Sashe 33
A Jini Take Izzata Part 1 Compleete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh Ya mu'allim.." ta faɗa tana miƙewa ta fice daga ajin. Tunda ta ɗaga kai ta kalli Hafsa Abban dan tabbatar da da gasken bulala ya aika a karɓo masa ta kasa saukewa. Dukanta ze yi bayan an tabbatar da cewar ba ya duka? Kenan ita yake so ya wulaƙanta a cikin ajinsu? Shi ya sa ze daketa? Wayyo Allah, me ya sa ta bari hakan ke shirin faruwa? Daga lokacin da ya daketa da bulala kuma ai shi kenan ita kuma tata ta ƙare. Duk wani mutuncinta da en ajin ke gani ta san tsiyayewa ze yi tass ya bi rariya. Kallan banza da yake mata shi kuma se dai ya ƙaru tunda dai har ya daketa. Se ta yi ƙasa da kanta tana jin wata ƙwalla na taho mata, anya kuwa ba za ta bi zugar da take ji zuciyarta na mata ba? Anya kuwa za ta jure zama ya daketa kamar jaka? Ba kuwa za ta bi abin da zuciya ke saƙa mata ba, idan ya so ko hakan ne ze zama sanadiyyar korarta daga makarantar, a koreta ɗin. Ta san dai Abba da Ammi za su mata faɗa, idan ya kama ma su daketa, amma dai ta san ba za su karyata ko su kasheta ba, kuma dai koma mene ne daga ƙarshe dai ta tsira da mutuncinta a wajen Gwanin.
... "Haba Hero. Ya mun gama magana da kai kuma za kace min ka fasa ka samo wata zazzafar hanyar? Ni dai tunda ka fita kuma ban san me za ka ce min ba, dan wallahi jikina ya yi sanyi.." Ladi ta faɗa cikin rashin jin daɗi.
"Kin ga zauna anan ki ji.." ya yi maganar yana riƙo hannunta ya zaunar da ita gefensa.
"Ki tsaya ki saurare ni. Na gama aikina na farko ba tare da an samu wata matsala ba. Ina shirin gabatar da na biyun na ga wata hanya da idan muka bi ta za ta ɓillar da mu hanya ɗoɗar. Kin san Areef Matawalle? The only son of Alhaji Matawalle..?
"Ni kuwa na san shi. Duk da dai ban san shi a gaske ba, amma na san shi a hoto.."
"Gud.. Toh abokina ne.."
"Abokin ka kuma? How?" Ladi ta tambaya cike da mamaki. Ɗaga kafaɗa ya yi yana taɓe baki kafin yace
"Manta da wannan.. Ke dai ba kin gane a kan wanda nake magana ba?"
"Ehh na gane.."
"Toh garin aikina na farko, akasi ya saka yarinyar ta ɗauka shi ya rungumeta, tsausayi ya sakata sharara masa mari.. Toh tsausayi mana, dan kuwa Bad Man ba ya yafiya, wannan kamar a rubuce yake.."
"Kai ka bari Hero. Na shiga uku. Mari kuma? Lallai na sake tabbatar da rashin kunyar yarinyar nan. Amma dai me ze yi mata?" Dariya Hero ya sheƙe da ita kafin yace
"Ke ai mu aiki ya zo mana cikin sauƙi.. Ni ɗin nan ba ɗan gidan uban kowa bane." Ya yi maganar yana nuna kansa. Dariya Ladi ta yi tace
"Kuma a haka fa se a ɗauka kai ɗin ɗan gidan wani shegen ne.."
