Sashe 24
A Jini Take Izzata Part 1 Compleete Hausa Novel · about 8 min read
"Hakan ya yi. Duk da dai na so na ɗan ƙara hutawa amma babu damuwa." Ya faɗa cikin er basarwa yana cizon lips ɗinsa na ƙasa lokaci ɗaya wani ƙawataccen murmushi na tashi a kan kyakkyawar fuskarsa. Jinjina kai Daddy ya yi sannan yace
"Tohm shi kenan, Allah ya taimaka. Yanzu se ku faɗa min duk wani abu da kuke buƙata, ina so ne a yau na sallameku zan shiga wasu sabgogin ne."
.. A ɓangarensu Lulu kuwa lokacin da suka koma cikin ɗakin su Abba basa nan, hakan ne ya sanyasu wucewa nasu ɗakin kawai. Ajiyar zuciya Didi ta sauke sanda ta zauna a gefen gadonsu tana faɗin
"Na shiga ukuna." Ta yi maganar tana dafe ƙirji. Da sauri Lulu ta ƙaraso tana faɗin
"Me ya faru Didi?" Se kuma ta girgiza kai tace bayan ta ɓata fuska
"Ba komai fa. Amma kuma me yasa Abba yace mu je wai? Na ga dai idan mutum ya fara zance ai aure ake masa koh?" Didi ta faɗa tana kallan Lulu. Ɗan ɗage idanu Lulu ta yi kafin tace cike da tsokana
"Umm ƙila aurar da Didina ze yi." Duka Didi ta kaiwa Lulun, se ta yi saurin tashi daga wajen tana dariya lokaci ɗaya tana faɗin
"Sorry my luv. Da wasa fa nake wallahi." Ta faɗa dan ta ga alamar Didin ta ɗauka da gaske take.
"Ni dai zuwa zan yi na maimaita karatu, gobe islamiyya.." Didi ta faɗa tana ƙarasawa wajen jakarta ta ɗauka. Wani irin bugawa zuciyar Lulu ta yi sanda ta tuna da abin da ya faru, ita sam ta manta se yanzu da Didin ta yi maganar islamiyya sannan ta tuna. Se ta nemi waje kawai ta zauna tana lumshe idanunta. Bata ankara ba se ji ta yi Didi ta dafa kafaɗarta a hankali, cikin rarrashi tace
"Lulu me ya faru ne wai?" Da sauri ta riƙo hannun Didin sosai sanda farar fuskarta ta ɗan yi ja ta soma faɗin
"Didi mutane abin tsoro ne, na tsorata matuƙa. Na rasa yanda zan yi na faɗa miki ko ke ko Ammi. Amma ina tsoron na yi shiru ta je ta cigaba da jan mutane." Cikin rashin fahimta Didi tace
"Wai a kan me ki ke magana ne? Wace ce?"
"Abida.." Lulu ta faɗa. Daga haka ta shiga labartawa Didi abin da ya faru tun daga farko har ƙarshe. Gaba ɗaya Didin se ta ruɗe, ilahirin jikinta ya ɗauki rawa. Se ta ja Lulun jikinta tana faɗin muryarta na rawa, har idanunta sun kawo ƙwalla
"Babu abin da suka miki koh? Ba su miki komai ba koh?" Jinjina kai Lulu ta yi kafin tace
"Ehh fa Didi."
"Tashi mu je mu faɗawa Ammi." Didi ta faɗa tana ƙoƙarin miƙewa. Da sauri Lulu ta riƙota tana girgiza kai tace
"Kin san dai halin Ammi, yanzun nan za ta ɗaga hankalinta har abin ya zo ya dinga damunta. Ki yi shiru kawai tunda dai Allah ya kuɓutar dani.." girgiza kai Didi ta yi tace
"A'ah gwara kawai a faɗa mata ɗin."
