← Book details Yar Gwagwarmaya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 23

Sashe 23

Yar Gwagwarmaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

A dakin Baffa kuma shi ne a kwance ya yi dai dai bisa lallausan gadon, idonsa a lumshe tamkar mai yin bacci. Ta tura kofar dakin ta shiga da salla. Cikin wasu kaya na atamfa dinkin doguwar riga buba. Ta yi matukar kyau kamar a sace ta a gudu. Ta kara cika ta yi bul bul gwanin sha'awa. Hannunta dauke da basket na abinci. Ta isa gaban gadon ta jere komai a kasan tails din inda ta shimfida wani zagayayyen farin kyalle, ta kalle shi da dara daran fararen idanunta tace "sweet husband ur break is ready". A hankali ya bude idonsa ya zube su a kanta kamar yau ya fara ganinta. Shi a kullum Fadwa sabuwa take zamar masa. Duk wata shiga da zata yi sai ta yi mishi kyau. Ya lushe idon ya koma budewa yana fadin "to a zo a dauke ni". Ya yi maganar a shagwabe da sigar wasa. Ya bata dariya sosai ta kuwa dara sannan tace "ai ko Fawad dinka ya wuce dauka yanzu balle kuma kai ubansa". Ya waro ido kadan "au haka ma zaki ce? To shikenan ki ci abincinki ke kadai". Jin hakan yasa ta marairaice fuska "afwan sweet husband tuba nake zo in dauke kan". Ta isa gareshi tana kokarin daga kansa ya tashi zaune. Shi kuwa sai dada narke mata yake yana dandara kansa da filo.

"Allah Dadyn Fawad rigimarka ta yi yawa, yanzu ya kake so a yi?". Ta tambayeshi lokacin da take daidaita zamanta bisa gadon. Ido daya ya kashe mata yana daga bargon da yake rufe da shi alamar ta shigo. Ta gane wayonsa da kuma manufarsa saboda haka ta makale kafada "ka bari mu fara yin break to". Ta fada a marairaice. Shi kuwa gogan sai ya saki blanket din ya juya mata baya. Wai a dole ya yi fushi. Da sauri ta kwanta a bayansa ta yi masa kyakkawar runguma tana rada masa a kunnensa "kar ka yi fushi da ni masoyi. Ni da duka abinda nake da shi naka ne hakak malak. Gani gareka hasken raina". Baffa da ya kasa jure salonta da yadda take maganar ya juyo da sauri ya kankame da yana fadin "Fawad zai iya girma a idonki Fadwa amma ni ba zan taba girma gareki ba. Ki sani ni ne asalin Babynki mai matukar bukatar kulawarki. Pls take a Gud care of me kin ji Fadwana?". Ta kanainaye mijinta cike da so da kauna da kuma jin dadin yadda yake gaya mata gaskiyarshi tace "yadda ka so haka Fadwa zata kasance..." Bata karasa ba ya mirginata suka shige blanket aka hau musayar... Nasmat kam na tattare litattafai da birurrukana nace "fatan alkhairi ga ilahirin rayuwarki 'yar gwa-gwarmaya ".

Tammat bi hamdillahi. A nan na kawo karshen wannan labarin mai cike da darussa ga rayuwar al'uma. Shakka babu labarin kirkirarre ne, amma abubuwan dake cikinsa asalin zahiri ne. Babu wanda ba a aikatawa a cikinsu. Fatana a kullum shi ne rubutuna ya yi tasirin canza rayuwar koda mutum daya ne daga mummuna zuwa kyakkyawa. Allah ta ala yasa mu dace amin. 🙏

Godiya mai tarin albarka ga daukacin masoya masu kokarin bibiyar wannan labarin wadanda ba zan iya kirga dukkaninku ba. Ina son ku duka kuma ina kaunarku. Fatana shi ne ku amfana da duk abinda na zo da shi. Na san kuna tare da ni, to ku ci gaba da kasancewa da ni zaku yi farin ciki.

Ina muku albishir da sabon littafina na gaba mai suna *BAN SAN SHI BA* karamin labari mai dauke da babban sako. Zai fadakar ya wa'azantar, sannan ya nishadantar da ku masoyana.

*Jinjina ta musamman ga kungiyar*
ZAMANI WRITERS ASSOCIATION.
Da daukacin marubutan dake cikinta. Allah ya kara hasken kwakwalwa jarumaina. 👍😇

Na barku lafiya 🙏

*Nasmat* ✍
Chapter 23 · 0% Book details