"Ah toh ya za a yi?" Ya faɗa yana sakin dariyar gefen baki. Se ya ɗora da faɗin
"Sunan mahaifin yarinyar can Alhaji Muhammad Aji. Duk da dai ba wani shahararren me kuɗi bane amma dai yana da rufin asirin da ze iya kai ƙara.Ke kin san ko ba shi da hali ma ze ɗauki mataki ne, kin san talakawa da buri. Idan dai har na aikatawa ɗiyarsa wani abun na san ze ɗauki mataki a kaina ni ɗin da ba ni da kowa.." ya ƙare cike da izgili yana wani rausayar da kai. Har se da hakan ya sanya Ladi sheƙewa da dariya. Se dai kafin tace komai ya ɗora da faɗin
"Shi kuwa Bad Man ɗan gidan Alhaji Matawalle ne, kina tunanin akwai wanda ze iya shari'a da shi bayan wannan shegen kuɗin da yake da su? Bar shi ma a wani me taurin kan ze iya, amma kina tunanin duk wanda ze yi shari'a da Matawalle ze yi nasara a kansa ne?" Ɗan shiru Ladi ta yi tana nazarin maganar Hero ɗin. Can dai tace
"Fito min a mutum. Me ka ke so ka ce?" Gyara zama ya yi sannan ya soma faɗin
"Yace ze je har gidansu a kan mari kawai.. ya ki ke gani idan al'amarin da nake ƙoƙarin aikatawa ya koma kansa? Komai ze zo da sauƙi dan na riga na san Bad Man ba ze yi zaman kurkuru ba. Kin ga ba a saka ni a matsala ba ke kuma kin samu cikar burinki.." Murmushi Ladi ta shiga yi cike da gamsuwa da maganar Hero ɗin. Se kuma can tace
"Amma kuma idan aka samu matsala aka riƙe abokin naka a gidan yari fa?" Ɗan taɓe baki Hero ya yi sannan yace
"Ehh toh.. duk can za ta ƙare musu. Ke dai ba kin samu abin da kike so ba?" Dariya Ladi ta yi sosai, jin yadda Hero ɗin ya zame kansa daga wannan al'amarin cikin ƙanƙanin lokaci.
"Lallai Hero ban san da abin da zan biyaka ba. Kai ɗin na daban ne Hero. Duk wanda ya samu kwanya irin taka ya godewa Allah, dan wallahi ba duk kai ba.." Dariya ya yi jin yanda take ta fasa masa kai.
"Amma tsaya? Kamar na san halin Alhaji Matawalle fa a kan ra'ayin riƙau, da son gaskiya, har ma da kula da tarbiyyar wasu bare nasa. Kana nufin kace min duk waɗannan halayen nasa da suka janyo masa baƙin jini a wajen wasu mutanen ɗansa guda ɗayan nan yana neman mata?" Shiru Hero ya yi na tsawon sakanni, kafin can yace
"Gaskiya dai a'ah.. Amma a wannan karon ze fara..!!"
https://chat.whatsapp.com/BClMNPwWybg2n3oRvtemv8
*♡☆A JINI TAKE☆♡*
*(IZZATA)*
By
_*ZARAH MAITAMA (Mhiz Innocent)*_
*CHAPTER ONE*
Page_21~22
... Babu daɗewa Hafsa Abba ta shigo ajin hannunta ɗauke da bulalar. Da sauri Lulu ta kalleta ganin da gasken karɓowa ta yi. Babu ɓata lokaci ta ƙarasa ta miƙawa Gwani. Karɓa ya yi, ita kuma ta koma wajenta ta zauna. A hankali ta ɗan kalli Gwanin se ta ga yana ƙoƙarin miƙewa. Cikin rawar murya tace
"Ya Sayyadi Fatima fa ta faɗa maka.." ta faɗa dan ganin mafita ta ƙwace mata. Ɗan shiru Gwani ya yi a ransa yana saƙa abin da ya kamata ya yi wa Lulun. Dan kuwa shi kansa ya san ba dukan ze yi ba, saboda ba ya jin har abada ze iya kai hannunsa jikin mace, gani yake kamar wani saɓo ne ze aikata. Be fasa miƙewar ba hannunsa ɗauke da bulalar da tun shigowarsa makarantar be taɓa riƙewa ba yace bayan ya kalleta fuskarsa a ɗaure
"Ka da ki sake zuwa makarantar nan, se bayan kwana biyu.." Ya faɗa, daga haka ya fice daga ajin. Duka en ajin bin Lulu suka yi da kallo, masu mata kallan mara tarbiyya na cigaba da yi. Masu mata kallan wadda ba ta jin magana na cigaba da yi. A hankali kuma se kowa ya fara zamewa daga cikin ajin, har kuma lokacin Lulu na tsugune kamar wadda aka dasa.
"Ki tashi mu tafi.." Fatima ta faɗa tana riƙota. Se a lokacin ta miƙe jikinta a matuƙar sanyaye se dai fuskarta kamar wadda aka yi wa mutuwa. Ta sauke numfashi tana hararar iska sannan ta kalli cikin ajin. Didi na tsaye tana jiransu su wuce, se dai ba ta ko kalli inda Lulu take ba. Ganin da tayi ta miƙe ne ya sanyata ficewa daga cikin ajin, se suma suka bi bayanta.
