Sashe 19
Yar Gwagwarmaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ai kuwa a take kotun ta kaure da hayaniya ciki da waje. Dubbanin mutanen dake jin labarin 'yar gwa-gwarmaya da hatsabibancinta suka marmatso dan ganewa idonsu wace ce ita?. Cikin matsananciyar kaduwa da tashin hankali Alhaji Habib ya mike tsaye yana fadin "Gata nan Fadwa ce ku kama ta kashe ni zata yi". Ya fada cikin bada umarni ga daukacin ma'aikatan dake wajen. Gaba daya suka mike suka nufi inda take suka yi mata kawanya. Kawunan bindigoginsu na fuskantar kwakwalwarta. 'Yan kallo na ciki da waje suka dauki ihu "ga 'yar gwa-gwarmaya, ga 'yar gwa-gwarmaya, yau dubunki ta cika, ku harbe ta! Ku harbe ta!!" Abinda da yawa suke fada kenan. Ganin kotun ta kacame da maganganunsu yasa alkalin buga gudumarsa domin dawo da nutsuwar kotu. Tsit! Kake ji ba wani mai magana ko dogon motsi, jami'an tsaro kuma suna nan zagaye da Fadwa alamar ta shiga hannu. Ita kuwa ko a jikinta ballatana ta nuna wata alama da zata nuna ta ji tsoro.
Alkalin ya kara daidaita zaman gilashinsa yana kare mata kallo. Yasha jin labarinta a gidajen radio da tv, jaridu da kuma bakunan al'uma. Amma bai taba tsammanin haka take ba.
Yariya ce shar da ita, siririya mai matsakaicin jiki, wankan tarwada mai karamin kyawu da yake tattare da sirruka. Da kallo daya zaka gane hakan a tattare da ita. Kada kai ya yi, ya yi sabon rubutu bisa takardar gabansa sannan ya yi gyaran murya ya fara da bawa jami'an tsaron umarnin su matsa gefe kutu tana son ji daga gareta.
Nan fa 'yayan cikin Alhaji Habib Shugaba suka duri ruwa. Ganin 'yan sandan sun matsa bisa umarnin alkali yasa ya mike cikin marairaicewa da kaskantar da kai. "Ya mai girma mai shari'a, a taimake ni a kama wannan mai laifin wallahi guba ce mai bata zukatan al'uma, ta sace min 'yata ta kuma baza video yadda ake keta mata haddi ana wulakanta ta a duniya. Ta kuma sace min babban yarona har yau ban san inda suke ba. Ta kuma sanar cewa nima yau zata kashe ni". Alkalin ya gama kallon Alhaji Habib da kuma nazartar kalamansa ya maida kallonsa ga Fadwa. Yana mamakin Kasancewar wannan yarinya dunkule da wadannan laifukan. Ya tsaida idonsa kan Alhaji Habib kana yace "da kai da ita duka kuna gaban shari'a yanzu. Saboda haka ka kwantar da hankalinka kotu ba zata taba barin mai laifi ya sha ba.
Ya juya ga Fadwa dake tsaye a inda take tamkar wadda aka dasa ya jefa mata tambaya "yarinya zamu iya sanin wace ce ke da kuma dalilin sako kanki a cikin wannan shari'ar? Shin mene ne alakarki da su dukan?" Babu wani jinkiri ta daga fuskarta daidai ta fukanci al'umar dake wajen sannan ta fara magana. "Dafari dai sunan Fadwa wadda a yanzu aka fi sani da 'yar gwa-gwarmaya. Kuma ni marainiya ce da ta tashi a gidan marayu na gwamnati mai lamba 3 a nan cikin garin Kano. Tun lokacin da na fara wayon sanin matsayina na tsinci kaina a matsayin marainiya maras asali da tushe. Hakan yasa na kuduri aniyar sayawa kaina kima da nemawa kaina makoma ta gari ta hanyar dagewa in sami nagartaccen ilimin da zai saya mini 'yanci a rayuwata ta gaba. A saboda haka ne na zamo daliba mafi kwazo da maida hankali a makarantar gwamnati ta jeka ka dawo da nake zuwa. Wannan ya saka gaba daya malamai da shugabannin makarantar suke alfahari da ni. A shekarar 2005 na sami nasarar kammala karatuna na sakandire. Inda a wannan lokacin ya zamana nice dalibar da tafi kawacce maki a matakin karshe. Wannan ne ya saka na sami damar kasancewa a cikin dalibai goma da wancan azzalumin yake dauka da sunan tura su kasashen duniya su ci gaba da karatu. Farin ciki sosai iyayen rikona suka yi a lokacin da labarin ya zo garesu. Bayan duk wasu shirye-shirye muka bar Nigeria muka tafi American da zummar ci gaba da karatu. Amma kash rana ta farko da muka shiga kasar ba a barmu mun kwana da mutuncinmu ba. A ranar ya saida mu duka ya karbi kudinsa ya dawo Najeriya. Mutanen nan basu duba karancin shekarunmu da maraicinmu ba a wannan lokacin, haka suka yi ta ci mana zarafi tun muna wahala har muka dawo muka saba.
