Sashe 17
Yar Gwagwarmaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*A maitama*
Karfe shida na yamma Ab'ha ya farfado daga nannauyan baccin da ya yi ta dalilin wata fauda dake jikin kyallen da Hameeda da shaka masa. A firgice ya farka yana kokarin tan-tance inda yake. Ganin kansa a cikin dakinsa ya yi matukar girgiza shi. Zumbur ya mike ya bude kofar ya fita yana dube-dube. Babu kowa a falon sai TV dake ta faman aiki ita kadai. Ya dauki remote ya kashe TV sannan ya zarce izuwa dakin Fadwa.
Da sallama ya tura kofar dakin ya shiga, tana zaune bisa kujerar gaban madubi tana daure gashin kanta da band. Ya ja ya tsaya a jikin kofa yana tunano abubuwan da suka faru da shi. Ya ma rasa ta inda zai fara magana. Shi dai ya san ya dauki Hameeda amma bai sami kaita inda ta bukata ba, ya kuma san ta yafa mishi wani kyalle a fuska. Daga nan kuma bai koma sanin komai ba sai yanzun da ya farka ya ga kanshi a gida.
"Meye ya rage wanda baka gaya min ba kuma Ab'ha? Naga ka yi shiru. Ka fada mana, kana sonta, ka yarda da ita, ba zata iya cutar da kai ba ko?". Tana maganar tana ci gaba da shirin da take. Ya yi kasa da kansa cikin matukar nauyi da jin kunyarta "ki yi hakuri Fadwa ni na dauki so kamar iri daya ne. Ashe abinda ban sani ba shi ne yadda nake ji game da ita daban yadda itama take ji game da ni daban. Na yi nadama Fadwa na kuma bar so bari na har abada. Na yarda soyayyata ta zo a sahu na marasa sa'a a duniya. Domin kuwa shi so daya ne, kuma ita kadai nake yi wa shi. Ta cuce ni ta ci amanata. A yadda ta nuna zata iya kashe ni.." Wasu zafafan hawaye suka biyo bayan kalaman nashi, kafin ya ci gaba "zata iya kashe ni Fadwa, saboda haka yanzu na tsane ta, na tsani duk wani abu da ya shafi so!". Allah sarki Ab'ha tausayinsa ya kama Fadwa shiru ya ratsa na dan lokaci kafin ta nisa tace "shikenan ka manta da ita kawai, ka ga, da ban je da wuri ba da sun lalata duka shirinmu. Nufinsu shi ne su azabtar da kai har sai ka fada musu shirinmu, su san inda nake su kashe mu duka da ni da kai. Amma Allah bai basu iko ba. Ka manta kawai komai ya wuce, na san Allah ba zai taba basu wannan damar ba".
Shiru ya koma ratsa tsakaninsu. Ganin haka yasa ya dago kansa dake kasa yace "na gode da ceton rayuwata da kika yi Fadwa". Murmushi kawai ta yi mishi ya juya zai fita.
"Ab'ha". Ta kira sunanshi, ya juyo yana dubanta tare da fadin " aa Fadwa ki kirani Abba kawai." Sai da ta dan sarara saboda tausayin shi da yanayin yadda ya yi maganar. Sannan ta kauda kanta tace "sorry Abba. Ka kasance cikin shiri gobe komai zai zo karshe". Ya gyada kai alamar ya gamsu sannan ya fice jikinsa a sanyaye.
Bayan ya kammala waya da lauyoyinsa ya koma kan gadonsa ya zauna tare da hada uban tagumi da duka hannayensa biyu, ya ma rasa abin yi. Yana cikin wannan halin wata bakar sakar ta zo masa a rai. Ai ko cikin azama ya daga wayarsa ya kira lambar Acp Sauwam. Har wayar ta yanke ba a daga ba. Ya koma danna kira itama dai kamar zata yanke sannan aka daga da
"Hello".
" Hello Sauwam kana ji na?".
"Ka yi hakuri ba zai sami damar amsa wayar ba yanzu yana meeting".
Aka fada da wata kakkaurar murya.
"Ok idan ya kammala a sanar masa na kira kuma ina neman shi gidana".
"To yallabai".
Dukkaninsu suka kashe wayar.