"Aikin kawai. Ka daɗe ba ka ba ni suspension ɗin ba mana.." Lulu ta faɗa sanda suka fito. Kallanta Fatima ta yi tace
"A'ah Masoyiya.. Idan kika je gida me za ki cewa Ammi?"
"Uhmm me basirata take yi? Cewa zan yi ba ni da lafiya. Ai ni wallahi ma ya ba ni lasisin da zan ji daɗin rayuwata na kwana biyu ba tare da na gan shi ba"
"Hmmm.." Fatima ta faɗa. Bayan shuɗewar wasu sakanni tace
"Amma dai Masoyiya ya kamata ki dinga sassautawa. Wannan abin ya yi yawa wallahi. Kuma su Abba za ki janyowa, don Allah ki bari.."
"Toh.." Lulu ta faɗa kawai. Har suka je gida Didi ba tace da Lulu komai ba, ta barta ta yi abin da ta ga dama, tunda ba ta jin magana. Itama kuma Lulun se ta share Didin, dan ka da ta mata magana ma ta tuna abin da ya faru, ballantana ma har ta faɗawa Ammi ko Abba. Dan haka se ta mata shiru, idan kwana biyun suka wuce se ta kulata.
... "Ki tashi ki fito mu ci abinci koh?" Ammi ta faɗa tana kallan Lulu da ke cikin blanket ita a lallai dole mara lafiya.
"Ammi na ƙoshi. Wallahi bacci nake ji.." Ƙarasowa Ammi ta yi cikin ɗakin zuwa kan gadon ta nemi waje ta zauna. Yaye blanket ɗin ta yi sannan tace
"Lafiya kike kuwa? Me ke damunki?"
"Ammi zazzaɓi ne a jikina.." ta faɗa tana runtse idanu.
"Zazzaɓi a jikinki kuma shi ne ba za ki faɗa min ba? Wannan ai shashanci ne. Tun yaushe kike jinsa?" Ammi ta faɗa tana taɓa goshin Lulun. Jin sanyi ƙalau ya sanyata faɗin
"Ikon Allah! Kuma babu zafi jikinki.."
"A cikin jikina nake jinsa.." Lulu ta faɗa tana rungumo bargo. Miƙewa Ammi ta yi tace
"Kin ga tashi maza ki shirya mu wuce asibiti.." Waro idanu Lulu ta yi tana jin yadda hantar cikinta ta kaɗa. Da sauri tace
"Ammi ba se mun je ba don Allah. Zan warke ne wallahi.." Ɓata rai Ammi ta yi tana kallanta tace
"Ki tashi nace koh?"
"Don Allah Ammi, don Allah kar mu je.."
"A wane dalilin zamu ƙi zuwa wai? Za ki tashi mu wuce koh se na zo na saɓa miki duk da baki da lafiya?" Ammi ta faɗa tana yaye blanket ɗin gaba ɗaya. Se a lokacin Lulu ta miƙe lokacin da ƙwalla ta cika idanunta taff. Haka ta miƙe ta buɗe wardrobe ta fito da hijab ta zura. Haka tana ji tana gani Ammi ta sakata a gaba suka fito parlour.
... "Haba Hero. Ya mun gama magana da kai kuma za kace min ka fasa ka samo wata zazzafar hanyar? Ni dai tunda ka fita kuma ban san me za ka ce min ba, dan wallahi jikina ya yi sanyi.." Ladi ta faɗa cikin rashin jin daɗi.
"Kin ga zauna anan ki ji.." ya yi maganar yana riƙo hannunta ya zaunar da ita gefensa.
"Ki tsaya ki saurare ni. Na gama aikina na farko ba tare da an samu wata matsala ba. Ina shirin gabatar da na biyun na ga wata hanya da idan muka bi ta za ta ɓillar da mu hanya ɗoɗar. Kin san Areef Matawalle? The only son of Alhaji Matawalle..?
"Ni kuwa na san shi. Duk da dai ban san shi a gaske ba, amma na san shi a hoto.."
"Gud.. Toh abokina ne.."
"Abokin ka kuma? How?" Ladi ta tambaya cike da mamaki. Ɗaga kafaɗa ya yi yana taɓe baki kafin yace
"Manta da wannan.. Ke dai ba kin gane a kan wanda nake magana ba?"
"Ehh na gane.."
"Toh garin aikina na farko, akasi ya saka yarinyar ta ɗauka shi ya rungumeta, tsausayi ya sakata sharara masa mari.. Toh tsausayi mana, dan kuwa Bad Man ba ya yafiya, wannan kamar a rubuce yake.."