A karshe da na sami kubita na dawo da zummar tona asirinsa karyata ni ya yi. Aka ce biyana aka yi in bata masa suna. A lokacin har ya gabatar da yan matan da ya fidda mu tare a matsayin shaida a kotu da takardun karya masu nuna alamar cewa lallai karatu suke yi a can". Ta sarara tare da matse kwallar idonta.
A lokacin duk wanda yake ciki da wajen kotun jikinsa ya fara sanyi. Ta dago da jajayen idonta ta ci gaba. "Bayan wannan lokacin na yi kokarin fita batun maganar in barshi da Allah, amma me? Sai na ga har zuwa lokacin bai daina abinda yake yi ba, bai daina kwasar 'yayan jama'a yana kaiwa turawa suna biyan bukatunsu da su ba. Haka kuma al'uma basu daina kallonsa a matsayin mutumin kirki mai kaunarsu ba. Bakin cikin rayuwar da ya jefani shi ya kashe uwar rikona duk da ba ita ta haifeni ba. Wannan ne yasa na dauki damarar yaki da shi. Saboda tsananin tausayin iyaye duk da ni ban san nawa ba. Babban burina shine ko wace mace ta sami farin ciki ko da ni ban samu ba. Bani da burin da ya wuce in kawar da karuwanci a kasar haihuwata. In kuma dakile ire-iren wannan mugun bawa masu safarar mata domin yin fasikanci, saboda lalacewar abin yanzu har kasa mai tsarki suke kai karuwai suna yin karuwanci. Maganar da ya yi na cewa na sace 'yarsa an keta mata haddi tabbas gaskiya ne. Ni na sace Anisa kuma na saida ta kamar yadda ya sayarda ni aka lalata ni. Amma maganar basu dawo gareshi ba wannan karya ne, a gidansa dukkansu suka kwana. Ina tafe da cikakkun bayanai da hujjoji da zasu tabbatar da laifinshi a fili kowa ya ganshi. Idan kotu ta bani iznin hakan."
Ta saka aya idonta a kan alkalin kotun. Zumbur Alhaji Habib ya mike, jikinsa na kyarma ya fara magana da karfi. "Karya take, mai shari'a wallahi karya take. Ban taba saida 'yar kowa ba. Ban san komai game da maganganunta ba.." Maganar alkalin ce ta katse shi. Inda yake cewa "kutu zata baka damar yin magana idan bukatar hakan ta taso. Yin magana ba da izni ba laifi ne, dan haka ka kula". Saboda tsabar rikicewa da fitar hayyaci kasa zama ya yi. A lokacin ji yake kamar ya rufe ido ya ganshi a gidanshi.
Wani masifaffen ciwon kai ya ziyarce shi lokaci daya. Idonsa suka fara gani dishi dishi. Wani daya daga cikin lauyoyinsa ne ya mike ya taimaka masa ta hanyar zaunar da shi. Gaba daya ya soma fita hayyacinsa. Alkalin ya maida kallonsa ga Fadwa yace "ina hujjojin naki suke? Kotu na bukatar gani da kuma jin su. Farin ciki ya lullube zuciyarta ganin dukkanin matsalointa sun zo karshe. Hannu ta saka ta sauke jakar hannu dake rataye a kafadarta. A cikinta ta fiddo wani faifan CD ta fara mikawa mai gabatar da kara na kotun wato rajistara ko ince muhutin alkali.
