Sashe 16
Yar Gwagwarmaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tafiya mai dan tsayi ya yi kafin ya tamyeta game da abinda ya ji ta fada "me yasa kika zabi ki sauka a hotel madadin ki wuce gidan iyayenki kai tsaye?" Hameeda ta marai-raice fuska ta soma magana "ina so ne sai na fara tura wasu dattabai su rarrasar min su, ina so zuciyarsu ta yi sanyi kafin na tunkare su. Ka san suna fushi dani saboda dadewar da nake ban zo gida ba". Ya jinjina kai yana auna kalaman nata. A lokacin kuma sun fara shiga karamar hanyar da zata sada su da karamin hotel din da ta bukaci ya kai ta. Kasancewar lokacin lokaci ne na sanyi kuma da safe, yasa layin ya yi shiru baka ganin giftawar mutum ko wani abin hawa a kan kari. Shiru ya ratsa tsakanin masoyan biyu. Ab'ha ya dukufa kan tukin da yake, ita kuma tana duba jakarta kamar mai neman wani abu. Ta saka salati tare da dan fiddo ido alamar ta rasa wani abu. Da sauri ya taka birkin motar yana kallonta da kuma jiran jin abinda ta yar ko ta manto a can. Cikin wannan yanayin ne ya samu ta shammace shi ta rufe masa fuska da wani karamin kelle. Kafin ya yi wani yunkurin tuni ya rasa kuzari a gabban jikinsa, kafin daga bisani kuma numfashinsa ya tsaya ga fita a kai-a kai ya dawo daya bayan daya.
Hameeda ta saki wani shu'umin murmushi na samun nasara, sannan ta dauko wayarta ta fara laluben wata number ta danna kira. Ba jimawa wanda take kiran ya daga wayar kamar dama can ita yake jira. Ba ko sallama ta fara magana. "Da girman kujerarka, aikinka ya kammala. Yanzu ina kake so a kai shi?". Ban san me aka gaya mata ba, ta dai amsa da cewa "an gama". Kawai sai ta katse wayar.
Ta fita ta zagaya ta yi wa kanta mazauni a bangaren driver. Ta tashi motar tare da juyar da kanta ta cillata bisa babban titi...
Babbar magana. 🤔
Ku ci gaba da bibiya, zan ci gaba.
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
```Page 22```
Ab'ha yana sunkuye bisa kujerar motar kamar mai bacci. Yayin da Hameeda take ta sharara gudu bisa titin kasancewar babu yawan zirga-zirgar ababen hawa a kan titin. Tafiya mai nisa ta yi kafin ta fara fita garin Kano. A lokacin ta fara hango inda ta nufa da shi, wato tsohon gidan gonar Alhaji Habib Inuwa. Zuciyarta ta fal da farin cikin cika aikin uban gidanta. Wani mahaukacin birki ta taka lokaci daya ta rike motar iya karfinta tana mai kife fuskarta bisa sitiyarin motar a matukar tsorace. A zatonta motar zata kife ne. Hakan kuwa duk ya faru ne a dalilin ganin mutum da ta gani ya diro mata tsudum a tsakiyar hanya ta gabanta, ba tare da sanin ta ina ya fito ba. 'Kuuuuuuuu...' Kake ji karar birki da kokarin tsayar da motar da take tsaka da gudu lokaci daya. Wani irin ihu Hameeda ta saki ganin motar zata bi ta kan wannan bakon mutumin da ya dirar mata a kan hanya sanye da bakaken kaya fuska a rufe. Sai dai kafin ta kai karshe ga tunaninta ta ga ya bace bat! Kamar bai taba wanzuwa a gurin ba. Sannan kuma motar ta tsaya lokaci daya.
Hameeda ta shiga waige-waige tana ware ido, ajiyar zuciya take saukewa wata na bin wata. Cikin sauri-sairi ta fara yunkurin yi wa motar key hannunta na rawa. "Wai shin ina ne kike kokarin kai shi Ha'ab?". Ta juyo da kallonta zuwa sit din motar na baya inda ta ji sautin na fitowa a matukar tsorace.