Karfe takwas na daren Acp Sauwam ya isa gidan Alhaji Habib domin amsa gayyatar da ya yi masa. Bai sha wata wahala wajen shiga gidan ba, kasancewar shi sananne ga dukkan securitys din. Yanayin da ya ga Alhajin ya tabbatar masa cewa yana cikin damuwa. Bayan gajeruwar gaisuwa aka gabatar masa da abin motsa baki. Sai dai bai ci komai ba idonsa na kan Shugaba. Ya fara magana "yallabai kamar kana cikin damuwa, ka kira ni nan ko lfy?". "Lafiyar kenan Sauwam, na tabbata a irin wannan aikin da kuke sam baku can-canci a kiraku jami'an tsaro ba". Asp cikin rashin fahimta ya kalli Alhajin yana neman karin bayani. Shugaba cikin fada-fada yake magana. "Banda lalacewar aikin dan sanda a yau, ta yaya za'a ce mace daya ta gagari ilahirin 'yan sandan dake jihar Kano? Ta sace min 'yata sannan ta watsa video yadda ake tozaratar da ita. Ta koma sace min dana, shima ta sako video yadda ta wulakanta shi ta kashe shi. Har yanzu ban san inda suke ba. Saboda jin dadin duk wannan abin da ta yi ba a kama ta ba yau ta kira waya tana shaida min gobe a tafiyar da zan yi kotu zata kashe ni a bainar jama'a. Wannan shi ne tsaron da kuke bawa kasa?"
Sauwam jikinsa ya yi sanyi, sai yanzu ya fahimci inda maganganun Alhajin suka dosa. Ya gyara zama yana fadin "ka gasgata ni Alhaji har yau muna kan binciki a kan wannan mai laifin. Ina tabbatar maka idonmu-idonta ba zata sha ba. Yaranka kuma da iznin Allah zaka same su cikin koshin lafiya. Ka kwantar da hankalinka babu abinda zai same ka, muna tare da kai. Babu shakka wannan wata dama ce a garemu da zamu sami damar kama ta. Barta ta zo gaben, babu makawa karshen ta'addancinta ne ya zo". Ya mike a fusace ya yi wa Alhajin sallama ya fita, a ransa yana sakawa muddin Fadwa ta bayyana kanta gobe to ko shi ko ita, sai ya tabbata kwato wa 'yan sanda mutuncinsu da take neman zubarwa a idon duniya.
Alhaji Habib ya bi bayansa da wani shu'umin murmushi ya tabbata ya kwanto mata kura, ta zo goben. Mikewa ya yi ya shiga cikin gidansa yana umartar Baffa da Anisa a kan kar su yarda su fita gidan nan balle har wani ya gan su ya san sun kubito daga hannun Fadwa. Yana gama maganar ya wuce sashensa ya barsu da kallon juna cikin wani al'ajabin.
Mugun shiri 🤔
Keep following, mu ga me suke shirin yi wa jarumarmu? 😒
Zan ci gaba.
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
```Page 24```
*Daren lahadi*
Wannan daren ya kasance mai tsayi kuma mai cike da buruka ga mutane masu yawan gaske. Ilahirin jama'ar jihar Kano sun kagu gari ya waye a je kutu, domin su ji me Shugaba zai fada domin kare kansa a gaban kotu? Musamman 'yan siyasa masu ban-bancin ra'ayi. Haka talakawa da suke masa kallon inuwa kuma mafaka ga irinsu. Sun kagu garin ya waye su ga me ake shirin kulla masa? Abin ya yi kamari a zukatansu domin wasu daga cikinsu ji suke kamar zasu iya bada rayukansu domin kare Shugabansu.
Haka bangaren 'yan sanda sun riga sun gama yin kwakkwaran shiri domin ganin sun kauda tarihin wata 'yar gwa-gwarmaya a birnin Dabo. A ganinsu wannan shi kadai zai sa su ci gaba da amsa sunan jami'an tsaro cike da izza. To Fadwa ma ba a barta a baya ba ta gama shirinta tsab, da kuma hada duk wasu ababen da take da tabbacin zata bukata goben a cikin kotu. Duk da cewa abokin aikin nata baya cikin nutsuwarsa, Ab'ha ya kusa rasa tunaninsa duka. Saboda ganin soyayyar da ya shafe shekaru yana tarairaya ta ruguje a rana daya. Ya rasa mafaka ko mafita, shi kansa bai san takamaiman yanayin da zuciyarsa take ciki ba. Ya zama tamkar wani hoto abin jinginewa. Babu um ba um...um. Sai ido da yake binta da su a duk shiga da fitarta.
