← Book details Yar Gwagwarmaya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 23

Sashe 2

Yar Gwagwarmaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shugaba. Habib ya mike tsaye lokaci daya gumi ya shiga yanko masa. "Wane irin sakaci kuka yi haka Sauwam? Ka kuwa san hatsarin dake tattare da Fadwa? Ku taimaka min mana. Yarinyar nan nema take ta bata min suna. Nema take ta wargaza rayuwar siyasata fa." Asp Sauwam yace "kwantar da hankalinka Alh. Fadwa ba zata gagare mu ba. Da iznin Allah nan bada dadewa ba zata shiga hannu. Ka huta gajiya."

Ya katse wayar, ya bar Alh. Habib rike da wayar yana saka da war-wara. Kai tsaye ya shiga laluben wata number a cikin wayar tashi, ya danna kira.

Ringing biyu a na uku aka daga. "Allah ya kama ma Shugaba." Aka fada a can inda ya kira din. "Amin amin Chaka. Kana ji na. Wannan ja'irar yarinyar tana Najeriya. Tana nan cikin Kano. Abinda nake so da kai maza ka baza yaranka kaima ka kutsa kai. Lungu da sako, ku nemo Fadwa kuma ku kashe ta."

Wanda aka kira da Chaka ya amsa da "an gama Alh. Ina gaya maka in dai muka yi arba da Fadwa sai dai gawarta." Alh. Habib ya hangame baki, farin ciki ya lullube shi yace "zan kuwa cika maka burukan rayuwarka Chaka...".

Ya kashe wayar sannan ya kira Aysha wadda ya kawo Senegal. Dan a yadda yake ji bai kamata ya koma kwana a kasar ba. Duk da akwai masu bukatar yarinyar da yawa. Saboda muhimmancin maganar Fadwa, yana da kyau ace yana kusa. Har wayar ta yanke bata daga ba. Ya ja tsaki yana fadin "wan-can shegen baya da sauki, har yanzu bai bar yarinyar nan ba?".

Haka dai ya yi ta zariyar kiran layin Aysha har dare. Bayan ya kira waya airport an yi musu komai na tafiya zasu bi jirgin sha dayan daren. (Ka ji manya)

Karfe tara da rabi, Okeke ya dawo masa da Aysha bayan ya yi mata ragas. Dakyar take tafiya. Ya kalli bakin mutumin yana bata rai yace "amma fa baka kyauta ba. Me yasa zaka yi mata haka? Ka kuwa san asarar da ka yi mini? Yanzu fa sai ta dauki lokaci kafin ta koma aiki."

Okeke ya hangame baki "sorry Alh. Yarinyar ce da a kwai sweet. Zan baka kudin jinyarta daban, kuma na yi bunking a dawo min da ita karshen wata mai zuwa." Take a wajen ya tura masa makudan kudi a account dinsa. Alh. Habib ya bashi bannu suka gaisa, sannan Okeken ya fita yana shafa fuskar Aysha.

To fa 🤔

*Shin Ina bakin zaren yake? Wane ne Alh. Habib Shugaba? Wace irin kiyayya ce tsakanin shi da Fadwa? Wace ce Fadwa? Mene ne burinta? A kan me take gwa-gwarmaya? Ku biyo Nasmat a shafi na gaba.*

*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)

🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀

👨🏻‍💻👩🏻‍💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.
_____________________________________

©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________

```Ina kaunarki``` Kanwata *Amina Auta.* ```kina raina kema``` *Maryam 'Yar Mama* ```ban manta da ke ba``` *Baby Maryam* love you fiye da tunaninku. 😍

