Sashe 28
A Jini Take Izzata Part 1 Compleete Hausa Novel · about 8 min read
"A'ah.. zan ɗan ga gari ne.." Murmushi Mom ta yi kafin tace
"Ni wannan fice_ficen duk ba sonsu nake yi ba. Ba dan bana so ka sake yin nisa da ni ba, da nace Daddynka ya sama maka aiki a wata ƙasar, saboda nan ɗin akwai 'ya'yan talakawa sosai da za ka dinga hulɗa dasu.."
"Gaskiya kam, nima ina bayanki Mom. Amma dai mu yi haƙuri da nan ɗin. Abin da za a kiyaye kawai shi ne haɗa shi da 'ya'yan talakawa, wannan kuma aikinki ne tunda mijinki ne.." Aunt Makiyy ta faɗa tana kallan Mom. Jinjina kai Mom ta shiga yi cike da gamsuwa da zancen Aunt Makiyy ɗin, se can ta kalli Bad Man da ba za ka taɓa cewa ya ji abin da suka faɗa ba.
"Ga key nan, idan kun gama hirar se ku kulle min." Ya yi maganar yana nuna key ɗin part ɗin nasa. Daga haka ya soma takawa ze fice
"A'ah Son mu je. Me za mu yi anan ɗin ba ka nan?" Aunt Makiyy ta faɗa tana soma takawa, se Mom ma ta biyo bayanta suka fice daga part ɗin. A compound suka yi sallama sannan ya soma takawa zuwa parking space. Daidai yana ƙoƙarin buɗe motarsa dan shi ba ya buƙatar taimakon kowa, Mommah ma ta ƙaraso wajen sanye cikin wata atamfa me shegen kyau da babban mayafi da ya dace da atamfar. Murmushi ta yi tana jin daɗin ganinsa dan ta daɗe ba ta sanya shi a ido ba. Daddy da ke gefenta sanye cikin wata shadda jamfa da wando ya kalli Bad Man da ya ƙaraso wajensu.
"Barka da wannan lokaci.."
"Barka dai Areef.." suka haɗa baki wajen faɗa, kafin Mommah ta ɗora da
"Ina za ka je ne haka?" Se da ya ɗan saci kallan Daddy kafin cikin basarwa yace
"Ina za ki je? Lem me drop u.."
"A'ah haba, je ka inda za ka ke, ba se ka wahalar da kanka ba driver ze kai ni.." Mommah ta faɗa tana murmushi. Ɗan yamutse fuska ya yi yace bayan ya kai hannunsa ya ɗan shafi gefen kansa
"Babu wani takura fa.. Daddy bari na ajjeta.."
"Kinga Sa'adatu je ki ya kaiki. Ai hakan ya fi.." Murmushi ta sake yi kafin tace
"Tohm shi kenan.. Daddyn Areef bari na je se na dawo.."
"Allah ya tsare.." Daddy ya faɗa, kafin ya maida dubansa kan Bad Man yace
"Pls daga nan ka da ka wuce ko ina.." Murmushin da be shiryawa zuwansa ba shi ne ya ƙwace masa kafin yace
"Ohk.." Daga haka ya shige motar, yayin da Mommah ta shiga wajen me zaman banza kafin ya tada motar. Se a lokacin sannan Daddy ya soma takawa dan komawa ciki cike da nutsuwa gami da kamala a cikin tafiyar tasa.
..."Zo ku zauna nan, tun a ranar ban samu mun yi magana ba se yau.." Abba ya faɗa yana kallan Twins. Babu musu suka nemi waje suka zauna dan ba su san a kan me ma Abban ke magana ba.
"Mun yi magana da shi wancan yaron Kaseem. So ban dai gane takamaimai ma a kan wadda yake magana ba. Afrah ce ko kuma Afaaf?" Abba ya faɗa yana kallansu. Da sauri Didi ta yi ƙasa da kanta cike da kunyar Abban, dan ba ta taɓa tsammanin maganar da ze yi ba kenan.
