Sashe 9
Yar Gwagwarmaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun a ranar Baffa ya mallaki bindiga da harsasai ba adadi. Ya hana kansa sukuni ya koma kamar wani zararre. Ba abinda yake sai yawo a cikin garin ko-wane bangare bi yake, ba tare da ya san inda zai ganta ba. Haka dare ya riske shi, dole ba dan ya so ba ya kama hanyar asibitin da Abbansu yake.
Sai dai kafin ya kai ga isa asibitin shima ya fada tarkon 'yar gwa-gwarmaya. Fadwa cikin shigar nan tata ta dare as usual. Ta tare hanya a matsayin jami'ar tsaro ta cafke shi da laifin mallakar makami ba bisa ka'ida ba. Sannan ta nufi gidanta da shi a madadin ofishin 'yan sanda. A ransa yana mamakin wannan jami'ar tsaron da ba a iya ganin fuskarta. Bangare daya kuma cewa yake ko ma wace ce su je. Ya san ai dole za'a sake shi ne.
🤔 Babbar magana.
*Keep following...*
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
```page 14```
Ranar litinin da sassafe aka tashi da rudanin rashin ganin Baffa. "Wannan wane irin al'amari ne? Alhaji me ka tarewa yarinyar nan ne? Don Allah ka taimake ni ban ga Baffa ba. Kar ace shima ta raba ni da shi". Hajiya Laurat ce mai wadannan maganganun cikin kuka tana zune gaban gadon da Alhaji Habib yake kai. Hankalinsa ya koma tashi, kamar wanda aka tsikara haka ya mike zumbur ya tashi daga gadon asibitin yana mai fiz-fizge robar karin ruwa dake makale a hannunsa.
"Wace irin magana kike haka, ina Baffan ya tafi?". Cikin matsanancin kuka tace "ban sani ba, shima dai fita yayi tun safiyar jiya bamu koma sa shi a ido ba".
"Haba inah! Abin ya isa haka kuma, wallahi ba wanda ya isa ya ga bayana ni Habib, sai dai mu ga bayan juna. Kamar ni za..." Karar wayarsa dake ajiye a gefen gadon da ya tashi, ita ce ta katse shi. Hajiya Laurat ta dauko da sauri ta duba ko zata ga sunan danta. Amma sai ta ga (null) boyayyiyar lamba. Hannunta na rawa ta mika masa. Ya karba yana ganin number ya gaggauta danna receive.
Kaifin ta yi magana shi ne ya fara. "Ke "yar gidan marasa mutunci, ina dana yake?". Fadwa ta lumshe lumsassun idonta fuskarta dauke da murmushi. Amma a kasan zuciyarta ta ji zafin zagin da ya dannawa iyayenta. Sai dai yanayin tashin hankalin da ta ji shi a ciki ya fi mata komai dadi a duniyar nan. Ta bude idanunta a hankali sannan ta fara magana "gud Alhajina. Na ji dadin da ka yi saurin gano danka yana hannuna. Na tabbata daga yau zaka fara killace kayanka saboda tsoron Fadwa. Ina so ka haddace daga yau duk abinda ka nema baka gani ba ka neme shi a gurin Fadwa. Daga karshe ina maka albishir Shugaba. Lokacin bakin cikinka ya soma. Wutar 'Yar gwa-gwarmaya ta fara cin abinda ka mallaka kenan har zuwa lokacin da zaka bayyanawa duniya asalin gaskiyarka. Dole mutanen nan su san boyayyiyar fuskarka. Na barka lafiya Shugaba... Am... Ka ga na manta fa, danka yace yana gaisheka, ni kuma har yanzu ina kan tunani ne. Idan na gama yanke yaddda zan yi da shi zan gaya maka".
Tana kokarin yanke wayar Hajiya Laurat dake sauraronsu tayi wuf ta fizge wayar ta kanga a kunnenta. Muryarta har rawa take ta fara magana cikin kuka. "Dakata mana 'yar nan, dan Allah ki yi min rai ki dawo min da dana. Na san kema 'ya ce kuma uwa a wata rana, ki tuna abinda ke tsakanin'yaya da iyayensu 'yar nan..." Sai kuka ya kwace mata.