```Sadaukarwa ga``` *Mom Heebah* ```fatan alkhairi gareki 'yar uwa. Nasmat na tare da ke. Addu'ata a kullum ita ce Allah ya bawa Babynmu lafiya.``` 🙏

```page 3```

*Alh. Habib Inuwa (Shugaba).* Haifaffen Jihar Kano ne. Cikakken mai kudi, kuma sanannen dan kasuwa. Wanda ake damawa da shi a bangaren siyasar Kasa. Shi ba mai mulki bane, sai dai shi ne yake nada shuwagabanni. A gaba daya kasar girmamashi ake. Ana mutuntashi, duk wanda ya gabatar a matsayin wanda za a zaba, ba makawa shi zai yi mulki. Alh. Habib yana da mata daya Laurat da yaranta uku. Abdul Aziz (Baffa) shi ne babba sai kaninshi Faisal. Sai kuma autarsu Anisa. Wadan-nan yaran 'yan gata ne gaba da baya, wadan-da basa neman abu su rasa. Masu galihu, masu yin abinda suke so. Mahaifinsu ne ya daure musu gindin yin hakan. Domin a cewarsa idan yana da kudi 'ya yansa basu sake ba to babu amfanin kudin kenan. Yana da yawan kyauta da sadaka. Yana yawan dibar talakawa da 'ya yansu ya biya musu Hajji. Su je saudiyayya su sauke farali. Wasu lokutan kuma ya dibi kana-nan 'yan mata wadan-da suka gama sakandire, ya tura su manyan kasashen duniya da sunan ci gaba da karatu. Wadan-nan halayen nashi ba karamin kima da daraja suke kara mishi a idon al'uma ba. Musamman talakawa. Kasancewar duk wadan-da yake yiwa hidimar su da 'ya yansu ne.

Sai dai a bangare daya Alh. Habib babban azzalumi ne. Makirin mutum, mai fuska biyu. Maha'inci, wanda ya maida 'ya yan talakawa da marayu jarin kasuwancinsa. Ya yarda da safarar 'yan mata sosai, dan yana saurin kawo kudi. Hakan yasa ya maida abin Sana'a. Yana fidda su manyan kasashe da sunan aiki ko ci gaba da karatu. Amma da an je can sai ya tilasta su yin karuwanci. Kudin wahalarsu kuma su dira a asusun ajiyarsa. Kasashen turawa da larabawa suna matukar so da kwadayin bakaken mata, 'yan afrika. Hakan yasa ya dage da tallata hajarsa a kasashen. Kasuwar kuma tana ci sosai. Yana aikin ne cikin hikima da kwarewa. Sam baya barin wata shaida wadda zata bayyana shi a matsayin mai hannu a cikin wannan badakalar.

Hakan ya sa koda zarginsa ba wanda ya taba yi. Sai kwatsam a cikin ja'jibe-ja'jibensa ya ja'jibo ruwan dafa kansa. *Fadwa!* Marainiya Fadwa!!.

Tun daga lokacin rayuwar shi ta shiga rudu. Sirrin da ya shafe shekaru yana binnewa yake neman fallasa. Mutuncin da kasarsa da talakawanta suke ganin shi da shi yake neman zubewa. Ya tabbata idan burin Fadwa ya cika ta fallasa shi, rayuwarsa ma ba lallai bane ya tsira da ita.

Wannan kenan.

*Wace ce Fadwa?*
Itama dai a Kano aka haife ta. Kuma ta zo ne a jerin 'ya yan nan wadan-da basu da takamai-man wanda zasu kira da nasu. A gidan marayu ta tsinci kanta, bayan an reneta tun daga jarintaka. Da aka tsince ta yashe a gefen hanya.

Uwar rikonta ita ce Amina wadda take kira Ummy ita ce ta rene ta tun daga kurciya har girma. Amina macen kirki, mai fara'a da nutsuwa. A karkashin kulawarta Fadwa ta sami cikakkiyar tarbiyya. Wadda ko wadan-da suke gaban iyayensu ba kasafai suke samun irinta ba. Soyayyar dake tsakanin Fadwa da Ummynta soyayya ce kwatankwacin wadda ke tsakanin 'ya ya, da iyayensu.

Nagartacciyar yarinya mai kaifin basira da kwazon karatu. Cikin nasara da saka rai ga ci gaba, ta kammala jarrabawarta ta karshe a babbar sakandire ta gwamnati. A shekarar ma kamar yanda ya saba yaudarar mutane Alh. Habib Inuwa Shugaba, ya sanar da daukar nauyin karatun dalibai mata goma a kasar waje. Marayu da 'ya yan talakawa marasa karfi. A cikinsu ne hukumar makarantar suka saka sunan Fadwa, saboda kwazo da dagewarta ga karatu.

Bayan fitowar sakamako aka fara shirye-shiryen tafiyar 'yan makaranta kasar waje. Allah sarki Fadwa a lokacin duk abokanin tafiyarta farin ciki suke, amma ita kuka take yi. Ba dan ta san wani abu game da tafiyar ba, a'a kukanta na rabuwa da Uwa ne. Wadda take ji kamar mahaifiya, Ummy. Ita ce wadda ta kara karfafa mata guiwa ga tafiyar. Ba dan ta so ba, ranar wata jumu'a jirginsu ya tashi zuwa kasar England. A inda aka ce an gama yi musu bunking na komai game da karatunsu.

Satinsu biyu a wani Hotel ana basu horo game da yadda zasu rika saka kayan turawa da kuma amfani da kayan kwalliya. Al'amarin da ya yi matukar daure kan daliban. Basu kara tsurewa ba sai lokacin da aka tilasta su yin ado, suka saka wasu dangalallun kaya masu kama da tsirara. Aka dauke su hotuna. Da wadan-nan hotunan aka tallata su a kasuwar kana-nan 'yan mata masu budurci a jiki. Nan da nan aka fara zuba daloli a kan su. Basuda labari ana can ana cinikinsu kamar wata haja. Bayan an karbi kudadensu ne aka debo su, aka danka ko wace a hannun wanda ya biya kudi mafi daraja a kanta.

Nan fa hankulan 'yan matan suka yi mummunan tashi. Babu yadda suka iya, a wannan ranar aka raba dukkaninsu da rigunan budurcinsu. Bala'i wanda ba a sa mishi rana. Tabbas wannan ranar ta zama bakar rana wadda har abada ba zata kau daga idon Fadwa ba. Wasu a matsayin karuwai aka bada su haya, wasun su kuma duka aka siye su kamar bayi. Fadwa tana cikin wadanda aka siyar duka. An kuma saida ta ne ga wani busashshen bature mai suna James. James bisa manufa biyu ya sayi Fadwa, wato ya biya bukatar kansa kuma ya yi kasuwanci da ita. Wannan ne yasa ta sha wahala sosai a wannan takin. Ta zama baiwa ta gasken-gaske. James yana cikin jinsin jarababbin mazajen nan da basa gajiya da mata. Kusan ko wane lokaci yana tare da ita. Zai iya amfani da ita sau biyar ko shida a rana daya. A hakan kuma zai tura ta biyawa wasu tasu bukatar ya karbi kudi.

*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)

🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀

👨🏻‍💻👩🏻‍💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.
_____________________________________

©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________