"Abba wajen Didi fa ya zo.." Lulu ta faɗa tana satar kallan Didi tana ɗan ƙunshe dariyarta. Ammi da ke lura da Didin itama ta yi murmushi tana ɗauke kai.
"Toh ikon Allah.. ke Didi matso nan kusa da ni.." Abba ya faɗa yana yin alama da hannunsa. Cike da kunyar dai ta matso tana sake yin ƙasa da kanta.
"Ki nutsu ki faɗa min kin ji? Yaron da ya zo wajenki da gaske yake aure ze yi, saboda haka za ki faɗa min idan ya yi miki zan san yanda za a yi a tsaida magana, idan ya so kuna gama secondary ɗin nan se a saka rana a ɗaura aure. Saboda haka faɗa min kina son shi?" Kunyar da tafi ta ɗazu ce duk ta sake rufe Didi, se kace wadda ke gaban alƙali ƙirjinta har wani harbawa yake yi.
"Abba.." shi ne abin da ta faɗa kawai har lokacin kanta a ƙasa.
"Assalamu alaikum.." Mami ta yi sallama cikin ɗakin. Dukkansu suka amsa sallamarta ta suna kallan ƙofar. Da gudu Lulu ta miƙe ta faɗa jikinta tana faɗin
"Oyoyo Mamina.." Murmushi Mamin ta yi sannan tace
"Yawwah daughter. Na same ku lafiya?"
"Ehh.." Lulu ta faɗa. Se suka ƙaraso cikin ɗakin, Mami ta nemi waje ta zauna suka gaisa da Abba da kuma Ammi sannan suka ɗan shiga hira kaɗan_kaɗan. Zuwa can Abba ya miƙe saboda lokacin sallah da ya gabato, ya musu sallama ya fice daga ɗakin. Cike da jin daɗi Didi ta miƙe ta tafi ɗakinsu dan dama wannan titsiyen da Abban ya mata gaba ɗaya ta kasa sukuni. Se a lokacin suka ɗan cigaba da hira jefi_jefi da Ammi. Zuwa can wayar Ammi ta shiga ruri, se ta kalli Mamin tace
"Bari na amsa kira.."
"Toh babu damuwa.." Mami ta faɗa tana murmushi. Se ta miƙe da wayar a hannunta ta shiga ɗaki. Se a lokacin Mami ta kalli Lulu da ke kusa da ita ta maka mata harara sannan tace
"Ina wayar da na ba ki?" Buɗe ido Lulu ta yi gami da buɗe baki tana tuna wayar da Mamin ta bata, dan wallahi tun ranar da ta bata ta manta da babinta. Toh aba ce dama da ba ta gabanta.
"Wallahi na manta da ita.." ta faɗa tana tura baki.
"Shashashar yarinya.." Mami ta faɗa tana ɗan dafe kanta. Se kuma can ta ɗaga kai ta kalli Lulun tace
"Kenan ba ku taɓa waya da Kaseem ɗin ba?" Se a lokacin sannan Lulu ta yi murmushi kafin tace
"Albishirinki.." cike da farin ciki Mami tace
"Goro fari tass. Maza faɗa min kuna ta waya koh?"
"Toh ba ni ya gani ba, ashe Didi ya gani ya ɗauka ni ce. Kuma ma ya zo wajen Abba ya kuma zo wajen Didin ma sau biyu.."
"Didi kuma?" Mami ta faɗa cike da mamaki.
"Ehh.." Lulu ta faɗa da murmushin dai. Zuwa can Mami ta sauke ajiyar zuciya tana jinjina kai kafin tace
"Lallai" ta faɗa a kan laɓɓanta tana jinjina kai, kafin ta saki murmushi tana soma tsara yanda komai ze tafi.