Jin matar na neman karyar mata da zuciya yasa ta katse wayar, sannan ta zube bisa kujerar dake kusa da ita. Ruf! Ta rufe idonta tana maida numfashi. "Hakika duk wanda ya san darajar iya da abinda ke tsakaninsu da 'ya yensu a bayana yake Hajiya. Ki sani saboda wannan kaunar ta iyaye nake fafutuka. Domin sharewa iyayen da ake fandarar musu da 'ya yansu hawaye. Na sani ke uwa ce. Amma mijinki azzalumin uba ne. Kuma na rantse ba zan bar shi ba".
A fili take maganar cikin zafi kamar tana gaban Hajiyar ne. "Mene ne Fadwa?". Ab'ha ya dake gefenta ya tambaya. Bata ce komai ba ta mike ta nufi dakin da ta kulle Baffa a daren jiya.
Shugaba da ya zama kamar zararre ya kalli matarsa dake rike da waya a hannu tana rusa kuka. Yace "ki kwantar da hankalin...". Bai karasa ba ta katse shi "a a, kar ka bata bakinka da lokacinka, ka sani babu wata kalmar rarrashi da zata isarwa uwar da ta rasa danta muddun ba mutuwar Allah ce ta dauke shi ba. Ba zan iya hakura ba Alhaji, kuma hankalina ba zai taba kwanciya a wannan takin ba".
Shugaba kam ya fara rasa tunaninsa sai zare ido yake, ya ma rasa wata kalma da zai koma furta mata. Can ya tsinkayo muryarta ta ci gaba da magana cikin kuka
"Ni wallahi na ma fara zarginka, ina ji a raina wanda aka cuta ne kadai zai iya aikata wadan-nan abubuwa da yarinyar nan take. In ko da laifinka a sanadin lalata rayuwar 'yata ba zan taba yafe maka b..."
Saukar wani mahaukacin mari da ta ji a kuncinta, shi ya hana ta cikata kalmominta. Ta dafe kunci tana kallonsa cike da mamaki da tsoro.
Cikin karfin hali da 'korewa irin ta mai son faranta kansa, ya fara magana cikin masifa. "Lauratu ashe baki da hankali ban sani ba? Ashe za'a wayi gari ki zarge ni da kanki? Tabbas kuwa mace ba adila bace. Duk duniyar nan babu wanda ya san sirrina sama da ke. Babu wanda ya fi ki kusanci da ni. Amma yau da bakinki kike neman yarda da buyagin makiyana. Kike cewa kina zargina... Ya jijjiga kai, cike da alamar tsabar takaici. Sannan ya dora ...to ke da duk mai bi na da sharri Allah ya fi ku".
Ya fizgi jiki ya fice daga dakin a fusace.
Hajiya Laurat jikinta ya yi sanyi sosai. Sai a lokacin take jin lallai bata kyauta ba, soyayyar 'yaya ce kai ta ga barin hayyaci har take kokarin saka zargi ga adalin mijinta. Nan da nan ta shiga istigfari tana tubarwa Allah. Shugaba kuwa wayar ma a hannunta ya bar ta balle ta yi yunkurin kiransa.
Sannu a hankali ta kai hannunta ga handle na kofar ta mirda bayan ta murza key. Jin an bude kofar yasa ya dago da idanunsa da suka gama rinewa ya zuba ma mai shigowar.
Ras! Ya ji gabansa ya yi wani mugun faduwa a lokacin da suka yi ido biyu da ita. Sanye take da doguwar riga dikin gown, ta wani lallausan yadi ja mai ratsin fari. Ba dan-kwali a kanta sai lallausan gashin kanta da ya sha gyara irin na turawa. Kana-nan 'yankunne ne makali a jikin fari kuma kakkyawan kunnenta. Kalar fatarta chocolate ce mai dauke da sirruka. Duk da cewa babu wata kwalliya a fuskar nan ta'ta, amma ba abinda take sai sheki da daukar ido.