Bayan samun izni daga alkalin aka dauki faifan CD aka saka a wata DVD dake ajiye a wurin. Wadda dama an tanade ta ne domin ire iren haka. Jama'ar dake wajen duka sun nutsu, al'ajabi ya cika zukatan wasu. 'Yan jaridu sai kara saura kamarorinsu suke a daidai fuskar TV da suka tabbatar ta cikinta hoton videon zai bayyana.
Ni kaina Nasmat tsayar da idona waje daya na yi dan ganin abinda zai fara bayyana a cikin laifukan Alhaji Habib Inuwa. Readers ku ban lokaci zuwa gobe dan jin me aka fara karo da shi.
Keep following.😘
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_*Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร*_
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
Na gode! Na gode da kulawa da kuma dimbin comments naku masoyan gaske.
'YAR MUTAN ARKILLA NOVES GROUP
KIN BOY ISAH NOVELS
UMMYN YUSRAH NOVELS
ZAMANI WRITERS FANS
WAHALA BATA KISA FANS GROUP
Nasmat na matukar godiya gareku mambobi na wadannan groups masu albarka Allah ya bar zumunci ya yi karko, ana matukar tare.
```Page 26```
A karon farko hoton Hameeda ne ya fara bayyana, wanda Ab'ha ya yi daukarta a lokacin da yake bibiyarta. Jikinta sanye da irin tsinannun kayan shan iskan nan na turawa irin na hutun bakin ruwa. Tana kwance ta yi plat bisa kirjin wani bature dake kwance a kan farin yashi yana shafa kirjinta.
Daidai nan tace a dakatar. Aka tsayar da CD ta hanyar danna stop. Ta fara magana "wannan da kuke gani wata daya daga cikin takwarorin tafiyata ne. Tare ya fitar da mu america. Amma da yake su suna da ra'ayin karuwancin har yau suna aiki tare da shi. Har yau bata daina yin karuwanci ana bashi kudi ba. Bayan ita yana da 'Yan mata sama da talatin wadanda duk aikin da suke masa kenan." "Ab'ha" ta kira sunan da daga sauti. Ba a ji amsa ba, sai karar bude daya kofar kotun da aka ji, tayayyen matashin ya shigo rike da ita tana ware ido, hannayenta na daure a baya kamar police ya kama mai laifi.
Ilahirin jama'ar dake kotun duka hankalinsu ya koma kan Hameeda. A lokacin ne kuma Fadwa ta dora da cewa "wannan ita ce kuka gani a jikin videon nan. Mutane suka kara kafa mata ido cike da son tabbatarwa, "tabbas ita ce, wallahi ita ce". Abinda suka shiga ambato a tare kenan. Suna "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un". Wasu daga cikin na fadin " subhanallahi". Hameeda ta yi kasa da kanta cike da kunya da bakin cikin ganin wannan rana da bata taba saka ran ganinta nan kusa ba.
Alkalin ya kara daidaita zaman gilashinsa yana kare mata kallo. Yasha jin labarinta a gidajen radio da tv, jaridu da kuma bakunan al'uma. Amma bai taba tsammanin haka take ba.
Yariya ce shar da ita, siririya mai matsakaicin jiki, wankan tarwada mai karamin kyawu da yake tattare da sirruka. Da kallo daya zaka gane hakan a tattare da ita. Kada kai ya yi, ya yi sabon rubutu bisa takardar gabansa sannan ya yi gyaran murya ya fara da bawa jami'an tsaron umarnin su matsa gefe kutu tana son ji daga gareta.
Nan fa 'yayan cikin Alhaji Habib Shugaba suka duri ruwa. Ganin 'yan sandan sun matsa bisa umarnin alkali yasa ya mike cikin marairaicewa da kaskantar da kai. "Ya mai girma mai shari'a, a taimake ni a kama wannan mai laifin wallahi guba ce mai bata zukatan al'uma, ta sace min 'yata ta kuma baza video yadda ake keta mata haddi ana wulakanta ta a duniya. Ta kuma sace min babban yarona har yau ban san inda suke ba. Ta kuma sanar cewa nima yau zata kashe ni". Alkalin ya gama kallon Alhaji Habib da kuma nazartar kalamansa ya maida kallonsa ga Fadwa. Yana mamakin Kasancewar wannan yarinya dunkule da wadannan laifukan. Ya tsaida idonsa kan Alhaji Habib kana yace "da kai da ita duka kuna gaban shari'a yanzu. Saboda haka ka kwantar da hankalinka kotu ba zata taba barin mai laifi ya sha ba.
