban ya dosa, gaba ɗaya idanunta suka makance a lokacin, kunnuwanta suka yi wani dumm, gangar jikinta ta kasa riƙeta, ƙirjinta ya cigaba da bugawa da gudun da ya mugun wuce na ƙa'ida. Saboda yanda ta ji kanta ya ɗaure tamau kamar wadda aka ɗorawa wani ƙaton abu akai, ya sanyata riƙo kan lokaci ɗaya tana faɗin
"Na shiga uku..." Tun kafin ta ida faɗar hakan ta yi wani baya kamar wadda aka ja, se kawai ta zube a wajen sumammiya. Abba, Ammi har ma da Didi duka kanta suka yi. Ammi na kiran sunanta cikin tsananin tashin hankali. Da ƙyar Didi ta iya ƙarasawa inda Lulun take, se dai ta kasa aikata komai, dan gaba ɗaya jikinta wani irin rawa yake kamar mazari. Haka zalika idanunta sun cika fall da ƙwalla, ita kaɗai kuma ta san yanda take jinta a cikin tashin hankali, har taso ta ɗan dena fahimtar wasu abubuwan saboda yanda ƙwaƙwalwarta ta toshe a lokacin. Tunda Abba ya ambaci sunan Gwani Affan a matsayin wanda ya aurawa Lulu, jikinta ya ɗauki zafi, ba ta taɓa zata ba, ba ta taɓa tsammani ba. Ga kuma er uwa rabin jiki a kwance kamar matacciya. Wannan tashin hankalin shi ne ya sanya ƙwalla zubowa daga cikin idanunta, se kuma wanda yafi kowanne, wato jiran jin sunan wanda Abba ze faɗa a matsayin wanda ya aura mata itama...
ALHAMDULILLAH! Anan na kawo ƙarshen A JINI TAKE Chapter one. Me son cigaba da karanta littafin A JINI TAKE Chapter two, ze tura ₦300 ne ta 8124818273, Zahra'u Yusuf Ishaq, Opay. Shedar biya ta 08124818273.
Don neman ƙarin bayani za a iya tuntuɓata ta 08124818273.