← Book details Secondary School Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 36

Sashe 32

Secondary School Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kuma a yau ne hutun Ibrahim ya 茩are da ya dauka zai koma bakin aiki dan haka tun safe Rufy take ta shirye shirye sabida kada mijin ta ya fita bai karya ba

Lokacin da yazo tafiya ji tayi kamar ta bishi domin sai take jin kamar kafin ya dawo wani abu zai same ta ,kallon shi tayi tana fa蓷in yaya ka aiko da azahar a karbar ma abinci banaso ka dinga siyan na waje

Tsaya wa yayi yana kallon ta ganin yadda take wannan shagwa蓳ar Tata da kullum take 茩ara narkar da shi yace
Gaskiya sweetie ya kamata a canza min sunan nan nikan idan kina cemin yaya sai naga kamar ba mijin ki ba

Dariya tayi tana fa蓷in
"Shike nan na dai na daga yanzu zan dinga cema ma hubby nasan nayi ma ko?

Hancin ta yaja yana fadin "eh yayi min sweetie bye bye sai na dawo

Daga haka ta koma cikin gidan cike da kewar mijin nata wanda cikin dan lokaci ka蓷an ya sa mata wata irin muguwar 茩aunar shi

Waya ta dakko domin kiran amarya jamsy

馃崈馃崈 SECONDARY SCHOOL馃崈馃崈

(Love & romantic story)

JAMA'A MUNA DA KAYAN GYARA FA WLH MASU KYAU BANA YABON KAYANA AMMA SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI HAR DAHUWAR KAZA MUNAYI DA NA YAN SHILA馃構馃構馃構DADI A BAKI DADI A AIKACE 馃拑馃拑馃拑MUNA DA TABAJE,AKWAI DARE DAYA WANKA GOMA , MUNA DA MAGANIN SANYI AKWAI WACCE SANYI YA HANA HAIHUWA INSHA ALLAH KUMA BATA ZA'A DACE ALLAH KE BADA HAIHUWA,KAI ABIN SAI WANDA YA GANI

SANNAN MUNA DA KAYAN BACCI MASU KYAU DA LAUSHI IYA KUDIN KA IYA SHAGALIN KA ,A DINGA YI ANA CANZA KAYAN BACCI UWAR GIDA

MUNA DA ATAMFOFI DA MAYAFAI HAR MA DA TAKALMA ABIN BA ANAN YA TSAYA BA AKWAI FASHION NA YARI DA SARKA MASU KYAU DA FAUKAR HANKALI,HARMA DA JAKUN KUNA

AKWAI KAYAN KITCHEN MA AZO A CANZAWA OGA KWANUKA MASU KYAU DA INGANCI

KU DAI KAWAI KU TUNTUBI WANNAN NUMBAR DOMIN SAMUN NAKU CIKIN AMINCI DA RAHUWA ,MUNA NAN A JAHAR KANO MUNA AIKA KAYAN MU KO INA DA IZININ UBANGIJI

DOMIN KARIN BAYANI 08144054353

Shalele ce馃拑

Paid page 79&80

_________Masha Allah rayuwa tana ta tafiya ango Ibrahim da amarya Rufy kamar ba suba cikin abinda bai wuce sati biyu ba sun 茩ara kyau sai hasken amarci suke,sosai suke nuna kulawa da junan su

Ibrahim yasai wa Rufy babbar waya dan haka kullum tana online suna hira da Farida da jamsy sosai sun zama kamar yan uwa kuma suna 茩ara bawa junan su shawarar yadda zasu kula da mazajan su

Tun da ta idar da sallar magariba take ta shirye shiryen shigowar mijin nata , wanka tasha cikin wasu 茩anan kaya riga da wando wanda wandon da shi da babu duk 蓷aya haka ma rigar domin kuwa ina nonon ta ta riga fe Shima banda sama ,turaruka masu da蓷in kamshi ta feshe jikin ta da su
Sannan ta fito ta fara shirya musu abincin su a inda suka saba ci ,jin karar bu蓷e Kofar falon ne yasa ta 蓷ago da gudun ta ta 茩ara sa inda yake tana kaimai kyakkyawan sunbata tare da fa蓷in

"Maraba da dawowa mijina abin alfahari na ango na kuma tauraro na,a da gidan yamin duhu amma tunda ka shigo sai naga yayi haske lallai kai din na musamman ne,ina alfahari da kai domin kaine gwarzo na

Tunda ta fara mai wannan kirarin yake kallon ta domin kullum abin nata da sabon salo yake zuwa na yau da ban na gobe da ban
Kuma shiyasa a kullum take 茩ara shiga ransa har takai idan bata gidan har Allah Allah yake ya dawo domin yasan kalamai masu dadi ne zai samu tare da kulawa da tarairaya