Hajiya Laurat da yaranta ma a ranar basu bari an barsu a baya ba, domin kuwa su ma sun gama yin shiri tsab dan yakar zalumci da son zuciya irin na Alhajin, sun gama yanke hukunci a matsayinsu na al'uma sun tabbata barin mutum irinsa a sarari ba karamin illa bane ga duka kasa. Duk da suna cikin matsanaciyar damuwa hakan bai hana zukatansu son bayyana gaskiya ba.
A wannan daren mai sarkakiya Alhaji Habib baccinsa ya tika hadda minshari, domin zamansa gogagge kuma masanin siyasa da tuggunta, ya san ya riga ya hadawa Fadwa kashin da ba zata iya rabe shi ba. Wato ya dana mata tarkon da ba zata taba tsallakawa ba. Bisa wannan dalilin ya tattare duk wata damuwa ya yi watsi da ita gefe. Domin dama Fadwa ita ce babbar damuwarsa.
*Washe gari*
Kasancewar ranar litinin ce, yasa zirga-zirga da kai komon jama'a da ababen hawa ta yawaita. Duk da cewa ana tsuga sanyi hakan bai dakile al'uma ga fitowa da sanyin safiyar suna nufatar guraren ayyukansu ba. (Monday) litinin kenan aka ce ko Nasara na tsoronta.
Karfe takwas dai-dai makeken agogon dake manne a bangon barandar kofar shiga high court din ya buga. Dimbin jama'a maza da mata yara da manya sun gama cika wajen har ba masaka tsintsiya. 'Yan jaridu daga kafafen yada labarai iri-iri sun bayyana har sun fara gudanar da ayyukansu. Duk inda ka gifta ji kake suna fadin "masu kallo da saurarenmu kamar yadda kuke ji kuma kuke gani, wato filin babbar kotu ya gama ciki da batsewa da jama'a, masu son ganin yadda wannan murdaddiyar shari'ar zata kaya. Lauyoyi daga ko-wane bangare sun bayyana, yayin da masu laifin ma tuni aka kawo su cikin kotun. Yanzu ya kasance kowa a nan yana dakon isowar Shugaba Alhaji Habib ne da kuma ainihin babban alkali na wannan jihar tamu mai albarka."
Karfe shida na yamma Ab'ha ya farfado daga nannauyan baccin da ya yi ta dalilin wata fauda dake jikin kyallen da Hameeda da shaka masa. A firgice ya farka yana kokarin tan-tance inda yake. Ganin kansa a cikin dakinsa ya yi matukar girgiza shi. Zumbur ya mike ya bude kofar ya fita yana dube-dube. Babu kowa a falon sai TV dake ta faman aiki ita kadai. Ya dauki remote ya kashe TV sannan ya zarce izuwa dakin Fadwa.
Da sallama ya tura kofar dakin ya shiga, tana zaune bisa kujerar gaban madubi tana daure gashin kanta da band. Ya ja ya tsaya a jikin kofa yana tunano abubuwan da suka faru da shi. Ya ma rasa ta inda zai fara magana. Shi dai ya san ya dauki Hameeda amma bai sami kaita inda ta bukata ba, ya kuma san ta yafa mishi wani kyalle a fuska. Daga nan kuma bai koma sanin komai ba sai yanzun da ya farka ya ga kanshi a gida.
"Meye ya rage wanda baka gaya min ba kuma Ab'ha? Naga ka yi shiru. Ka fada mana, kana sonta, ka yarda da ita, ba zata iya cutar da kai ba ko?". Tana maganar tana ci gaba da shirin da take. Ya yi kasa da kansa cikin matukar nauyi da jin kunyarta "ki yi hakuri Fadwa ni na dauki so kamar iri daya ne. Ashe abinda ban sani ba shi ne yadda nake ji game da ita daban yadda itama take ji game da ni daban. Na yi nadama Fadwa na kuma bar so bari na har abada. Na yarda soyayyata ta zo a sahu na marasa sa'a a duniya. Domin kuwa shi so daya ne, kuma ita kadai nake yi wa shi. Ta cuce ni ta ci amanata. A yadda ta nuna zata iya kashe ni.." Wasu zafafan hawaye suka biyo bayan kalaman nashi, kafin ya ci gaba "zata iya kashe ni Fadwa, saboda haka yanzu na tsane ta, na tsani duk wani abu da ya shafi so!". Allah sarki Ab'ha tausayinsa ya kama Fadwa shiru ya ratsa na dan lokaci kafin ta nisa tace "shikenan ka manta da ita kawai, ka ga, da ban je da wuri ba da sun lalata duka shirinmu. Nufinsu shi ne su azabtar da kai har sai ka fada musu shirinmu, su san inda nake su kashe mu duka da ni da kai. Amma Allah bai basu iko ba. Ka manta kawai komai ya wuce, na san Allah ba zai taba basu wannan damar ba".
