Sashe 36
A Jini Take Izzata Part 1 Compleete Hausa Novel · about 8 min read
"Abokai ke neman ɓata masa suna. Se dai ban san dalilin da ya sanya suke so ya aikatawa ɗiyarka abin da suke so ya yi ba. Alfarma nake son nema a wajenka.. Don Allah ina so kafin mu bar cikin asibitin nan ka ba ni erka na aurawa yaron nan nawa.." Da sauri Abba ya kalli Alhaji Matawalle yana ji kamar ya yi wani saɓo ne. Cikin mamaki yace
"Aure kuma?".
"Ƙwarai kuwa aure. Tunda muka shigo cikin asibitin nan idan ka lura za ka ga idanun mutane a kanmu yake. Zan yi amfani da wannan damar ne wajen maidawa da munafukai fatan tsiyar da suke mana. Ko da an ɗaura auren ba za a fitar a yau ɗin ba. Se idan wani abun ne ya taso sannan za mu fito mu sanarwa da duniya dama can mata da miji ne. Idan dai har ka sanni ka san yanda nake da maƙiya a cikin garin nan waɗanda ban san dalilinsu na ƙina ba. Su nake tsoro, ɓacin sunan yarinyarka da yarona har ma da namu gaba ɗaya nake tsoro. Dan haka ka yadda a ɗaura auren nan a yau ba se gobe ba.." Har Daddy ya gama wannan bayanin Abba be ce komai ba, dan gaba ɗaya kansa ya kulle. Jin da Daddy ya yi Abba ya yi shiru ne ya sanya shi sake faɗin
"Na san ɗana yana da rashin ji. Se dai na isa da shi.. na kuma yadda ko da ba ɗana ba ne zan iya bawa 'yata aurensa ba wai kuma dan ka yadda ba. A'ah na shaidi ɗana.. Amma na faɗa maka aibunsa, kuma ina fatan idan ya yi aure matar ta chanja min shi. Tun kuma da na ganka na ji hankalina ya kwanta da kai.. Ina kuma da tabbacin kwatankwacin yanda kake haka ɗiyarka ma za ta kasance.." ya ɗan dakata anan sannan ya sake faɗin
"Ka yi duba i zuwa wannan abin alkhairin da muke ƙoƙarin aikatawa. Na farko za mu watsawa maƙiya ƙasa a ido. Na biyu muna ƙoƙarin haɗa aure ne sunnah babba. Sannan na uku daga mu har 'ya'yanmu za mu tsira daga zargin nutane.." Se a lokacin Abba ya sauke ajiyar zuciya sannan yace bayan ya ɗan runtse idanunsa
"Allah ya tabbatar da alkhairi. Idan babu alkhairi ya kawo sanadiyyar wargajewar al'amarin kafin lokacin da za a ɗaura auren.."
"Ameen.." Daddy ya faɗa cikin jin daɗi.
"Se dai wani hanzari ba gudu ba. Ina so a ba ni aron awa ɗaya na je na dawo.."
"Awa ɗaya?" Daddy ya tambaya. Kafin kuma Abban ya amsa yace
"Shi kenan.. Allah ya dawo da kai lafiya.."
"Ameen Ameen.." Abba ya faɗa yana miƙewa ya fice daga ɗakin. Daddy ya ɗan maida dubansa kan Bad cike da tausayawa.
... "Toh na san za ka yi mamakin zuwana bayan na zo ɗazu. Se dai wata muhimmiyar magana ce ta saka ni dawowa, amma ban san yanda za ka ɗauketa ba." Murmushi Abeey ya yi kafin yace
"Babu damuwa, kar ka ji komai ka sanar da ni. Na riga na fahimci maganar na da muhimmanci, dan haka kawai ka sanar da ni." Se da Abba ya sauke ajiyar zuciya sannan yace
"Mun riga mun san cewa iyayen ɗa namiji su ke zuwa neman aure wajen iyayen 'ya mace. Se dai a wannan karon abin ya chanja, duk da mun san hakan ba laifi bane. Ni da kai na na zo neman iri, neman alfarma, neman haɗa iri da kai Malam. Ina neman alfarmar 'yata ta auri ɗanka Affan.."