"A'ah Didi, mu bar shi kawai a tsakaninmu se kuma a islamiyya da zan tona mata asiri." Buɗe ido Didi ta yi tace bayan ta girgiza kai
"Kin san mene tonon asiri kuwa Lulu? Ai ta riga ta san kin santa, ba za ta nuna halinta a makarantar nan ba. Se dai kawai a yi mata barazana saboda tsaro. Ke idan ma tana tsoron ka da asirinta ya tonu za ki ga ta ja baya da zuwa makarantar, mu kuma daga yau za mu dinga saka mata ido, idan hakan ya yi toh shi kenan, idan kuma be yi ba se mu sanar da wani malamin."
"Amma Didi.." lumshe idanunta Didi ta yi tana jinjinawa Lulun kai. Ba dan ta so ba tace
"Toh Allah ya ƙara tsarewa."
"Ameen." Didi ta faɗa tana tuna yanda tun farko ta kasa aminta da yarinyar, ashe mutuniyar banza ce, shi ne hadda ɗauko ƙazaman ƙafafuwanta ta zo gidansu. Se ta girgiza kai kawai, daidai lokacin da Ammi ta shigo ɗakin
"Me ya faru?" Ta tambaya sanda ta gansu kamar masu zaman makoki. Da sauri dukansu suka wanzar da murmushi kan fuskarsu kafin suka ce
"Babu komai Ammi." Duk da bata yarda ba, amma se ta bar shi ɗin kawai, a tunaninta may be magana ce a tsakaninsu da basa so ta sani, dan ta san idan da suna so ta sani ɗin su da kansu zasu zo su faɗa mata.
... Kiran wayar Ladi da ya shigo cikin ƙatuwar wayarta Abida ta kalla. ta ja doguwar ajiyar zuciya tana tunanin yanda za ta ɓillowa Ladi, tun farko ta sani ba ta kai mata zancen Lulu ba, da yanzu ita da kanta za ta dinga fakar Lulun tunda itama tana sonta. Se dai kuma tunda Ladin ta ƙyalla ido a kanta ya zama dole ita ta haƙura da ita. A karo na barkatai kiran Ladin ya sake shigowa cikin wayarta, se ta jefar da wayar gefe tana faɗin
"Na shiga ukuna.." ta yi maganar tana dafe kanta, ita kam yau ta ga ta kanta. Ba za ta iya ɗaga kiran Ladin ba, dan ko ta ɗaga ma ba ta san me za tace mata ba, saboda ta tabbatar maganar Lulu za ta mata. Se dai kuma ta san shi kansa rashin ɗaga kiran matsala ne, hakan ne ya sanyata janyo wayar ta kasheta gaba ɗaya. Tun ɗazu take kwance a gida ta kasa fita ko nan da can ne, ballantana kuma a yi zancen islamiyya, dan ita dai har yanzu tsoron zuwa take bare ta haɗu da Lulu, dan ita kanta za ta iya zama sheda a kan Lulun ba ta da kirki. Ta riga ta tsara yau ba za ta je makarantar ba, duk yadda ake ciki dai se gobe za ta je, kafin lokacin ta gama tsarawa kanta yadda za ta ɓillowa Lulun har ta yadda da ita ta sake kaita wajen Ladi. Hakan ne ya sanyata gyara kwanciyarta ta soma saƙawa da warwarewa duk a kan Lulun.
___"Duk wanda ba shi da littafin ya fita.." Gwani ya yi maganar lokacin da yake buɗe nasa littafin. Kallan Lulu Didi ta yi ganin tana shirin miƙewa, dama ita haka take so, dan ba ƙauna ma take ya dinga shigo musu aji ba.