Ya juya ga Fadwa dake tsaye a inda take tamkar wadda aka dasa ya jefa mata tambaya "yarinya zamu iya sanin wace ce ke da kuma dalilin sako kanki a cikin wannan shari'ar? Shin mene ne alakarki da su dukan?" Babu wani jinkiri ta daga fuskarta daidai ta fukanci al'umar dake wajen sannan ta fara magana. "Dafari dai sunan Fadwa wadda a yanzu aka fi sani da 'yar gwa-gwarmaya. Kuma ni marainiya ce da ta tashi a gidan marayu na gwamnati mai lamba 3 a nan cikin garin Kano. Tun lokacin da na fara wayon sanin matsayina na tsinci kaina a matsayin marainiya maras asali da tushe. Hakan yasa na kuduri aniyar sayawa kaina kima da nemawa kaina makoma ta gari ta hanyar dagewa in sami nagartaccen ilimin da zai saya mini 'yanci a rayuwata ta gaba. A saboda haka ne na zamo daliba mafi kwazo da maida hankali a makarantar gwamnati ta jeka ka dawo da nake zuwa. Wannan ya saka gaba daya malamai da shugabannin makarantar suke alfahari da ni. A shekarar 2005 na sami nasarar kammala karatuna na sakandire. Inda a wannan lokacin ya zamana nice dalibar da tafi kawacce maki a matakin karshe. Wannan ne ya saka na sami damar kasancewa a cikin dalibai goma da wancan azzalumin yake dauka da sunan tura su kasashen duniya su ci gaba da karatu. Farin ciki sosai iyayen rikona suka yi a lokacin da labarin ya zo garesu. Bayan duk wasu shirye-shirye muka bar Nigeria muka tafi American da zummar ci gaba da karatu. Amma kash rana ta farko da muka shiga kasar ba a barmu mun kwana da mutuncinmu ba. A ranar ya saida mu duka ya karbi kudinsa ya dawo Najeriya. Mutanen nan basu duba karancin shekarunmu da maraicinmu ba a wannan lokacin, haka suka yi ta ci mana zarafi tun muna wahala har muka dawo muka saba.
A karshe da na sami kubita na dawo da zummar tona asirinsa karyata ni ya yi. Aka ce biyana aka yi in bata masa suna. A lokacin har ya gabatar da yan matan da ya fidda mu tare a matsayin shaida a kotu da takardun karya masu nuna alamar cewa lallai karatu suke yi a can". Ta sarara tare da matse kwallar idonta.
A lokacin duk wanda yake ciki da wajen kotun jikinsa ya fara sanyi. Ta dago da jajayen idonta ta ci gaba. "Bayan wannan lokacin na yi kokarin fita batun maganar in barshi da Allah, amma me? Sai na ga har zuwa lokacin bai daina abinda yake yi ba, bai daina kwasar 'yayan jama'a yana kaiwa turawa suna biyan bukatunsu da su ba. Haka kuma al'uma basu daina kallonsa a matsayin mutumin kirki mai kaunarsu ba. Bakin cikin rayuwar da ya jefani shi ya kashe uwar rikona duk da ba ita ta haifeni ba. Wannan ne yasa na dauki damarar yaki da shi. Saboda tsananin tausayin iyaye duk da ni ban san nawa ba. Babban burina shine ko wace mace ta sami farin ciki ko da ni ban samu ba. Bani da burin da ya wuce in kawar da karuwanci a kasar haihuwata. In kuma dakile ire-iren wannan mugun bawa masu safarar mata domin yin fasikanci, saboda lalacewar abin yanzu har kasa mai tsarki suke kai karuwai suna yin karuwanci. Maganar da ya yi na cewa na sace 'yarsa an keta mata haddi tabbas gaskiya ne. Ni na sace Anisa kuma na saida ta kamar yadda ya sayarda ni aka lalata ni. Amma maganar basu dawo gareshi ba wannan karya ne, a gidansa dukkansu suka kwana. Ina tafe da cikakkun bayanai da hujjoji da zasu tabbatar da laifinshi a fili kowa ya ganshi. Idan kotu ta bani iznin hakan."