"Na shiga ukuna waye kai?...". Ta fada tare da dafe kanta cikin tsantsan tashin hankali da rudewa, saboda ganin wannan mutumin da motar ta bi ta kansa zaune a kan kujerar motar ta baya. Tunda take bata taba jin kanta a yanayin tsoro kwatankwacin wanda take ciki a yau ba. Mai bakin kayan nan ya saka hannu ya yane hular roba dake rufe da ilahirin fuskarsa zuwa wuya. Ga mamakin Hameeda sai ta ga gashi ya zubo ya rufe fuskar mamallakin kayan. Tsoronta ya kara hau hawa zuciyarta ta shiga sake-sake, a yanzu kam ta tabbatar gamo ta yi da aljan. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!". Ta fada cikin matsancin razani tana neman balle motar ta fita. Cikin zafin nama mai bazajje gashin nan ya yunkura ya kife ta da mari. Ji kake tas.! Ta tsandara kara tare da dafe kuncin nata da ta ji kamar zai cire saboda zafi, idonta a kan wannan aljani kamar yadda ta dauka.
Mai bazajjen gashin ya saka hannu ya yaye gashin tare da watsa shi bayan kansa. Me zata gani? Fadwa ce tsohuwar class mate abokiyar gaba. " Fadwa?!". Ta kira sunan cike da mamaki kana ta shiga tunanin gaggawa. 'Anya ma Fadwa ce? To idan ita ce ta yaya take bacewa kamar aljana?' Fadwa ta bushe da mahaukaciyar dariyar nan tata. Kana ta dora da cewa "dama na sani, mugu bashi da sabo Hameeda. Yanzu ke rashin arzikin naki har ya kai ki ga iya cutar da Ab'ha? Shin kin manta waye Abba kuwa? Abba fa shi ne mahaukacin masoyin nan naki, Ab'ha shi ne wanda ya bar iyayensa da 'yan uwansa da kuma duk wani jin dadin rayuwa saboda ke. Kin yi kuskure Hameeda kin yi kuskure na cutar masoyi kamar wannan. Duk muguwar hallaya da mummunar dabi'arki bai taba daina sonki ba. Kullum fatansa shi ne ki shiryu ki dawo gida, ki zama ta gari ku ci gaba da soyayyar da kuka fara a baya. Tir dake, da kuma halayyarki Hameeda".
Hameeda ta sunkui da kanta kasa cikin tsananin jin kunya da nauyin kalaman na Fadwa. Hakika bata fadi karya ba ita kanta shaida ce, tafi kowa sanin irin son da Abba yake mata. Ita shaida ce game da hakan tunda ya shafe shekaru yana bin bayanta a kasashen duniya... Tunaninta ya katse ne lokacin da ta ji an buda kofar motar dai-dai inda take an fizgo ta waje. Naushi daya fadwa ta yi mata ta nisanta ta da shaka da kuma fitar da numgashi dai-dai. Ta sumar da ita, sannan ta watsa ta bayan motar ta rufe, ita kuma ta shiga mazaunin driver ta tayar da motar ta nufi gidanta da su.
A ranar da karfe bakwai da rabi na safiya aka sallami Hajiya Laurat daga asibiti saboda ta sami sauki. Haka suka dunguma ita da yaranta wadanda take ganin su kadai suka rage abinda ke faranta mata a duniya, suka koma gida. Zukatansu dunkule da sabon yanayin kunci da jimamin da ya zame musu abokin rayuwa a 'yan kwanakin. Gidan ma sai ya zame musu wani fanko kamar ba asalin gidansu ba, sai suke kallon komai dake gidan kamar haramtacce ne a garesu. Haka kawai suka tsani gidan da komai dake cikinsa, sun tabbata duk wani jin dadi da suka yi an gina shi ne haramun. Mummunan haram na sayar da mutuncin 'yayan mutane.
Alhaji Habib kuwa yana can ya kebance kansa a daki yana jiran kiran Hameeda, domin ta sanar masa ta kai Ab'ha inda ya bukata. Manufarsa a kan hakan kuwa shi ne ya san in dai Ab'ha yana hannunsa to zai san duk wani shiri da Fadwa take yi a kansa, sannan ya wargaza shi. Zai kuma san sirrinta da inda take rayuwarta wanda hatta jami'an tsaro duka suka gagara sani. Ya tabbata idan ya sami duka wadannan zai iya batar da ita, ya shafe tarihinta da duk wasu muradai nata na nemawa mata 'yanci bisa kasuwancin da yake da yi su.