Ya kasa kauda idonsa ga barin kallonta, tun da ya mallaki hankalinsa bai taba ganin macen da komai nata ya burge shi farat daya kamar na wannan dake gabansa ba. A ransa yace "tsarki ta tabbata ga mahaliccin wannan kakkyawar halittar". Ya dauke kansa dakyar, zuciyarsa na raya masa ya samu abinda shi da iyayensa suka dade suna nema wato matar aure. Babu shakka wannan 'yar sanda ta tafi da imaninsa...
Bai kai karshe ga maganar zucinsa ba ta katse shi. "Kai karamin mara kunya, shin ka san inda kake kuwa?". Baffa cikin sanyin muryar da shi kansa bai san yana da shi ba yace "ranki ya dade, na san ina hannun jami'an tsaro ne".
Fadwa ta fashe da muguwar dariyar nan ta'ta mai ban haushi ga wanda ya san manufarta tace "shakka babu uban da 'yayan duka kwakwalen jakai ne da su". Maganar ta tunzura Baffa kasancewarsa mai saurin daukar zafi. Sai dai sanin muhimmancin wadda yake maganar da ita a zuciyarsa yasa ya danne "ban gane me kike nufi ba". Ya bukaci karin bayani. Ta girgiza kai "yaro, yaro ne. A yadda naga zafinka a gidan TV sam ban kawo haka zaka yi sanyi a gaban abin nemanka 'yar gwa-gwarmaya ba".
Maganar ta saukar masa kamar almara. Kansa ya buga da karfi, lokaci daya tare da ziciyarsa. Ya kura mata ido yana neman gasgata abinda ta fada. Kasancewar duka video da ta sake babu fuskarta sai dai murya. Tabbas ita ce. Yanzu muryar take dawo mishi.
Cikin karaji da matsanancin zafin bacin rai ya zaburo mata...
Zan ci gaba.
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
*Alhamdulillah na ji dadi na kuma gode da yawan comments da privete test naku a kan wannan labarin. Hakika kuna karawa Nasmat kwarin guiwa matuka. Ku ci gaba da bibiya ni kuma cikin farin ciki zan ci gaba da antayo muku shi.*
~The great gift in this life is a *love* and *care*. U guys give all those to me. I hav no one like u my fans keep following~ 🤝
```page 15```
Sai dai kafin ya kai ga isa asibitin shima ya fada tarkon 'yar gwa-gwarmaya. Fadwa cikin shigar nan tata ta dare as usual. Ta tare hanya a matsayin jami'ar tsaro ta cafke shi da laifin mallakar makami ba bisa ka'ida ba. Sannan ta nufi gidanta da shi a madadin ofishin 'yan sanda. A ransa yana mamakin wannan jami'ar tsaron da ba a iya ganin fuskarta. Bangare daya kuma cewa yake ko ma wace ce su je. Ya san ai dole za'a sake shi ne.
🤔 Babbar magana.
*Keep following...*
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
```page 14```
Ranar litinin da sassafe aka tashi da rudanin rashin ganin Baffa. "Wannan wane irin al'amari ne? Alhaji me ka tarewa yarinyar nan ne? Don Allah ka taimake ni ban ga Baffa ba. Kar ace shima ta raba ni da shi". Hajiya Laurat ce mai wadannan maganganun cikin kuka tana zune gaban gadon da Alhaji Habib yake kai. Hankalinsa ya koma tashi, kamar wanda aka tsikara haka ya mike zumbur ya tashi daga gadon asibitin yana mai fiz-fizge robar karin ruwa dake makale a hannunsa.
"Wace irin magana kike haka, ina Baffan ya tafi?". Cikin matsanancin kuka tace "ban sani ba, shima dai fita yayi tun safiyar jiya bamu koma sa shi a ido ba".
"Haba inah! Abin ya isa haka kuma, wallahi ba wanda ya isa ya ga bayana ni Habib, sai dai mu ga bayan juna. Kamar ni za..." Karar wayarsa dake ajiye a gefen gadon da ya tashi, ita ce ta katse shi. Hajiya Laurat ta dauko da sauri ta duba ko zata ga sunan danta. Amma sai ta ga (null) boyayyiyar lamba. Hannunta na rawa ta mika masa. Ya karba yana ganin number ya gaggauta danna receive.