"Ikon Allah.." Abeey ya faɗa yana jinjina kai. Se kuma ya yi murmushi sannan ya soma faɗin
"In dai har mahaifin yarinya ze nemawa 'yarsa auran wani ɗa, toh lallai tabbas wannan ɗa ya cika ɗa, tunda har uba da kansa ya ga dacewar haɗa ɗiyarsa da shi. Dan haka ina me sake godewa Allah da wannan ni'imar da ya min, wannan ma kaɗai ya isa ya nuna min hankalin Affan ko kuma wasu abubuwan nasa ne suka birgeka har ka ji kana sha'awar haɗa alaƙa da shi. Saboda haka ka kwantar da hankalinka, In Sha Allah wannan ɗin duk ba me wuya bane. Ya ya sunan yarinyar taka?" Cikin matuƙar jin daɗi Abba yace
"Afaaf.. Ɗalibar shi Malam Affan ce.."
"Ikon Allah. Masha Allah, Masha Allah.. gaskiya na ji daɗin wannan al'amari.. Hakan kuma yana nuni da komai ze zo mana cikin sauƙi. Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa.."
"Ameen Ameen. Na gode sosai Malam, Allah ya saka da alkhairi.. Se dai kuma na zo da wata magana ne Malam.."
"Toh ina jinka.." Gyara zama Abba ya yi yana tunanin ta inda ze fara wannan maganar. Se dai kawai ya daure ya soma faɗin
"Wato Malam ina me roƙo da neman alfarmar ɗaura auran a yau ɗin nan idan babu damuwa. Da yake ita yarinyar tana da er uwar tagwaitaka, se auranta ya tashi itama a yau ɗin saboda wani dalili. Hakan ne ya sanya ni tunanin na nemawa er uwarta alfarmar auran Malam Affan saboda ba tun yau ba hankalin yaron ke burge ni Malam. Dan haka nace bari na zo da ƙoƙon barata ko za ka amince ka yadda yau ɗin a haɗa auransu gaba ɗaya.." Shiru Abeey ya yi na tsawon sakanni yana nazarin maganar da Abban ya faɗa. Se can ya sauke Numfashi kafin yace
"A yau yau ɗin za a ɗaura auran ita er uwarta ta?"
"Ehh Malam. Nan da anjima kaɗan.."
"Shi kenan.. Amma bari na fara sanarwa da shi yaron.."
"Toh.." Abba ya faɗa a sanyaye dan yana tunanin idan har Gwani ya ji wadda Abeeyn ze aura masa ba lallai ne ya amince ba. Dan babu wanda ze so aurarwa 'ya'yansa uwa wadda ba ta gari ba. Se dai ya yi hakan ne da zuciya me kyau, yana fatan idan har Gwani ya auri Lulu ya chanjata da ikon Allah. Ya kuma yadda ze aurawa ɗan gidan Matawalle Didi ne saboda itama ta chanja shi, duk da be san yana shan wani abu ba, kamar yadda Daddy ma da kansa be san yana sha ba. Se dai ya fahimci wasu daga cikin halayen nasa. Ya kuma yadda da Didin ɗari bisa ɗari, ya san da yaddar Allah za ta chanja yaron shi ma.
"Ka da fa ka damu. Affan ba ze taɓa cewa a'ah ba. Kawai dai dan na fita haƙƙinsa ne, da kuma na mahaifiyarsa.." Abeey ya faɗa yana kallan Abba da jikinsa ya yi sanyi.
"Toh godiya nake.." Kai tsaye Abeey shigewa ya yi zuwa cikin gidan. Ummeey da ke zaune a ɗaki ya kalla bayan ta amsa sallamar da ya yi.
"A'ah Malam sannu da dawowa.."
"Yawwah.." Abeey ya faɗa yana neman waje ya zauna. Miƙewa Ummeey ta yi da nufin kawo masa ruwa, ya yi saurin katseta da faɗin
"Dawo ki zauna. Magana zamu yi.."