Yana cikin wannan dakon ya jiyo kiran ya shigo wayarsa da number tata. Cikin azama da ya daga wayar yana fadin "kin jinkirta da yawa Hameeda, ina nan ina ta zullumi". "Ka ci gaba da zullumin Shugaba, domin ko har yau baka fita a cikinsa ba". Fadwa ta gayar masa a zafafe ta cikin wayar. Alhaji Habib ya zabura kamar tsinke aka saka aka zungure shi. Ya kalli wayar, ya kuma kalli number. Babu shakka number Hameeda ce, amma muryar kam ya fi kowa sanin mamallakiyarta. "Fadwa?!". Ya fada a lokacin da gabansa yake dukan uku-uku, kansa na fitar da gumi. Ya tabbata ya rasa komai, ya rasa Hameeda ya rasa na hannun damanta Abba. Anya wannan mutum ce? Ta yaya ta gano shirinsu? Ya ma aka yi ta kama Hameeda bayan ta tabbatar masa ta kama gayen...?'
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
```Page 23```
Cikin tsawa ta katse masa tunani da fadin "ka dakatar da wannan karamin tunanin naka ka saurare ni tukunna. Na san yanzu ta riga ta kare maka kai kanka ka san da hakan, saboda haka nake gargadinka a kan ka tabbatar ka fadawa duniya da kotu gaskiya a tsayuwarka ta gobe gabanta. Ina mai shawartar ka da kar ka yi kokarin yin karya a goben domin ni na riga da na gama shirina. Ko da ka yi karyar na tanadi gaggan hujjojin da zasu tabbatar da gaskiya, saboda haka ka kula. A karshe ina maka albishir cewa gobe ce ranarka ta karshe da duk wani mahaluki zai kalleka da mutunci a ciki da wajen jihar Kano. Karshenka ya zo Shugaba..." Ta kece da dariya tana karasa maganarta "tabbas na fada kuma zan cika burina zai cika."
Alhaji Habib a matukar razane ya fara magana "ke tsinanniya 'yar gidan marasa mutunci, goben da kike cewa ta kare min to ke ce ta karewa baki sani ba. Ke har kin manta da yadda jami'an tsaron jihar nan suke nemanki ruwa a jallo? To ki sani har yanzu ni Alhaji Habib Inuwa Shugaba ne. Kina yin kuskuren bayyana kanki a goben kin zama gawa ko da kuwa a cikin kotun ne. Shashasha mara hankali" ya katse wayar a kufule ya shiga kai komo a dakin yana share gumi. Cike da neman mafita game da wannan masifar da ta tunkaro shi.
Hameeda ta saki wani shu'umin murmushi na samun nasara, sannan ta dauko wayarta ta fara laluben wata number ta danna kira. Ba jimawa wanda take kiran ya daga wayar kamar dama can ita yake jira. Ba ko sallama ta fara magana. "Da girman kujerarka, aikinka ya kammala. Yanzu ina kake so a kai shi?". Ban san me aka gaya mata ba, ta dai amsa da cewa "an gama". Kawai sai ta katse wayar.
Ta fita ta zagaya ta yi wa kanta mazauni a bangaren driver. Ta tashi motar tare da juyar da kanta ta cillata bisa babban titi...
Babbar magana. 🤔
Ku ci gaba da bibiya, zan ci gaba.