.... "So nake na yi mata wani abun da har ta mutu ba za ta taɓa mantawa da shi ba, ba kuma tare da ta san ni ce na aikata mata ba. Dan idan dai har ta sani na san ba za ta dawo wajena neman taimako ba. Dan haka zan yi amfani da dabarata na sakata ta ji dole a wajena ne za ta zo ta samu mafita.." Dariya Abida ta kwashe da ita bayan gama sauraron abin da Ladi ta faɗa kafin tace
"Ina yinki Jakadiyarmu, Allah ya ƙara miki lafiya da kwanya. Kamar me za a yi mata?" Ɗan murmushi Ladi ta yi tana wani jujjuya kai irin ita shegiyar nan ana fasa mata kai kana tace
"Auruwa ne ba na so ta yi, dan idan dai har ta yi aure na san ba za ta taɓa amincewa da buƙatata ba, shi ya sa nake so in yi mata wani abun da za ta kasa auruwa, wanda daga ƙarshe idan ta rasa mafita dole ta dawo wajena" Cike da amincewa da zancen nata Abida ta shiga jinjina kai, dan itama ta daɗe da ƙuluwa da al'amarin Lulu, gwara a yi mata abin da ze tarwatsa wannan ji ji da kan nata da kuma taurin kan da take fama da shi.
"Ta ina za a fara kenan?" Abida ta faɗa tana murmushin jin daɗin yanda a wannan karon Ladin ke zama tana shawara da ita, se dai ta san hakan na da nasaba da kasancewar ita ta kawo Lulun. Amma dai koma menene ita hakan ma ya yi mata daɗi. Shiru na tsawon mintuna Ladi ba tace komai ba, se ƙurawa waje ɗaya idanu da ta yi kamar me nazari. Bayan shafewar wasu mintuna ukun Ladi ta saki wani murmushi tana sauke ajiyar zuciya gami da murza hannunta irin komai ya yi ɗin nan, kafin a fili ta furta
"Hero!!!" Ta faɗa tana sake jinjina kai gami da sakin wani murmushi..
Me son yin payment yanzu kafin mu gama Free pages, ze tura ₦300 ne ta 8124818273, Zahra'u Yusuf Ishaq, Opay. Shedar biya ta 08124818273.
https://chat.whatsapp.com/BClMNPwWybg2n3oRvtemv8
*♡☆A JINI TAKE☆♡*
*(IZZATA)*
By
_*ZARAH MAITAMA (Mhiz Innocent)*_
*CHAPTER ONE*
Page_18
__"Hero!" Abida ta maimaita sunan tana jinjina kai. Ba ta taɓa jin sunan a bakin Ladi ba, ba kuma ta taɓa ganinsa a cikin gidan nan ba. Dan haka maimaita sunan da ta yi tana jira ne ta ji Ladin ta mata ƙarin bayani a kan Hero ɗin. Kamar kuwa Ladin ta gane abin da take so, se ta yi murmushi kafin ta fara faɗin
"Cikin lokaci ƙanƙani kwanyata ta samo min mafita. Ba na buƙatar jigari_jigarin mutum, duk da ko cikin gidan nan ina da yaran da zan iya sakawa su min aiki a kan yarinyar nan. Se dai Hero tantiri ne kuma riƙaƙƙen ɗan duniya na bugawa a jarida. Shi ya dace na saka ya min wannan aikin, na san ze min yadda ya kamata har ma ya ƙara wani abun a kai.." Ladi ta ƙarasa maganar tana miƙewa. Cikin jin daɗi Abida tace
"Gaskiya ne, dama irinsa ya kamata a haɗa wannan shegiyar yarinyar me shegen taurin kai da shi, na san ze gyara mata zama.."
"Me kyan ma kuwa.." in ji Ladi.
... Tana zaune a gaban Kurfoti da ƙaramar tukunya ke kai tana yin miya, ƙamshi me daɗi gaba ɗaya ya cika gidan, dan kuwa Ummeeyn gwana ce wajen iya sarrafa abinci.
"Sannu da aiki.." Abeey da ke kishingiɗe kan dadduma ya faɗa yana murmushi. Itama murmushin ta yi sannan tace
"Yawwah.."