"Toh.." ta faɗa tana komawa ta zauna. Wayarsa Abeey ya ɗakko daga aljihu, ya kamo number Gwani ya kira. Babu jimawa kuwa ya ɗaga. Da ɗan murmushin da idan ka ga ya yi za ka iya tunanin na yaƙe ne, se dai ba na yaƙen bane, haka yake a halittarsa, dan shi ɗin ba shi da wata fara'a a halitta. Se dai wannan murmushin ba ƙaramin kyau yake masa ba. Yace
"Abeeyn Affan.." ya faɗa kamar yanda ya saba faɗa wani lokacin. Murmushi Abeey ya yi kafin yace
"Na'am Affan. Ka na ina ne?"
"Ina wani masallacin ne Abeey. Musabaƙa ake yi, yanzu ma haka an samu er matsala ne, kafin mu koma na ga kiranka.." ya faɗa.
"Toh madallah. Kana dai ji na koh?"
"Ehh Abeey.."
"Na samar maka mata" Abeey ya faɗa. Se ya ɗan yi murmushi, dan ya ɗauka ko zalayar Abeeyn ce da ya saba lokaci zuwa lokaci.
"Tohm Abeey.."
"A wannan karon da gaske nake Affan. Na sama maka mata.."
"Toh na gode. Allah ya ƙara girma.." Gwani ya faɗa a nutse.
"Ameen Ameen. Idan kuma har ka amince toh ina so ne na ɗaura muku aure a yau ɗin nan ba se gobe ba.." Ɗan tsayawa ya yi kamar be ji abin da Abeeyn ya faɗa ba. Dan se ya ji kamar wani wasa. Jin shiru ne ya sanya Abeey faɗin
"Ka na tare da ni Affan?"
"Ehh Abeey.."
"Toh ka amince? Ko kuwa akwai damuwa? Ba a ina nufin damuwar gida da sauran kayayyaki ba a'ah ina magana ne a kan zaɓin da na maka. In dai har ya maka toh kar ka damu.."
"Toh Abeey. Allah ya sa albarka.." Ya faɗa da nutsuwar nan tasa.
"Allah ya yi albarka.. Se ka dawo.." Abeey ya faɗa. Tunda ya fara maganar Ummeey ke kallansa. Ya yi murmushi yana kallanta sannan yace
"Ina fatan kin ji abin da nace koh?"
"Wai kuma Malam kana nufin abin da ka faɗa ɗin?" Se da ya jinjina kai sannan yace
"Ƙwarai kuwa.. yanzu haka ma zan fita na samu uban yarinyar za mu je a ɗaura auren. Kar ki damu kin ji?"
"Ai dole ne na damu Malam.." Ummeey ta faɗa tana girgiza kai.
"Toh ai yanzu so nake ma na ji kema kin ce kin amince.."
"Anya kuwa?" Ummeey ta faɗa.
"Sosai ma kuwa.. Babu damuwa In Sha Allah alkhairi ne kin ji?"
"Toh Allah ya sa.." Ummeey ta faɗa bayan ta sauke ajiyar zuciya. Se a lokacin sannan ya fita daga ɗakin zuwa inda ya bar Abba. Babu ɓata lokaci suka ɗauki hanya zuwa asibitin. Fita suka yi daga asibitin zuwa wani masallaci dake nesa da asibitin bayan sun bar masu kula da marasa lafiyar. Cikin ƙanƙanin lokaci aka tara mutane. Daddy ya bayar da sadakin Didi, yayin da Abeey ma be yi ƙasa a gwuiwa ba wajen fito da kuɗi daidai shi, kuɗaɗen da be daɗe da samun su ba, ya bayar dasu a matsayin sadakin Lulu. Babu ɓata lokaci aka shiga shirye shiryen ɗaurin aure. Cikin lokaci ƙanƙani kuwa aka ɗaura auren AREEF ABUBAKAR MATAWALLE da amayarsa AFRAH MUHAMMAD AJI. Se kuma AFFAN ABUBAKAR AHMAD da amaryarsa AFAAF MUHAMMAD AJI.. (Ƙaƙaƙaraƙaƙa🤭🤐)
... Tunda suka shigo gidan Ammi ke ta duba ɗaki ba ta ji motsin Didi ba.