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
```Page 22```
Ab'ha yana sunkuye bisa kujerar motar kamar mai bacci. Yayin da Hameeda take ta sharara gudu bisa titin kasancewar babu yawan zirga-zirgar ababen hawa a kan titin. Tafiya mai nisa ta yi kafin ta fara fita garin Kano. A lokacin ta fara hango inda ta nufa da shi, wato tsohon gidan gonar Alhaji Habib Inuwa. Zuciyarta ta fal da farin cikin cika aikin uban gidanta. Wani mahaukacin birki ta taka lokaci daya ta rike motar iya karfinta tana mai kife fuskarta bisa sitiyarin motar a matukar tsorace. A zatonta motar zata kife ne. Hakan kuwa duk ya faru ne a dalilin ganin mutum da ta gani ya diro mata tsudum a tsakiyar hanya ta gabanta, ba tare da sanin ta ina ya fito ba. 'Kuuuuuuuu...' Kake ji karar birki da kokarin tsayar da motar da take tsaka da gudu lokaci daya. Wani irin ihu Hameeda ta saki ganin motar zata bi ta kan wannan bakon mutumin da ya dirar mata a kan hanya sanye da bakaken kaya fuska a rufe. Sai dai kafin ta kai karshe ga tunaninta ta ga ya bace bat! Kamar bai taba wanzuwa a gurin ba. Sannan kuma motar ta tsaya lokaci daya.
Hameeda ta shiga waige-waige tana ware ido, ajiyar zuciya take saukewa wata na bin wata. Cikin sauri-sairi ta fara yunkurin yi wa motar key hannunta na rawa. "Wai shin ina ne kike kokarin kai shi Ha'ab?". Ta juyo da kallonta zuwa sit din motar na baya inda ta ji sautin na fitowa a matukar tsorace.
"Na shiga ukuna waye kai?...". Ta fada tare da dafe kanta cikin tsantsan tashin hankali da rudewa, saboda ganin wannan mutumin da motar ta bi ta kansa zaune a kan kujerar motar ta baya. Tunda take bata taba jin kanta a yanayin tsoro kwatankwacin wanda take ciki a yau ba. Mai bakin kayan nan ya saka hannu ya yane hular roba dake rufe da ilahirin fuskarsa zuwa wuya. Ga mamakin Hameeda sai ta ga gashi ya zubo ya rufe fuskar mamallakin kayan. Tsoronta ya kara hau hawa zuciyarta ta shiga sake-sake, a yanzu kam ta tabbatar gamo ta yi da aljan. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!". Ta fada cikin matsancin razani tana neman balle motar ta fita. Cikin zafin nama mai bazajje gashin nan ya yunkura ya kife ta da mari. Ji kake tas.! Ta tsandara kara tare da dafe kuncin nata da ta ji kamar zai cire saboda zafi, idonta a kan wannan aljani kamar yadda ta dauka.
Mai bazajjen gashin ya saka hannu ya yaye gashin tare da watsa shi bayan kansa. Me zata gani? Fadwa ce tsohuwar class mate abokiyar gaba. " Fadwa?!". Ta kira sunan cike da mamaki kana ta shiga tunanin gaggawa. 'Anya ma Fadwa ce? To idan ita ce ta yaya take bacewa kamar aljana?' Fadwa ta bushe da mahaukaciyar dariyar nan tata. Kana ta dora da cewa "dama na sani, mugu bashi da sabo Hameeda. Yanzu ke rashin arzikin naki har ya kai ki ga iya cutar da Ab'ha? Shin kin manta waye Abba kuwa? Abba fa shi ne mahaukacin masoyin nan naki, Ab'ha shi ne wanda ya bar iyayensa da 'yan uwansa da kuma duk wani jin dadin rayuwa saboda ke. Kin yi kuskure Hameeda kin yi kuskure na cutar masoyi kamar wannan. Duk muguwar hallaya da mummunar dabi'arki bai taba daina sonki ba. Kullum fatansa shi ne ki shiryu ki dawo gida, ki zama ta gari ku ci gaba da soyayyar da kuka fara a baya. Tir dake, da kuma halayyarki Hameeda".
Hameeda ta sunkui da kanta kasa cikin tsananin jin kunya da nauyin kalaman na Fadwa. Hakika bata fadi karya ba ita kanta shaida ce, tafi kowa sanin irin son da Abba yake mata. Ita shaida ce game da hakan tunda ya shafe shekaru yana bin bayanta a kasashen duniya... Tunaninta ya katse ne lokacin da ta ji an buda kofar motar dai-dai inda take an fizgo ta waje. Naushi daya fadwa ta yi mata ta nisanta ta da shaka da kuma fitar da numgashi dai-dai. Ta sumar da ita, sannan ta watsa ta bayan motar ta rufe, ita kuma ta shiga mazaunin driver ta tayar da motar ta nufi gidanta da su.