"Ni dai da ina da hali da na samo miki er aiki ta dinga rage miki wasu ayyukan.." Abeeyn ya sake faɗa.
"Ni wannan fice_ficen duk ba sonsu nake yi ba. Ba dan bana so ka sake yin nisa da ni ba, da nace Daddynka ya sama maka aiki a wata ƙasar, saboda nan ɗin akwai 'ya'yan talakawa sosai da za ka dinga hulɗa dasu.."
"Gaskiya kam, nima ina bayanki Mom. Amma dai mu yi haƙuri da nan ɗin. Abin da za a kiyaye kawai shi ne haɗa shi da 'ya'yan talakawa, wannan kuma aikinki ne tunda mijinki ne.." Aunt Makiyy ta faɗa tana kallan Mom. Jinjina kai Mom ta shiga yi cike da gamsuwa da zancen Aunt Makiyy ɗin, se can ta kalli Bad Man da ba za ka taɓa cewa ya ji abin da suka faɗa ba.
"Ga key nan, idan kun gama hirar se ku kulle min." Ya yi maganar yana nuna key ɗin part ɗin nasa. Daga haka ya soma takawa ze fice
"A'ah Son mu je. Me za mu yi anan ɗin ba ka nan?" Aunt Makiyy ta faɗa tana soma takawa, se Mom ma ta biyo bayanta suka fice daga part ɗin. A compound suka yi sallama sannan ya soma takawa zuwa parking space. Daidai yana ƙoƙarin buɗe motarsa dan shi ba ya buƙatar taimakon kowa, Mommah ma ta ƙaraso wajen sanye cikin wata atamfa me shegen kyau da babban mayafi da ya dace da atamfar. Murmushi ta yi tana jin daɗin ganinsa dan ta daɗe ba ta sanya shi a ido ba. Daddy da ke gefenta sanye cikin wata shadda jamfa da wando ya kalli Bad Man da ya ƙaraso wajensu.
"Barka da wannan lokaci.."
"Barka dai Areef.." suka haɗa baki wajen faɗa, kafin Mommah ta ɗora da
"Ina za ka je ne haka?" Se da ya ɗan saci kallan Daddy kafin cikin basarwa yace
"Ina za ki je? Lem me drop u.."
"A'ah haba, je ka inda za ka ke, ba se ka wahalar da kanka ba driver ze kai ni.." Mommah ta faɗa tana murmushi. Ɗan yamutse fuska ya yi yace bayan ya kai hannunsa ya ɗan shafi gefen kansa
"Babu wani takura fa.. Daddy bari na ajjeta.."
"Kinga Sa'adatu je ki ya kaiki. Ai hakan ya fi.." Murmushi ta sake yi kafin tace
"Tohm shi kenan.. Daddyn Areef bari na je se na dawo.."
"Allah ya tsare.." Daddy ya faɗa, kafin ya maida dubansa kan Bad Man yace
"Pls daga nan ka da ka wuce ko ina.." Murmushin da be shiryawa zuwansa ba shi ne ya ƙwace masa kafin yace
"Ohk.." Daga haka ya shige motar, yayin da Mommah ta shiga wajen me zaman banza kafin ya tada motar. Se a lokacin sannan Daddy ya soma takawa dan komawa ciki cike da nutsuwa gami da kamala a cikin tafiyar tasa.
..."Zo ku zauna nan, tun a ranar ban samu mun yi magana ba se yau.." Abba ya faɗa yana kallan Twins. Babu musu suka nemi waje suka zauna dan ba su san a kan me ma Abban ke magana ba.
"Mun yi magana da shi wancan yaron Kaseem. So ban dai gane takamaimai ma a kan wadda yake magana ba. Afrah ce ko kuma Afaaf?" Abba ya faɗa yana kallansu. Da sauri Didi ta yi ƙasa da kanta cike da kunyar Abban, dan ba ta taɓa tsammanin maganar da ze yi ba kenan.