"Wai dama ba ki zo da shi ba?" Didi ta tambaya ƙasa_ƙasa. Jinjina kai ta yi tana ɓata fuska
"Allah kuwa se na faɗawa Ammi wannan rashin kirkin da kike yi." Didi ta faɗa tana ɗauke kai ta maida kanta kan littafin hannunta. Ita dai Lulu burinta kawai ta fice daga ajin. Se kuwa ta saɓi jiki tana wani ciccin magani ita a lallai dole kar ya rainata. Ko kallan sharar da ta kwasota be yi ba, kai ba ma za ka ce ya san ta fita ba. Se dai tana ficewar ya yi gyaran murya sannan ya yi sallama cikin muryar nan tasa da duk lokacin da yake larabci ba za ka yi tunanin idan ka yi masa hausa ze ji ba. Cike da farin ciki Lulu kuwa ta nemi wani aji da babu kowa a ciki ta zauna, dama tana sane taƙi zuwa da littafin dan ya koreta. Se kuwa ta zauna abinta inda ta san har ya gama ba za ta jiyo muryarsa ba. Kafin a tashi Gwani ya bar makarantar zuwa asibiti, dan haka se Malam Ahmad ya shigo ya karɓi ajin. Se a lokacin sannan Lulu ta shigo ajin, tana ƙoƙarin ƙarasawa kusa da Didi ta jiyo muryar Malam Ahmad ɗin na faɗin
"Afaaf Muhammad Aji.." se ta dakata sannan ta ɗaga kanta ta kalle shi kana ta amsa da
"Na'am.."
"Daga ina?" Ya tambaya yana kallanta. Dan tsabar shaƙiyanci da rashin kirki irin na Lulu, se ta ɗan yi shiru a ranta tana tuna sunan da ya kamata ta yi amfani da shi ba tare da ta ambaci sunan Gwani ba, dan se take ji kamar ta manta sunan nasa ma, hakan ne ya sanyata faɗin
"Littafi ne ba ni da shi, shi ne ya koreni.."
"Waye..?" Ya sake tambaya. Ji ta yi kamar kawai ta yi wucewarta ba tare da ta amsa masa tambayar ba, se dai ba ta yi hakan ba. Amma kenan yana nufin dole dai se ta faɗi sunan kuma ta fara faɗar wata kalmar girmamawar kafin sunan shi. Duk da baya kusa amma ai mutane suna ji.
"Amma ya aka yi ke Afrah ki ke da shi?" Malam Ahmad ya katseta da faɗin hakan yana kallan Didi. Se da Didi ta sauke ajiyar zuciya sannan cikin niƙab ɗinta ta furta
"Ya mu'allim manta guda ɗaya muka yi a gida." Ɗan numfashi kaɗan ya sauke sannan yace
"Shi kenan, je ki zauna." A hankali ta ƙarasa cikin ajin ta nemi waje ta zauna. Didi ko kallanta ba ta yi ba, dan yau ɗin da gaske ta ji haushin abin da Lulun ke yi sosae.
"Idan Allah ya kai mu anjima, za a je dubiyar mahaifin Malam Affan kamar yanda muka sanar jiya. Waɗanda za su je se su jirani a harabar makaranta." Malam Ahmad ya faɗa. daga nan be wani daɗe ba ya fita daga ajin. Gaba ɗaya en ajin a harabar makarantar suka haɗu, dan kowannensu na son zuwa gaishe da mahaifin Gwanin ko dan kirkinsa a garesu. Se dai ita kam Lulu kallan Didi da har lokacin ba ta kalleta ba ta yi tace
"Bari na je na ɗauki Little mu tafi. Se kun dawo.." da sauri Didi ta kalleta cike da mamakin jin furucinta. "Wai me ke damun Lulun? Anya kuwa kanta ɗaya? Me ye haka take yi kamar wani maƙiyinta ne Gwani? Me yasa ta ɗauki abin da yake mata a matsayin tsana, bayan kullum ita ke janyowa kanta? Fuskarta a haɗe duk da tana cikin niƙab amma Lulu ta fuskanci hakan. Ta kuma sake tabbatar da fushin ne sanda ta soma faɗin
"Wai Lulu me ye haka ne? Abin da kike yi kina ganin daidai ne? Mene ne aibu dan kin je kin duba mahaifinsa ko kuwa za a gutsiri naman jikinki ne?" Ta ƙare tana kallan Lulun.