Shiru ya koma ratsa tsakaninsu. Ganin haka yasa ya dago kansa dake kasa yace "na gode da ceton rayuwata da kika yi Fadwa". Murmushi kawai ta yi mishi ya juya zai fita.
"Ab'ha". Ta kira sunanshi, ya juyo yana dubanta tare da fadin " aa Fadwa ki kirani Abba kawai." Sai da ta dan sarara saboda tausayin shi da yanayin yadda ya yi maganar. Sannan ta kauda kanta tace "sorry Abba. Ka kasance cikin shiri gobe komai zai zo karshe". Ya gyada kai alamar ya gamsu sannan ya fice jikinsa a sanyaye.
Bayan ya kammala waya da lauyoyinsa ya koma kan gadonsa ya zauna tare da hada uban tagumi da duka hannayensa biyu, ya ma rasa abin yi. Yana cikin wannan halin wata bakar sakar ta zo masa a rai. Ai ko cikin azama ya daga wayarsa ya kira lambar Acp Sauwam. Har wayar ta yanke ba a daga ba. Ya koma danna kira itama dai kamar zata yanke sannan aka daga da
"Hello".
" Hello Sauwam kana ji na?".
"Ka yi hakuri ba zai sami damar amsa wayar ba yanzu yana meeting".
Aka fada da wata kakkaurar murya.
"Ok idan ya kammala a sanar masa na kira kuma ina neman shi gidana".
"To yallabai".
Dukkaninsu suka kashe wayar.
Karfe takwas na daren Acp Sauwam ya isa gidan Alhaji Habib domin amsa gayyatar da ya yi masa. Bai sha wata wahala wajen shiga gidan ba, kasancewar shi sananne ga dukkan securitys din. Yanayin da ya ga Alhajin ya tabbatar masa cewa yana cikin damuwa. Bayan gajeruwar gaisuwa aka gabatar masa da abin motsa baki. Sai dai bai ci komai ba idonsa na kan Shugaba. Ya fara magana "yallabai kamar kana cikin damuwa, ka kira ni nan ko lfy?". "Lafiyar kenan Sauwam, na tabbata a irin wannan aikin da kuke sam baku can-canci a kiraku jami'an tsaro ba". Asp cikin rashin fahimta ya kalli Alhajin yana neman karin bayani. Shugaba cikin fada-fada yake magana. "Banda lalacewar aikin dan sanda a yau, ta yaya za'a ce mace daya ta gagari ilahirin 'yan sandan dake jihar Kano? Ta sace min 'yata sannan ta watsa video yadda ake tozaratar da ita. Ta koma sace min dana, shima ta sako video yadda ta wulakanta shi ta kashe shi. Har yanzu ban san inda suke ba. Saboda jin dadin duk wannan abin da ta yi ba a kama ta ba yau ta kira waya tana shaida min gobe a tafiyar da zan yi kotu zata kashe ni a bainar jama'a. Wannan shi ne tsaron da kuke bawa kasa?"
Sauwam jikinsa ya yi sanyi, sai yanzu ya fahimci inda maganganun Alhajin suka dosa. Ya gyara zama yana fadin "ka gasgata ni Alhaji har yau muna kan binciki a kan wannan mai laifin. Ina tabbatar maka idonmu-idonta ba zata sha ba. Yaranka kuma da iznin Allah zaka same su cikin koshin lafiya. Ka kwantar da hankalinka babu abinda zai same ka, muna tare da kai. Babu shakka wannan wata dama ce a garemu da zamu sami damar kama ta. Barta ta zo gaben, babu makawa karshen ta'addancinta ne ya zo". Ya mike a fusace ya yi wa Alhajin sallama ya fita, a ransa yana sakawa muddin Fadwa ta bayyana kanta gobe to ko shi ko ita, sai ya tabbata kwato wa 'yan sanda mutuncinsu da take neman zubarwa a idon duniya.