"Abba wajen Didi fa ya zo.." Lulu ta faɗa tana satar kallan Didi tana ɗan ƙunshe dariyarta. Ammi da ke lura da Didin itama ta yi murmushi tana ɗauke kai.
"Toh ikon Allah.. ke Didi matso nan kusa da ni.." Abba ya faɗa yana yin alama da hannunsa. Cike da kunyar dai ta matso tana sake yin ƙasa da kanta.
"Ki nutsu ki faɗa min kin ji? Yaron da ya zo wajenki da gaske yake aure ze yi, saboda haka za ki faɗa min idan ya yi miki zan san yanda za a yi a tsaida magana, idan ya so kuna gama secondary ɗin nan se a saka rana a ɗaura aure. Saboda haka faɗa min kina son shi?" Kunyar da tafi ta ɗazu ce duk ta sake rufe Didi, se kace wadda ke gaban alƙali ƙirjinta har wani harbawa yake yi.
"Abba.." shi ne abin da ta faɗa kawai har lokacin kanta a ƙasa.
"Assalamu alaikum.." Mami ta yi sallama cikin ɗakin. Dukkansu suka amsa sallamarta ta suna kallan ƙofar. Da gudu Lulu ta miƙe ta faɗa jikinta tana faɗin
"Oyoyo Mamina.." Murmushi Mamin ta yi sannan tace
"Yawwah daughter. Na same ku lafiya?"
"Ehh.." Lulu ta faɗa. Se suka ƙaraso cikin ɗakin, Mami ta nemi waje ta zauna suka gaisa da Abba da kuma Ammi sannan suka ɗan shiga hira kaɗan_kaɗan. Zuwa can Abba ya miƙe saboda lokacin sallah da ya gabato, ya musu sallama ya fice daga ɗakin. Cike da jin daɗi Didi ta miƙe ta tafi ɗakinsu dan dama wannan titsiyen da Abban ya mata gaba ɗaya ta kasa sukuni. Se a lokacin suka ɗan cigaba da hira jefi_jefi da Ammi. Zuwa can wayar Ammi ta shiga ruri, se ta kalli Mamin tace
"Bari na amsa kira.."
"Toh babu damuwa.." Mami ta faɗa tana murmushi. Se ta miƙe da wayar a hannunta ta shiga ɗaki. Se a lokacin Mami ta kalli Lulu da ke kusa da ita ta maka mata harara sannan tace
"Ina wayar da na ba ki?" Buɗe ido Lulu ta yi gami da buɗe baki tana tuna wayar da Mamin ta bata, dan wallahi tun ranar da ta bata ta manta da babinta. Toh aba ce dama da ba ta gabanta.
"Wallahi na manta da ita.." ta faɗa tana tura baki.
"Shashashar yarinya.." Mami ta faɗa tana ɗan dafe kanta. Se kuma can ta ɗaga kai ta kalli Lulun tace
"Kenan ba ku taɓa waya da Kaseem ɗin ba?" Se a lokacin sannan Lulu ta yi murmushi kafin tace
"Albishirinki.." cike da farin ciki Mami tace
"Goro fari tass. Maza faɗa min kuna ta waya koh?"
"Toh ba ni ya gani ba, ashe Didi ya gani ya ɗauka ni ce. Kuma ma ya zo wajen Abba ya kuma zo wajen Didin ma sau biyu.."
"Didi kuma?" Mami ta faɗa cike da mamaki.
"Ehh.." Lulu ta faɗa da murmushin dai. Zuwa can Mami ta sauke ajiyar zuciya tana jinjina kai kafin tace
"Lallai" ta faɗa a kan laɓɓanta tana jinjina kai, kafin ta saki murmushi tana soma tsara yanda komai ze tafi.