"Aure kuma?".
"Ƙwarai kuwa aure. Tunda muka shigo cikin asibitin nan idan ka lura za ka ga idanun mutane a kanmu yake. Zan yi amfani da wannan damar ne wajen maidawa da munafukai fatan tsiyar da suke mana. Ko da an ɗaura auren ba za a fitar a yau ɗin ba. Se idan wani abun ne ya taso sannan za mu fito mu sanarwa da duniya dama can mata da miji ne. Idan dai har ka sanni ka san yanda nake da maƙiya a cikin garin nan waɗanda ban san dalilinsu na ƙina ba. Su nake tsoro, ɓacin sunan yarinyarka da yarona har ma da namu gaba ɗaya nake tsoro. Dan haka ka yadda a ɗaura auren nan a yau ba se gobe ba.." Har Daddy ya gama wannan bayanin Abba be ce komai ba, dan gaba ɗaya kansa ya kulle. Jin da Daddy ya yi Abba ya yi shiru ne ya sanya shi sake faɗin
"Na san ɗana yana da rashin ji. Se dai na isa da shi.. na kuma yadda ko da ba ɗana ba ne zan iya bawa 'yata aurensa ba wai kuma dan ka yadda ba. A'ah na shaidi ɗana.. Amma na faɗa maka aibunsa, kuma ina fatan idan ya yi aure matar ta chanja min shi. Tun kuma da na ganka na ji hankalina ya kwanta da kai.. Ina kuma da tabbacin kwatankwacin yanda kake haka ɗiyarka ma za ta kasance.." ya ɗan dakata anan sannan ya sake faɗin
"Ka yi duba i zuwa wannan abin alkhairin da muke ƙoƙarin aikatawa. Na farko za mu watsawa maƙiya ƙasa a ido. Na biyu muna ƙoƙarin haɗa aure ne sunnah babba. Sannan na uku daga mu har 'ya'yanmu za mu tsira daga zargin nutane.." Se a lokacin Abba ya sauke ajiyar zuciya sannan yace bayan ya ɗan runtse idanunsa
"Allah ya tabbatar da alkhairi. Idan babu alkhairi ya kawo sanadiyyar wargajewar al'amarin kafin lokacin da za a ɗaura auren.."
"Ameen.." Daddy ya faɗa cikin jin daɗi.
"Se dai wani hanzari ba gudu ba. Ina so a ba ni aron awa ɗaya na je na dawo.."
"Awa ɗaya?" Daddy ya tambaya. Kafin kuma Abban ya amsa yace
"Shi kenan.. Allah ya dawo da kai lafiya.."
"Ameen Ameen.." Abba ya faɗa yana miƙewa ya fice daga ɗakin. Daddy ya ɗan maida dubansa kan Bad cike da tausayawa.
... "Toh na san za ka yi mamakin zuwana bayan na zo ɗazu. Se dai wata muhimmiyar magana ce ta saka ni dawowa, amma ban san yanda za ka ɗauketa ba." Murmushi Abeey ya yi kafin yace
"Babu damuwa, kar ka ji komai ka sanar da ni. Na riga na fahimci maganar na da muhimmanci, dan haka kawai ka sanar da ni." Se da Abba ya sauke ajiyar zuciya sannan yace
"Mun riga mun san cewa iyayen ɗa namiji su ke zuwa neman aure wajen iyayen 'ya mace. Se dai a wannan karon abin ya chanja, duk da mun san hakan ba laifi bane. Ni da kai na na zo neman iri, neman alfarma, neman haɗa iri da kai Malam. Ina neman alfarmar 'yata ta auri ɗanka Affan.."