"Kai ka bari Hero. Na shiga uku. Mari kuma? Lallai na sake tabbatar da rashin kunyar yarinyar nan. Amma dai me ze yi mata?" Dariya Hero ya sheƙe da ita kafin yace
"Ke ai mu aiki ya zo mana cikin sauƙi.. Ni ɗin nan ba ɗan gidan uban kowa bane." Ya yi maganar yana nuna kansa. Dariya Ladi ta yi tace
"Kuma a haka fa se a ɗauka kai ɗin ɗan gidan wani shegen ne.."
"Ah toh ya za a yi?" Ya faɗa yana sakin dariyar gefen baki. Se ya ɗora da faɗin
"Sunan mahaifin yarinyar can Alhaji Muhammad Aji. Duk da dai ba wani shahararren me kuɗi bane amma dai yana da rufin asirin da ze iya kai ƙara.Ke kin san ko ba shi da hali ma ze ɗauki mataki ne, kin san talakawa da buri. Idan dai har na aikatawa ɗiyarsa wani abun na san ze ɗauki mataki a kaina ni ɗin da ba ni da kowa.." ya ƙare cike da izgili yana wani rausayar da kai. Har se da hakan ya sanya Ladi sheƙewa da dariya. Se dai kafin tace komai ya ɗora da faɗin
"Shi kuwa Bad Man ɗan gidan Alhaji Matawalle ne, kina tunanin akwai wanda ze iya shari'a da shi bayan wannan shegen kuɗin da yake da su? Bar shi ma a wani me taurin kan ze iya, amma kina tunanin duk wanda ze yi shari'a da Matawalle ze yi nasara a kansa ne?" Ɗan shiru Ladi ta yi tana nazarin maganar Hero ɗin. Can dai tace
"Fito min a mutum. Me ka ke so ka ce?" Gyara zama ya yi sannan ya soma faɗin
"Yace ze je har gidansu a kan mari kawai.. ya ki ke gani idan al'amarin da nake ƙoƙarin aikatawa ya koma kansa? Komai ze zo da sauƙi dan na riga na san Bad Man ba ze yi zaman kurkuru ba. Kin ga ba a saka ni a matsala ba ke kuma kin samu cikar burinki.." Murmushi Ladi ta shiga yi cike da gamsuwa da maganar Hero ɗin. Se kuma can tace
"Amma kuma idan aka samu matsala aka riƙe abokin naka a gidan yari fa?" Ɗan taɓe baki Hero ya yi sannan yace
"Ehh toh.. duk can za ta ƙare musu. Ke dai ba kin samu abin da kike so ba?" Dariya Ladi ta yi sosai, jin yadda Hero ɗin ya zame kansa daga wannan al'amarin cikin ƙanƙanin lokaci.
"Lallai Hero ban san da abin da zan biyaka ba. Kai ɗin na daban ne Hero. Duk wanda ya samu kwanya irin taka ya godewa Allah, dan wallahi ba duk kai ba.." Dariya ya yi jin yanda take ta fasa masa kai.
"Amma tsaya? Kamar na san halin Alhaji Matawalle fa a kan ra'ayin riƙau, da son gaskiya, har ma da kula da tarbiyyar wasu bare nasa. Kana nufin kace min duk waɗannan halayen nasa da suka janyo masa baƙin jini a wajen wasu mutanen ɗansa guda ɗayan nan yana neman mata?" Shiru Hero ya yi na tsawon sakanni, kafin can yace
"Gaskiya dai a'ah.. Amma a wannan karon ze fara..!!"
https://chat.whatsapp.com/BClMNPwWybg2n3oRvtemv8
*♡☆A JINI TAKE☆♡*
*(IZZATA)*
By
_*ZARAH MAITAMA (Mhiz Innocent)*_
*CHAPTER ONE*
Page_21~22
... Babu daɗewa Hafsa Abba ta shigo ajin hannunta ɗauke da bulalar. Da sauri Lulu ta kalleta ganin da gasken karɓowa ta yi. Babu ɓata lokaci ta ƙarasa ta miƙawa Gwani. Karɓa ya yi, ita kuma ta koma wajenta ta zauna. A hankali ta ɗan kalli Gwanin se ta ga yana ƙoƙarin miƙewa. Cikin rawar murya tace
"Ya Sayyadi Fatima fa ta faɗa maka.." ta faɗa dan ganin mafita ta ƙwace mata. Ɗan shiru Gwani ya yi a ransa yana saƙa abin da ya kamata ya yi wa Lulun. Dan kuwa shi kansa ya san ba dukan ze yi ba, saboda ba ya jin har abada ze iya kai hannunsa jikin mace, gani yake kamar wani saɓo ne ze aikata. Be fasa miƙewar ba hannunsa ɗauke da bulalar da tun shigowarsa makarantar be taɓa riƙewa ba yace bayan ya kalleta fuskarsa a ɗaure
"Ka da ki sake zuwa makarantar nan, se bayan kwana biyu.." Ya faɗa, daga haka ya fice daga ajin. Duka en ajin bin Lulu suka yi da kallo, masu mata kallan mara tarbiyya na cigaba da yi. Masu mata kallan wadda ba ta jin magana na cigaba da yi. A hankali kuma se kowa ya fara zamewa daga cikin ajin, har kuma lokacin Lulu na tsugune kamar wadda aka dasa.