Ta saka aya idonta a kan alkalin kotun. Zumbur Alhaji Habib ya mike, jikinsa na kyarma ya fara magana da karfi. "Karya take, mai shari'a wallahi karya take. Ban taba saida 'yar kowa ba. Ban san komai game da maganganunta ba.." Maganar alkalin ce ta katse shi. Inda yake cewa "kutu zata baka damar yin magana idan bukatar hakan ta taso. Yin magana ba da izni ba laifi ne, dan haka ka kula". Saboda tsabar rikicewa da fitar hayyaci kasa zama ya yi. A lokacin ji yake kamar ya rufe ido ya ganshi a gidanshi.
Wani masifaffen ciwon kai ya ziyarce shi lokaci daya. Idonsa suka fara gani dishi dishi. Wani daya daga cikin lauyoyinsa ne ya mike ya taimaka masa ta hanyar zaunar da shi. Gaba daya ya soma fita hayyacinsa. Alkalin ya maida kallonsa ga Fadwa yace "ina hujjojin naki suke? Kotu na bukatar gani da kuma jin su. Farin ciki ya lullube zuciyarta ganin dukkanin matsalointa sun zo karshe. Hannu ta saka ta sauke jakar hannu dake rataye a kafadarta. A cikinta ta fiddo wani faifan CD ta fara mikawa mai gabatar da kara na kotun wato rajistara ko ince muhutin alkali.
Bayan samun izni daga alkalin aka dauki faifan CD aka saka a wata DVD dake ajiye a wurin. Wadda dama an tanade ta ne domin ire iren haka. Jama'ar dake wajen duka sun nutsu, al'ajabi ya cika zukatan wasu. 'Yan jaridu sai kara saura kamarorinsu suke a daidai fuskar TV da suka tabbatar ta cikinta hoton videon zai bayyana.
Ni kaina Nasmat tsayar da idona waje daya na yi dan ganin abinda zai fara bayyana a cikin laifukan Alhaji Habib Inuwa. Readers ku ban lokaci zuwa gobe dan jin me aka fara karo da shi.
Keep following.😘
*Nasmat* ✍
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*'YAR GWA-GWARMAYA.*
(Fitilar 'yan-cin mata.)
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_*Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร*_
https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation?
©
'Yar mutan
Arkilla✍
____________
Na gode! Na gode da kulawa da kuma dimbin comments naku masoyan gaske.
'YAR MUTAN ARKILLA NOVES GROUP
KIN BOY ISAH NOVELS
UMMYN YUSRAH NOVELS
ZAMANI WRITERS FANS
WAHALA BATA KISA FANS GROUP
Nasmat na matukar godiya gareku mambobi na wadannan groups masu albarka Allah ya bar zumunci ya yi karko, ana matukar tare.
```Page 26```
A karon farko hoton Hameeda ne ya fara bayyana, wanda Ab'ha ya yi daukarta a lokacin da yake bibiyarta. Jikinta sanye da irin tsinannun kayan shan iskan nan na turawa irin na hutun bakin ruwa. Tana kwance ta yi plat bisa kirjin wani bature dake kwance a kan farin yashi yana shafa kirjinta.
Daidai nan tace a dakatar. Aka tsayar da CD ta hanyar danna stop. Ta fara magana "wannan da kuke gani wata daya daga cikin takwarorin tafiyata ne. Tare ya fitar da mu america. Amma da yake su suna da ra'ayin karuwancin har yau suna aiki tare da shi. Har yau bata daina yin karuwanci ana bashi kudi ba. Bayan ita yana da 'Yan mata sama da talatin wadanda duk aikin da suke masa kenan." "Ab'ha" ta kira sunan da daga sauti. Ba a ji amsa ba, sai karar bude daya kofar kotun da aka ji, tayayyen matashin ya shigo rike da ita tana ware ido, hannayenta na daure a baya kamar police ya kama mai laifi.
Ilahirin jama'ar dake kotun duka hankalinsu ya koma kan Hameeda. A lokacin ne kuma Fadwa ta dora da cewa "wannan ita ce kuka gani a jikin videon nan. Mutane suka kara kafa mata ido cike da son tabbatarwa, "tabbas ita ce, wallahi ita ce". Abinda suka shiga ambato a tare kenan. Suna "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un". Wasu daga cikin na fadin " subhanallahi". Hameeda ta yi kasa da kanta cike da kunya da bakin cikin ganin wannan rana da bata taba saka ran ganinta nan kusa ba.