.... "So nake na yi mata wani abun da har ta mutu ba za ta taɓa mantawa da shi ba, ba kuma tare da ta san ni ce na aikata mata ba. Dan idan dai har ta sani na san ba za ta dawo wajena neman taimako ba. Dan haka zan yi amfani da dabarata na sakata ta ji dole a wajena ne za ta zo ta samu mafita.." Dariya Abida ta kwashe da ita bayan gama sauraron abin da Ladi ta faɗa kafin tace
"Ina yinki Jakadiyarmu, Allah ya ƙara miki lafiya da kwanya. Kamar me za a yi mata?" Ɗan murmushi Ladi ta yi tana wani jujjuya kai irin ita shegiyar nan ana fasa mata kai kana tace
"Auruwa ne ba na so ta yi, dan idan dai har ta yi aure na san ba za ta taɓa amincewa da buƙatata ba, shi ya sa nake so in yi mata wani abun da za ta kasa auruwa, wanda daga ƙarshe idan ta rasa mafita dole ta dawo wajena" Cike da amincewa da zancen nata Abida ta shiga jinjina kai, dan itama ta daɗe da ƙuluwa da al'amarin Lulu, gwara a yi mata abin da ze tarwatsa wannan ji ji da kan nata da kuma taurin kan da take fama da shi.
"Ta ina za a fara kenan?" Abida ta faɗa tana murmushin jin daɗin yanda a wannan karon Ladin ke zama tana shawara da ita, se dai ta san hakan na da nasaba da kasancewar ita ta kawo Lulun. Amma dai koma menene ita hakan ma ya yi mata daɗi. Shiru na tsawon mintuna Ladi ba tace komai ba, se ƙurawa waje ɗaya idanu da ta yi kamar me nazari. Bayan shafewar wasu mintuna ukun Ladi ta saki wani murmushi tana sauke ajiyar zuciya gami da murza hannunta irin komai ya yi ɗin nan, kafin a fili ta furta
"Hero!!!" Ta faɗa tana sake jinjina kai gami da sakin wani murmushi..
Me son yin payment yanzu kafin mu gama Free pages, ze tura ₦300 ne ta 8124818273, Zahra'u Yusuf Ishaq, Opay. Shedar biya ta 08124818273.
https://chat.whatsapp.com/BClMNPwWybg2n3oRvtemv8
*♡☆A JINI TAKE☆♡*
*(IZZATA)*
By
_*ZARAH MAITAMA (Mhiz Innocent)*_
*CHAPTER ONE*
Page_18
__"Hero!" Abida ta maimaita sunan tana jinjina kai. Ba ta taɓa jin sunan a bakin Ladi ba, ba kuma ta taɓa ganinsa a cikin gidan nan ba. Dan haka maimaita sunan da ta yi tana jira ne ta ji Ladin ta mata ƙarin bayani a kan Hero ɗin. Kamar kuwa Ladin ta gane abin da take so, se ta yi murmushi kafin ta fara faɗin
"Cikin lokaci ƙanƙani kwanyata ta samo min mafita. Ba na buƙatar jigari_jigarin mutum, duk da ko cikin gidan nan ina da yaran da zan iya sakawa su min aiki a kan yarinyar nan. Se dai Hero tantiri ne kuma riƙaƙƙen ɗan duniya na bugawa a jarida. Shi ya dace na saka ya min wannan aikin, na san ze min yadda ya kamata har ma ya ƙara wani abun a kai.." Ladi ta ƙarasa maganar tana miƙewa. Cikin jin daɗi Abida tace
"Gaskiya ne, dama irinsa ya kamata a haɗa wannan shegiyar yarinyar me shegen taurin kai da shi, na san ze gyara mata zama.."
"Me kyan ma kuwa.." in ji Ladi.
... Tana zaune a gaban Kurfoti da ƙaramar tukunya ke kai tana yin miya, ƙamshi me daɗi gaba ɗaya ya cika gidan, dan kuwa Ummeeyn gwana ce wajen iya sarrafa abinci.
"Sannu da aiki.." Abeey da ke kishingiɗe kan dadduma ya faɗa yana murmushi. Itama murmushin ta yi sannan tace
"Yawwah.."
"Ni dai da ina da hali da na samo miki er aiki ta dinga rage miki wasu ayyukan.." Abeeyn ya sake faɗa.