"Ki tashi mu tafi.." Fatima ta faɗa tana riƙota. Se a lokacin ta miƙe jikinta a matuƙar sanyaye se dai fuskarta kamar wadda aka yi wa mutuwa. Ta sauke numfashi tana hararar iska sannan ta kalli cikin ajin. Didi na tsaye tana jiransu su wuce, se dai ba ta ko kalli inda Lulu take ba. Ganin da tayi ta miƙe ne ya sanyata ficewa daga cikin ajin, se suma suka bi bayanta.
"Aikin kawai. Ka daɗe ba ka ba ni suspension ɗin ba mana.." Lulu ta faɗa sanda suka fito. Kallanta Fatima ta yi tace
"A'ah Masoyiya.. Idan kika je gida me za ki cewa Ammi?"
"Uhmm me basirata take yi? Cewa zan yi ba ni da lafiya. Ai ni wallahi ma ya ba ni lasisin da zan ji daɗin rayuwata na kwana biyu ba tare da na gan shi ba"
"Hmmm.." Fatima ta faɗa. Bayan shuɗewar wasu sakanni tace
"Amma dai Masoyiya ya kamata ki dinga sassautawa. Wannan abin ya yi yawa wallahi. Kuma su Abba za ki janyowa, don Allah ki bari.."
"Toh.." Lulu ta faɗa kawai. Har suka je gida Didi ba tace da Lulu komai ba, ta barta ta yi abin da ta ga dama, tunda ba ta jin magana. Itama kuma Lulun se ta share Didin, dan ka da ta mata magana ma ta tuna abin da ya faru, ballantana ma har ta faɗawa Ammi ko Abba. Dan haka se ta mata shiru, idan kwana biyun suka wuce se ta kulata.
... "Ki tashi ki fito mu ci abinci koh?" Ammi ta faɗa tana kallan Lulu da ke cikin blanket ita a lallai dole mara lafiya.
"Ammi na ƙoshi. Wallahi bacci nake ji.." Ƙarasowa Ammi ta yi cikin ɗakin zuwa kan gadon ta nemi waje ta zauna. Yaye blanket ɗin ta yi sannan tace
"Lafiya kike kuwa? Me ke damunki?"
"Ammi zazzaɓi ne a jikina.." ta faɗa tana runtse idanu.
"Zazzaɓi a jikinki kuma shi ne ba za ki faɗa min ba? Wannan ai shashanci ne. Tun yaushe kike jinsa?" Ammi ta faɗa tana taɓa goshin Lulun. Jin sanyi ƙalau ya sanyata faɗin
"Ikon Allah! Kuma babu zafi jikinki.."
"A cikin jikina nake jinsa.." Lulu ta faɗa tana rungumo bargo. Miƙewa Ammi ta yi tace
"Kin ga tashi maza ki shirya mu wuce asibiti.." Waro idanu Lulu ta yi tana jin yadda hantar cikinta ta kaɗa. Da sauri tace
"Ammi ba se mun je ba don Allah. Zan warke ne wallahi.." Ɓata rai Ammi ta yi tana kallanta tace
"Ki tashi nace koh?"
"Don Allah Ammi, don Allah kar mu je.."
"A wane dalilin zamu ƙi zuwa wai? Za ki tashi mu wuce koh se na zo na saɓa miki duk da baki da lafiya?" Ammi ta faɗa tana yaye blanket ɗin gaba ɗaya. Se a lokacin Lulu ta miƙe lokacin da ƙwalla ta cika idanunta taff. Haka ta miƙe ta buɗe wardrobe ta fito da hijab ta zura. Haka tana ji tana gani Ammi ta sakata a gaba suka fito parlour.