Kaifin ta yi magana shi ne ya fara. "Ke "yar gidan marasa mutunci, ina dana yake?". Fadwa ta lumshe lumsassun idonta fuskarta dauke da murmushi. Amma a kasan zuciyarta ta ji zafin zagin da ya dannawa iyayenta. Sai dai yanayin tashin hankalin da ta ji shi a ciki ya fi mata komai dadi a duniyar nan. Ta bude idanunta a hankali sannan ta fara magana "gud Alhajina. Na ji dadin da ka yi saurin gano danka yana hannuna. Na tabbata daga yau zaka fara killace kayanka saboda tsoron Fadwa. Ina so ka haddace daga yau duk abinda ka nema baka gani ba ka neme shi a gurin Fadwa. Daga karshe ina maka albishir Shugaba. Lokacin bakin cikinka ya soma. Wutar 'Yar gwa-gwarmaya ta fara cin abinda ka mallaka kenan har zuwa lokacin da zaka bayyanawa duniya asalin gaskiyarka. Dole mutanen nan su san boyayyiyar fuskarka. Na barka lafiya Shugaba... Am... Ka ga na manta fa, danka yace yana gaisheka, ni kuma har yanzu ina kan tunani ne. Idan na gama yanke yaddda zan yi da shi zan gaya maka".
Tana kokarin yanke wayar Hajiya Laurat dake sauraronsu tayi wuf ta fizge wayar ta kanga a kunnenta. Muryarta har rawa take ta fara magana cikin kuka. "Dakata mana 'yar nan, dan Allah ki yi min rai ki dawo min da dana. Na san kema 'ya ce kuma uwa a wata rana, ki tuna abinda ke tsakanin'yaya da iyayensu 'yar nan..." Sai kuka ya kwace mata.
Jin matar na neman karyar mata da zuciya yasa ta katse wayar, sannan ta zube bisa kujerar dake kusa da ita. Ruf! Ta rufe idonta tana maida numfashi. "Hakika duk wanda ya san darajar iya da abinda ke tsakaninsu da 'ya yensu a bayana yake Hajiya. Ki sani saboda wannan kaunar ta iyaye nake fafutuka. Domin sharewa iyayen da ake fandarar musu da 'ya yansu hawaye. Na sani ke uwa ce. Amma mijinki azzalumin uba ne. Kuma na rantse ba zan bar shi ba".
A fili take maganar cikin zafi kamar tana gaban Hajiyar ne. "Mene ne Fadwa?". Ab'ha ya dake gefenta ya tambaya. Bata ce komai ba ta mike ta nufi dakin da ta kulle Baffa a daren jiya.
Shugaba da ya zama kamar zararre ya kalli matarsa dake rike da waya a hannu tana rusa kuka. Yace "ki kwantar da hankalin...". Bai karasa ba ta katse shi "a a, kar ka bata bakinka da lokacinka, ka sani babu wata kalmar rarrashi da zata isarwa uwar da ta rasa danta muddun ba mutuwar Allah ce ta dauke shi ba. Ba zan iya hakura ba Alhaji, kuma hankalina ba zai taba kwanciya a wannan takin ba".
Shugaba kam ya fara rasa tunaninsa sai zare ido yake, ya ma rasa wata kalma da zai koma furta mata. Can ya tsinkayo muryarta ta ci gaba da magana cikin kuka
"Ni wallahi na ma fara zarginka, ina ji a raina wanda aka cuta ne kadai zai iya aikata wadan-nan abubuwa da yarinyar nan take. In ko da laifinka a sanadin lalata rayuwar 'yata ba zan taba yafe maka b..."
Saukar wani mahaukacin mari da ta ji a kuncinta, shi ya hana ta cikata kalmominta. Ta dafe kunci tana kallonsa cike da mamaki da tsoro.