A ranar da karfe bakwai da rabi na safiya aka sallami Hajiya Laurat daga asibiti saboda ta sami sauki. Haka suka dunguma ita da yaranta wadanda take ganin su kadai suka rage abinda ke faranta mata a duniya, suka koma gida. Zukatansu dunkule da sabon yanayin kunci da jimamin da ya zame musu abokin rayuwa a 'yan kwanakin. Gidan ma sai ya zame musu wani fanko kamar ba asalin gidansu ba, sai suke kallon komai dake gidan kamar haramtacce ne a garesu. Haka kawai suka tsani gidan da komai dake cikinsa, sun tabbata duk wani jin dadi da suka yi an gina shi ne haramun. Mummunan haram na sayar da mutuncin 'yayan mutane.
Alhaji Habib kuwa yana can ya kebance kansa a daki yana jiran kiran Hameeda, domin ta sanar masa ta kai Ab'ha inda ya bukata. Manufarsa a kan hakan kuwa shi ne ya san in dai Ab'ha yana hannunsa to zai san duk wani shiri da Fadwa take yi a kansa, sannan ya wargaza shi. Zai kuma san sirrinta da inda take rayuwarta wanda hatta jami'an tsaro duka suka gagara sani. Ya tabbata idan ya sami duka wadannan zai iya batar da ita, ya shafe tarihinta da duk wasu muradai nata na nemawa mata 'yanci bisa kasuwancin da yake da yi su.
Yana cikin wannan dakon ya jiyo kiran ya shigo wayarsa da number tata. Cikin azama da ya daga wayar yana fadin "kin jinkirta da yawa Hameeda, ina nan ina ta zullumi". "Ka ci gaba da zullumin Shugaba, domin ko har yau baka fita a cikinsa ba". Fadwa ta gayar masa a zafafe ta cikin wayar. Alhaji Habib ya zabura kamar tsinke aka saka aka zungure shi. Ya kalli wayar, ya kuma kalli number. Babu shakka number Hameeda ce, amma muryar kam ya fi kowa sanin mamallakiyarta. "Fadwa?!". Ya fada a lokacin da gabansa yake dukan uku-uku, kansa na fitar da gumi. Ya tabbata ya rasa komai, ya rasa Hameeda ya rasa na hannun damanta Abba. Anya wannan mutum ce? Ta yaya ta gano shirinsu? Ya ma aka yi ta kama Hameeda bayan ta tabbatar masa ta kama gayen...?'
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
```Page 23```
Cikin tsawa ta katse masa tunani da fadin "ka dakatar da wannan karamin tunanin naka ka saurare ni tukunna. Na san yanzu ta riga ta kare maka kai kanka ka san da hakan, saboda haka nake gargadinka a kan ka tabbatar ka fadawa duniya da kotu gaskiya a tsayuwarka ta gobe gabanta. Ina mai shawartar ka da kar ka yi kokarin yin karya a goben domin ni na riga da na gama shirina. Ko da ka yi karyar na tanadi gaggan hujjojin da zasu tabbatar da gaskiya, saboda haka ka kula. A karshe ina maka albishir cewa gobe ce ranarka ta karshe da duk wani mahaluki zai kalleka da mutunci a ciki da wajen jihar Kano. Karshenka ya zo Shugaba..." Ta kece da dariya tana karasa maganarta "tabbas na fada kuma zan cika burina zai cika."
Alhaji Habib a matukar razane ya fara magana "ke tsinanniya 'yar gidan marasa mutunci, goben da kike cewa ta kare min to ke ce ta karewa baki sani ba. Ke har kin manta da yadda jami'an tsaron jihar nan suke nemanki ruwa a jallo? To ki sani har yanzu ni Alhaji Habib Inuwa Shugaba ne. Kina yin kuskuren bayyana kanki a goben kin zama gawa ko da kuwa a cikin kotun ne. Shashasha mara hankali" ya katse wayar a kufule ya shiga kai komo a dakin yana share gumi. Cike da neman mafita game da wannan masifar da ta tunkaro shi.