"Tohm shi kenan, Allah ya taimaka. Yanzu se ku faɗa min duk wani abu da kuke buƙata, ina so ne a yau na sallameku zan shiga wasu sabgogin ne."
.. A ɓangarensu Lulu kuwa lokacin da suka koma cikin ɗakin su Abba basa nan, hakan ne ya sanyasu wucewa nasu ɗakin kawai. Ajiyar zuciya Didi ta sauke sanda ta zauna a gefen gadonsu tana faɗin
"Na shiga ukuna." Ta yi maganar tana dafe ƙirji. Da sauri Lulu ta ƙaraso tana faɗin
"Me ya faru Didi?" Se kuma ta girgiza kai tace bayan ta ɓata fuska
"Ba komai fa. Amma kuma me yasa Abba yace mu je wai? Na ga dai idan mutum ya fara zance ai aure ake masa koh?" Didi ta faɗa tana kallan Lulu. Ɗan ɗage idanu Lulu ta yi kafin tace cike da tsokana
"Umm ƙila aurar da Didina ze yi." Duka Didi ta kaiwa Lulun, se ta yi saurin tashi daga wajen tana dariya lokaci ɗaya tana faɗin
"Sorry my luv. Da wasa fa nake wallahi." Ta faɗa dan ta ga alamar Didin ta ɗauka da gaske take.
"Ni dai zuwa zan yi na maimaita karatu, gobe islamiyya.." Didi ta faɗa tana ƙarasawa wajen jakarta ta ɗauka. Wani irin bugawa zuciyar Lulu ta yi sanda ta tuna da abin da ya faru, ita sam ta manta se yanzu da Didin ta yi maganar islamiyya sannan ta tuna. Se ta nemi waje kawai ta zauna tana lumshe idanunta. Bata ankara ba se ji ta yi Didi ta dafa kafaɗarta a hankali, cikin rarrashi tace
"Lulu me ya faru ne wai?" Da sauri ta riƙo hannun Didin sosai sanda farar fuskarta ta ɗan yi ja ta soma faɗin
"Didi mutane abin tsoro ne, na tsorata matuƙa. Na rasa yanda zan yi na faɗa miki ko ke ko Ammi. Amma ina tsoron na yi shiru ta je ta cigaba da jan mutane." Cikin rashin fahimta Didi tace
"Wai a kan me ki ke magana ne? Wace ce?"
"Abida.." Lulu ta faɗa. Daga haka ta shiga labartawa Didi abin da ya faru tun daga farko har ƙarshe. Gaba ɗaya Didin se ta ruɗe, ilahirin jikinta ya ɗauki rawa. Se ta ja Lulun jikinta tana faɗin muryarta na rawa, har idanunta sun kawo ƙwalla
"Babu abin da suka miki koh? Ba su miki komai ba koh?" Jinjina kai Lulu ta yi kafin tace
"Ehh fa Didi."
"Tashi mu je mu faɗawa Ammi." Didi ta faɗa tana ƙoƙarin miƙewa. Da sauri Lulu ta riƙota tana girgiza kai tace
"Kin san dai halin Ammi, yanzun nan za ta ɗaga hankalinta har abin ya zo ya dinga damunta. Ki yi shiru kawai tunda dai Allah ya kuɓutar dani.." girgiza kai Didi ta yi tace
"A'ah gwara kawai a faɗa mata ɗin."