Cikin karfin hali da 'korewa irin ta mai son faranta kansa, ya fara magana cikin masifa. "Lauratu ashe baki da hankali ban sani ba? Ashe za'a wayi gari ki zarge ni da kanki? Tabbas kuwa mace ba adila bace. Duk duniyar nan babu wanda ya san sirrina sama da ke. Babu wanda ya fi ki kusanci da ni. Amma yau da bakinki kike neman yarda da buyagin makiyana. Kike cewa kina zargina... Ya jijjiga kai, cike da alamar tsabar takaici. Sannan ya dora ...to ke da duk mai bi na da sharri Allah ya fi ku".
Ya fizgi jiki ya fice daga dakin a fusace.
Hajiya Laurat jikinta ya yi sanyi sosai. Sai a lokacin take jin lallai bata kyauta ba, soyayyar 'yaya ce kai ta ga barin hayyaci har take kokarin saka zargi ga adalin mijinta. Nan da nan ta shiga istigfari tana tubarwa Allah. Shugaba kuwa wayar ma a hannunta ya bar ta balle ta yi yunkurin kiransa.
Sannu a hankali ta kai hannunta ga handle na kofar ta mirda bayan ta murza key. Jin an bude kofar yasa ya dago da idanunsa da suka gama rinewa ya zuba ma mai shigowar.
Ras! Ya ji gabansa ya yi wani mugun faduwa a lokacin da suka yi ido biyu da ita. Sanye take da doguwar riga dikin gown, ta wani lallausan yadi ja mai ratsin fari. Ba dan-kwali a kanta sai lallausan gashin kanta da ya sha gyara irin na turawa. Kana-nan 'yankunne ne makali a jikin fari kuma kakkyawan kunnenta. Kalar fatarta chocolate ce mai dauke da sirruka. Duk da cewa babu wata kwalliya a fuskar nan ta'ta, amma ba abinda take sai sheki da daukar ido.
Ya kasa kauda idonsa ga barin kallonta, tun da ya mallaki hankalinsa bai taba ganin macen da komai nata ya burge shi farat daya kamar na wannan dake gabansa ba. A ransa yace "tsarki ta tabbata ga mahaliccin wannan kakkyawar halittar". Ya dauke kansa dakyar, zuciyarsa na raya masa ya samu abinda shi da iyayensa suka dade suna nema wato matar aure. Babu shakka wannan 'yar sanda ta tafi da imaninsa...
Bai kai karshe ga maganar zucinsa ba ta katse shi. "Kai karamin mara kunya, shin ka san inda kake kuwa?". Baffa cikin sanyin muryar da shi kansa bai san yana da shi ba yace "ranki ya dade, na san ina hannun jami'an tsaro ne".
Fadwa ta fashe da muguwar dariyar nan ta'ta mai ban haushi ga wanda ya san manufarta tace "shakka babu uban da 'yayan duka kwakwalen jakai ne da su". Maganar ta tunzura Baffa kasancewarsa mai saurin daukar zafi. Sai dai sanin muhimmancin wadda yake maganar da ita a zuciyarsa yasa ya danne "ban gane me kike nufi ba". Ya bukaci karin bayani. Ta girgiza kai "yaro, yaro ne. A yadda naga zafinka a gidan TV sam ban kawo haka zaka yi sanyi a gaban abin nemanka 'yar gwa-gwarmaya ba".
Maganar ta saukar masa kamar almara. Kansa ya buga da karfi, lokaci daya tare da ziciyarsa. Ya kura mata ido yana neman gasgata abinda ta fada. Kasancewar duka video da ta sake babu fuskarta sai dai murya. Tabbas ita ce. Yanzu muryar take dawo mishi.
Cikin karaji da matsanancin zafin bacin rai ya zaburo mata...
Zan ci gaba.
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
*Alhamdulillah na ji dadi na kuma gode da yawan comments da privete test naku a kan wannan labarin. Hakika kuna karawa Nasmat kwarin guiwa matuka. Ku ci gaba da bibiya ni kuma cikin farin ciki zan ci gaba da antayo muku shi.*
~The great gift in this life is a *love* and *care*. U guys give all those to me. I hav no one like u my fans keep following~ 🤝
```page 15```