Alhaji Habib ya bi bayansa da wani shu'umin murmushi ya tabbata ya kwanto mata kura, ta zo goben. Mikewa ya yi ya shiga cikin gidansa yana umartar Baffa da Anisa a kan kar su yarda su fita gidan nan balle har wani ya gan su ya san sun kubito daga hannun Fadwa. Yana gama maganar ya wuce sashensa ya barsu da kallon juna cikin wani al'ajabin.
Mugun shiri 🤔
Keep following, mu ga me suke shirin yi wa jarumarmu? 😒
Zan ci gaba.
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
```Page 24```
*Daren lahadi*
Wannan daren ya kasance mai tsayi kuma mai cike da buruka ga mutane masu yawan gaske. Ilahirin jama'ar jihar Kano sun kagu gari ya waye a je kutu, domin su ji me Shugaba zai fada domin kare kansa a gaban kotu? Musamman 'yan siyasa masu ban-bancin ra'ayi. Haka talakawa da suke masa kallon inuwa kuma mafaka ga irinsu. Sun kagu garin ya waye su ga me ake shirin kulla masa? Abin ya yi kamari a zukatansu domin wasu daga cikinsu ji suke kamar zasu iya bada rayukansu domin kare Shugabansu.
Haka bangaren 'yan sanda sun riga sun gama yin kwakkwaran shiri domin ganin sun kauda tarihin wata 'yar gwa-gwarmaya a birnin Dabo. A ganinsu wannan shi kadai zai sa su ci gaba da amsa sunan jami'an tsaro cike da izza. To Fadwa ma ba a barta a baya ba ta gama shirinta tsab, da kuma hada duk wasu ababen da take da tabbacin zata bukata goben a cikin kotu. Duk da cewa abokin aikin nata baya cikin nutsuwarsa, Ab'ha ya kusa rasa tunaninsa duka. Saboda ganin soyayyar da ya shafe shekaru yana tarairaya ta ruguje a rana daya. Ya rasa mafaka ko mafita, shi kansa bai san takamaiman yanayin da zuciyarsa take ciki ba. Ya zama tamkar wani hoto abin jinginewa. Babu um ba um...um. Sai ido da yake binta da su a duk shiga da fitarta.
Hajiya Laurat da yaranta ma a ranar basu bari an barsu a baya ba, domin kuwa su ma sun gama yin shiri tsab dan yakar zalumci da son zuciya irin na Alhajin, sun gama yanke hukunci a matsayinsu na al'uma sun tabbata barin mutum irinsa a sarari ba karamin illa bane ga duka kasa. Duk da suna cikin matsanaciyar damuwa hakan bai hana zukatansu son bayyana gaskiya ba.
A wannan daren mai sarkakiya Alhaji Habib baccinsa ya tika hadda minshari, domin zamansa gogagge kuma masanin siyasa da tuggunta, ya san ya riga ya hadawa Fadwa kashin da ba zata iya rabe shi ba. Wato ya dana mata tarkon da ba zata taba tsallakawa ba. Bisa wannan dalilin ya tattare duk wata damuwa ya yi watsi da ita gefe. Domin dama Fadwa ita ce babbar damuwarsa.
*Washe gari*
Kasancewar ranar litinin ce, yasa zirga-zirga da kai komon jama'a da ababen hawa ta yawaita. Duk da cewa ana tsuga sanyi hakan bai dakile al'uma ga fitowa da sanyin safiyar suna nufatar guraren ayyukansu ba. (Monday) litinin kenan aka ce ko Nasara na tsoronta.
Karfe takwas dai-dai makeken agogon dake manne a bangon barandar kofar shiga high court din ya buga. Dimbin jama'a maza da mata yara da manya sun gama cika wajen har ba masaka tsintsiya. 'Yan jaridu daga kafafen yada labarai iri-iri sun bayyana har sun fara gudanar da ayyukansu. Duk inda ka gifta ji kake suna fadin "masu kallo da saurarenmu kamar yadda kuke ji kuma kuke gani, wato filin babbar kotu ya gama ciki da batsewa da jama'a, masu son ganin yadda wannan murdaddiyar shari'ar zata kaya. Lauyoyi daga ko-wane bangare sun bayyana, yayin da masu laifin ma tuni aka kawo su cikin kotun. Yanzu ya kasance kowa a nan yana dakon isowar Shugaba Alhaji Habib ne da kuma ainihin babban alkali na wannan jihar tamu mai albarka."