"A'ah Didi, mu bar shi kawai a tsakaninmu se kuma a islamiyya da zan tona mata asiri." Buɗe ido Didi ta yi tace bayan ta girgiza kai
"Kin san mene tonon asiri kuwa Lulu? Ai ta riga ta san kin santa, ba za ta nuna halinta a makarantar nan ba. Se dai kawai a yi mata barazana saboda tsaro. Ke idan ma tana tsoron ka da asirinta ya tonu za ki ga ta ja baya da zuwa makarantar, mu kuma daga yau za mu dinga saka mata ido, idan hakan ya yi toh shi kenan, idan kuma be yi ba se mu sanar da wani malamin."
"Amma Didi.." lumshe idanunta Didi ta yi tana jinjinawa Lulun kai. Ba dan ta so ba tace
"Toh Allah ya ƙara tsarewa."
"Ameen." Didi ta faɗa tana tuna yanda tun farko ta kasa aminta da yarinyar, ashe mutuniyar banza ce, shi ne hadda ɗauko ƙazaman ƙafafuwanta ta zo gidansu. Se ta girgiza kai kawai, daidai lokacin da Ammi ta shigo ɗakin
"Me ya faru?" Ta tambaya sanda ta gansu kamar masu zaman makoki. Da sauri dukansu suka wanzar da murmushi kan fuskarsu kafin suka ce
"Babu komai Ammi." Duk da bata yarda ba, amma se ta bar shi ɗin kawai, a tunaninta may be magana ce a tsakaninsu da basa so ta sani, dan ta san idan da suna so ta sani ɗin su da kansu zasu zo su faɗa mata.
... Kiran wayar Ladi da ya shigo cikin ƙatuwar wayarta Abida ta kalla. ta ja doguwar ajiyar zuciya tana tunanin yanda za ta ɓillowa Ladi, tun farko ta sani ba ta kai mata zancen Lulu ba, da yanzu ita da kanta za ta dinga fakar Lulun tunda itama tana sonta. Se dai kuma tunda Ladin ta ƙyalla ido a kanta ya zama dole ita ta haƙura da ita. A karo na barkatai kiran Ladin ya sake shigowa cikin wayarta, se ta jefar da wayar gefe tana faɗin
"Na shiga ukuna.." ta yi maganar tana dafe kanta, ita kam yau ta ga ta kanta. Ba za ta iya ɗaga kiran Ladin ba, dan ko ta ɗaga ma ba ta san me za tace mata ba, saboda ta tabbatar maganar Lulu za ta mata. Se dai kuma ta san shi kansa rashin ɗaga kiran matsala ne, hakan ne ya sanyata janyo wayar ta kasheta gaba ɗaya. Tun ɗazu take kwance a gida ta kasa fita ko nan da can ne, ballantana kuma a yi zancen islamiyya, dan ita dai har yanzu tsoron zuwa take bare ta haɗu da Lulu, dan ita kanta za ta iya zama sheda a kan Lulun ba ta da kirki. Ta riga ta tsara yau ba za ta je makarantar ba, duk yadda ake ciki dai se gobe za ta je, kafin lokacin ta gama tsarawa kanta yadda za ta ɓillowa Lulun har ta yadda da ita ta sake kaita wajen Ladi. Hakan ne ya sanyata gyara kwanciyarta ta soma saƙawa da warwarewa duk a kan Lulun.
___"Duk wanda ba shi da littafin ya fita.." Gwani ya yi maganar lokacin da yake buɗe nasa littafin. Kallan Lulu Didi ta yi ganin tana shirin miƙewa, dama ita haka take so, dan ba ƙauna ma take ya dinga shigo musu aji ba.