"Ikon Allah.." Abeey ya faɗa yana jinjina kai. Se kuma ya yi murmushi sannan ya soma faɗin
"In dai har mahaifin yarinya ze nemawa 'yarsa auran wani ɗa, toh lallai tabbas wannan ɗa ya cika ɗa, tunda har uba da kansa ya ga dacewar haɗa ɗiyarsa da shi. Dan haka ina me sake godewa Allah da wannan ni'imar da ya min, wannan ma kaɗai ya isa ya nuna min hankalin Affan ko kuma wasu abubuwan nasa ne suka birgeka har ka ji kana sha'awar haɗa alaƙa da shi. Saboda haka ka kwantar da hankalinka, In Sha Allah wannan ɗin duk ba me wuya bane. Ya ya sunan yarinyar taka?" Cikin matuƙar jin daɗi Abba yace
"Afaaf.. Ɗalibar shi Malam Affan ce.."
"Ikon Allah. Masha Allah, Masha Allah.. gaskiya na ji daɗin wannan al'amari.. Hakan kuma yana nuni da komai ze zo mana cikin sauƙi. Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa.."
"Ameen Ameen. Na gode sosai Malam, Allah ya saka da alkhairi.. Se dai kuma na zo da wata magana ne Malam.."
"Toh ina jinka.." Gyara zama Abba ya yi yana tunanin ta inda ze fara wannan maganar. Se dai kawai ya daure ya soma faɗin
"Wato Malam ina me roƙo da neman alfarmar ɗaura auran a yau ɗin nan idan babu damuwa. Da yake ita yarinyar tana da er uwar tagwaitaka, se auranta ya tashi itama a yau ɗin saboda wani dalili. Hakan ne ya sanya ni tunanin na nemawa er uwarta alfarmar auran Malam Affan saboda ba tun yau ba hankalin yaron ke burge ni Malam. Dan haka nace bari na zo da ƙoƙon barata ko za ka amince ka yadda yau ɗin a haɗa auransu gaba ɗaya.." Shiru Abeey ya yi na tsawon sakanni yana nazarin maganar da Abban ya faɗa. Se can ya sauke Numfashi kafin yace
"A yau yau ɗin za a ɗaura auran ita er uwarta ta?"
"Ehh Malam. Nan da anjima kaɗan.."
"Shi kenan.. Amma bari na fara sanarwa da shi yaron.."
"Toh.." Abba ya faɗa a sanyaye dan yana tunanin idan har Gwani ya ji wadda Abeeyn ze aura masa ba lallai ne ya amince ba. Dan babu wanda ze so aurarwa 'ya'yansa uwa wadda ba ta gari ba. Se dai ya yi hakan ne da zuciya me kyau, yana fatan idan har Gwani ya auri Lulu ya chanjata da ikon Allah. Ya kuma yadda ze aurawa ɗan gidan Matawalle Didi ne saboda itama ta chanja shi, duk da be san yana shan wani abu ba, kamar yadda Daddy ma da kansa be san yana sha ba. Se dai ya fahimci wasu daga cikin halayen nasa. Ya kuma yadda da Didin ɗari bisa ɗari, ya san da yaddar Allah za ta chanja yaron shi ma.
"Ka da fa ka damu. Affan ba ze taɓa cewa a'ah ba. Kawai dai dan na fita haƙƙinsa ne, da kuma na mahaifiyarsa.." Abeey ya faɗa yana kallan Abba da jikinsa ya yi sanyi.
"Toh godiya nake.." Kai tsaye Abeey shigewa ya yi zuwa cikin gidan. Ummeey da ke zaune a ɗaki ya kalla bayan ta amsa sallamar da ya yi.
"A'ah Malam sannu da dawowa.."
"Yawwah.." Abeey ya faɗa yana neman waje ya zauna. Miƙewa Ummeey ta yi da nufin kawo masa ruwa, ya yi saurin katseta da faɗin
"Dawo ki zauna. Magana zamu yi.."