```Gare ki 'yar Uwa ta gari``` *Ama Alh. Kabir* ```Nasmat tana yin ki sweet Sis Allah ya raya mana zuri'a```

```page 4```

Rayuwa ta yi wa Fadwa zafi, ko kadan bata samun hutu. Sun maida ita tamkar sex machine. Nan da nan ta ra-rake ta dawo kamar wata babbar mace.

*Bayan shekaru Uku*
Tun tana cikin firgici da tsoro har ta gaji ta bada kai. Ta zama cikakkiyar karuwa, wadda take ji babu wata macen da zata iya yi mata tunkaho game da juriyar aiki. Ta zama kwararriya wajen sarrafa maza da iya amfani da kwayoyin kara kuzari, da magun-gunan mata na karin ni'ima da juriyar sex. Haka turawa suka ci gaba da jagwal-gwalo da ita. Ta sake sosai har ma tana karawa da gyaran jiki. Kamar yadda yake kasancewa ga sauran wadan-da ake kaiwa irin wannan wajen.

Ta fara fadawa shaye-shaye dan ragewa kanta damuwa da yawan tunanin Ummynta. Wadda kullum take kwana take tashi da tunaninta. Babu shakka Fadwa ta bautu ta kuma ci kwa-kwarta kafin ta saba din. Daga baya kuma ta fara kasawa.
Chapter 2 · 0% Book details