"Wai dama ba ki zo da shi ba?" Didi ta tambaya ƙasa_ƙasa. Jinjina kai ta yi tana ɓata fuska
"Allah kuwa se na faɗawa Ammi wannan rashin kirkin da kike yi." Didi ta faɗa tana ɗauke kai ta maida kanta kan littafin hannunta. Ita dai Lulu burinta kawai ta fice daga ajin. Se kuwa ta saɓi jiki tana wani ciccin magani ita a lallai dole kar ya rainata. Ko kallan sharar da ta kwasota be yi ba, kai ba ma za ka ce ya san ta fita ba. Se dai tana ficewar ya yi gyaran murya sannan ya yi sallama cikin muryar nan tasa da duk lokacin da yake larabci ba za ka yi tunanin idan ka yi masa hausa ze ji ba. Cike da farin ciki Lulu kuwa ta nemi wani aji da babu kowa a ciki ta zauna, dama tana sane taƙi zuwa da littafin dan ya koreta. Se kuwa ta zauna abinta inda ta san har ya gama ba za ta jiyo muryarsa ba. Kafin a tashi Gwani ya bar makarantar zuwa asibiti, dan haka se Malam Ahmad ya shigo ya karɓi ajin. Se a lokacin sannan Lulu ta shigo ajin, tana ƙoƙarin ƙarasawa kusa da Didi ta jiyo muryar Malam Ahmad ɗin na faɗin
"Afaaf Muhammad Aji.." se ta dakata sannan ta ɗaga kanta ta kalle shi kana ta amsa da
"Na'am.."
"Daga ina?" Ya tambaya yana kallanta. Dan tsabar shaƙiyanci da rashin kirki irin na Lulu, se ta ɗan yi shiru a ranta tana tuna sunan da ya kamata ta yi amfani da shi ba tare da ta ambaci sunan Gwani ba, dan se take ji kamar ta manta sunan nasa ma, hakan ne ya sanyata faɗin
"Littafi ne ba ni da shi, shi ne ya koreni.."
"Waye..?" Ya sake tambaya. Ji ta yi kamar kawai ta yi wucewarta ba tare da ta amsa masa tambayar ba, se dai ba ta yi hakan ba. Amma kenan yana nufin dole dai se ta faɗi sunan kuma ta fara faɗar wata kalmar girmamawar kafin sunan shi. Duk da baya kusa amma ai mutane suna ji.
"Amma ya aka yi ke Afrah ki ke da shi?" Malam Ahmad ya katseta da faɗin hakan yana kallan Didi. Se da Didi ta sauke ajiyar zuciya sannan cikin niƙab ɗinta ta furta
"Ya mu'allim manta guda ɗaya muka yi a gida." Ɗan numfashi kaɗan ya sauke sannan yace
"Shi kenan, je ki zauna." A hankali ta ƙarasa cikin ajin ta nemi waje ta zauna. Didi ko kallanta ba ta yi ba, dan yau ɗin da gaske ta ji haushin abin da Lulun ke yi sosae.
"Idan Allah ya kai mu anjima, za a je dubiyar mahaifin Malam Affan kamar yanda muka sanar jiya. Waɗanda za su je se su jirani a harabar makaranta." Malam Ahmad ya faɗa. daga nan be wani daɗe ba ya fita daga ajin. Gaba ɗaya en ajin a harabar makarantar suka haɗu, dan kowannensu na son zuwa gaishe da mahaifin Gwanin ko dan kirkinsa a garesu. Se dai ita kam Lulu kallan Didi da har lokacin ba ta kalleta ba ta yi tace
"Bari na je na ɗauki Little mu tafi. Se kun dawo.." da sauri Didi ta kalleta cike da mamakin jin furucinta. "Wai me ke damun Lulun? Anya kuwa kanta ɗaya? Me ye haka take yi kamar wani maƙiyinta ne Gwani? Me yasa ta ɗauki abin da yake mata a matsayin tsana, bayan kullum ita ke janyowa kanta? Fuskarta a haɗe duk da tana cikin niƙab amma Lulu ta fuskanci hakan. Ta kuma sake tabbatar da fushin ne sanda ta soma faɗin
"Wai Lulu me ye haka ne? Abin da kike yi kina ganin daidai ne? Mene ne aibu dan kin je kin duba mahaifinsa ko kuwa za a gutsiri naman jikinki ne?" Ta ƙare tana kallan Lulun.