"Toh.." ta faɗa tana komawa ta zauna. Wayarsa Abeey ya ɗakko daga aljihu, ya kamo number Gwani ya kira. Babu jimawa kuwa ya ɗaga. Da ɗan murmushin da idan ka ga ya yi za ka iya tunanin na yaƙe ne, se dai ba na yaƙen bane, haka yake a halittarsa, dan shi ɗin ba shi da wata fara'a a halitta. Se dai wannan murmushin ba ƙaramin kyau yake masa ba. Yace
"Abeeyn Affan.." ya faɗa kamar yanda ya saba faɗa wani lokacin. Murmushi Abeey ya yi kafin yace
"Na'am Affan. Ka na ina ne?"
"Ina wani masallacin ne Abeey. Musabaƙa ake yi, yanzu ma haka an samu er matsala ne, kafin mu koma na ga kiranka.." ya faɗa.
"Toh madallah. Kana dai ji na koh?"
"Ehh Abeey.."
"Na samar maka mata" Abeey ya faɗa. Se ya ɗan yi murmushi, dan ya ɗauka ko zalayar Abeeyn ce da ya saba lokaci zuwa lokaci.
"Tohm Abeey.."
"A wannan karon da gaske nake Affan. Na sama maka mata.."
"Toh na gode. Allah ya ƙara girma.." Gwani ya faɗa a nutse.
"Ameen Ameen. Idan kuma har ka amince toh ina so ne na ɗaura muku aure a yau ɗin nan ba se gobe ba.." Ɗan tsayawa ya yi kamar be ji abin da Abeeyn ya faɗa ba. Dan se ya ji kamar wani wasa. Jin shiru ne ya sanya Abeey faɗin
"Ka na tare da ni Affan?"
"Ehh Abeey.."
"Toh ka amince? Ko kuwa akwai damuwa? Ba a ina nufin damuwar gida da sauran kayayyaki ba a'ah ina magana ne a kan zaɓin da na maka. In dai har ya maka toh kar ka damu.."
"Toh Abeey. Allah ya sa albarka.." Ya faɗa da nutsuwar nan tasa.
"Allah ya yi albarka.. Se ka dawo.." Abeey ya faɗa. Tunda ya fara maganar Ummeey ke kallansa. Ya yi murmushi yana kallanta sannan yace
"Ina fatan kin ji abin da nace koh?"
"Wai kuma Malam kana nufin abin da ka faɗa ɗin?" Se da ya jinjina kai sannan yace
"Ƙwarai kuwa.. yanzu haka ma zan fita na samu uban yarinyar za mu je a ɗaura auren. Kar ki damu kin ji?"
"Ai dole ne na damu Malam.." Ummeey ta faɗa tana girgiza kai.
"Toh ai yanzu so nake ma na ji kema kin ce kin amince.."
"Anya kuwa?" Ummeey ta faɗa.
"Sosai ma kuwa.. Babu damuwa In Sha Allah alkhairi ne kin ji?"
"Toh Allah ya sa.." Ummeey ta faɗa bayan ta sauke ajiyar zuciya. Se a lokacin sannan ya fita daga ɗakin zuwa inda ya bar Abba. Babu ɓata lokaci suka ɗauki hanya zuwa asibitin. Fita suka yi daga asibitin zuwa wani masallaci dake nesa da asibitin bayan sun bar masu kula da marasa lafiyar. Cikin ƙanƙanin lokaci aka tara mutane. Daddy ya bayar da sadakin Didi, yayin da Abeey ma be yi ƙasa a gwuiwa ba wajen fito da kuɗi daidai shi, kuɗaɗen da be daɗe da samun su ba, ya bayar dasu a matsayin sadakin Lulu. Babu ɓata lokaci aka shiga shirye shiryen ɗaurin aure. Cikin lokaci ƙanƙani kuwa aka ɗaura auren AREEF ABUBAKAR MATAWALLE da amayarsa AFRAH MUHAMMAD AJI. Se kuma AFFAN ABUBAKAR AHMAD da amaryarsa AFAAF MUHAMMAD AJI.. (Ƙaƙaƙaraƙaƙa🤭🤐)
... Tunda suka shigo gidan Ammi ke ta duba ɗaki ba ta ji motsin Didi ba.