(Dan Allah mata mu 茩ara zage damtse wajan nuna kulawar mu ga mazajan mu,mu zama masu nuna farin cikin mu idan muna tare da su ko da kuwa Bama cikin wannan farin cikin ,mu zama muna wa mazajan mu kirari koda kuwa bamai yawa ba
Wlh mijina shine mutumin da ya ra蓷amin shalele haka zalika a kullum idan ya shigo gida ina kallon yana yinsa nasan a farin ciki ya shigo zan ce na shalele bada kanka asare idan kaje gida kace ya fa蓷a sosai yake nuna jin dadin wannan Maganar kunga dai ba yawa

Amma wata sai mijin ya dawo sannun da zuwa ma kamar anyi mata dole sai cin magani take tana ha蓷e rai kamar wata mesa,wata sanu da zuwan ma wahalar fa蓷a take mata sai tayi sati bata fadawa miji ba bare akai ga maganar wanka da sa turare

Sai ranada miji yace zai 茩ara aure ayi ta masifa da ita bayan ministar ce ta marasa M

Nida kaina zan nemowa mazajan masu wannan halin zawarawa duk su aura馃毝馃徎鈥嶁檧锔忦煔娥煆烩€嶁檧锔忦煔娥煆烩€嶁檧锔?)

Wanka ta ra茩ashi yayi sannan suka ci abinci cike da wasa da dariya ,kallo suka tsaya yi kafin su je su kwanta

Tana daga kwance tayi matashi da kansa ne take cewa cike da shagwa蓳a

"Hubby Dan Allah kabar ni gobe zamuje gidan jamsy kaga tunda akai bikin sati biyu kenan bamu jeba kace amarci nake yi nima to nagama tunda na riga ta aure ..

Hannu Ibrahim yakai yana kama hancin ta yasan yarda ja ka蓷an yana fa蓷in
"Watakon baby son yawo ne ya motsa miki ko hadda cewa kin gama amarci bayan ni kuma ban gama nawa angon cin ba kinga sai na nemo wata matar tazo ta 茩ara sa min ragowar amarcin da kika bari ko?
Ya 茩ara sa maganar yana kallon fuskar ta

Da sauri ta tashi zaune tana fa蓷in

"Haba dai hubby bafa haka nake nufi ba ina nufin idan na dawo daga gidan jamsy sai naciga ba da amarcin

Sosai Rufy taba Ibrahim dariya dan haka ya dara son ranshi kafin ya tsagaita yace
"Karki damu baby itafa wadda zata zo tayi amarcin tana gamawa zata tafi shike nan ke kuma sai muci gaba da rayuwar mu kawai

"A'a dan Allah hubby ni wallahi ma na hakura da zuwa gidan jamsyn dama Farida ce tace ya kamata muje dan haka zan ce mata kawai ta tafi ita kadai wataran Ni naje

Nan ma dariya yasa mata ganin yadda take maganar da iya gaskiyar ta dan haka yace
"No baby karki damu kema zakije goben Allah ya kaimu lafiya dama gwada ki nake

Hannu tasa tana kaimai dukan wasa cike da shagwa蓳a take fa蓷in
"Amma wallahi hubby ka tsorata Ni wai ni yanzu idan na ganka da wata ya zanji chabb ai sai kun kaini asibiti nasan

Washe gari da wuri ta gama duk abinda zatai sabida tare zasu fita zai aje ta a gidan jamsy sun hadu da faridan a can

Pink color din material tasa doguwar riga sannan ta nade kanta da mayafi kalar zaran jikin matarial din
Rufy ba ma'abociyar kwalliya bace amma da yake yar gayu ce gayun ya zauna ajikin ta sai ta fito kamar wadda tasha makeup kuma a haka kwalli kawai tasa

Tana shiga gidan da gudu jamsy tazo ta rugume ta sosai tayi farin cikin ganin ta,ba tare da 蓳ata lokaci ba suka fara hira kamar ba gobe ahaka har Farida itama ta 茩ara so nan fa suka hadu aka sha hira sosai sannan suka shiga kitchen tare sukai girki suka ci suka gyara gidan kafin aka cigaba da hira
Cikin sati biyun jamsy ta dan canza domin koba komai ta samu kwanciyar hankali g dai shi ba don Abdullahi take ba amma yadda yake nuna mata 茩auna da kulawa yasa take ganin zata iya rayuwa da shi ta har abada

*************Sanye take cikin hijabi har 茩asa tasa ni茩af ga Safa a abinda ake gani ajikin ta tafiya take a nutse wanda duk wanda yaga yanayin tafiyar ta zaisan cewa ta musamman ce wajan nutsuwa domin tafiyar ma abin kallo ce yadda take daga 茩afar a nutse ta kuma sauke ba tare da tada kura ba

Wani wajan idan tazo wucewa yara zasu ce Malama ina wuni ko kadan ba'a jin sautin Muryar ta wajan amsa musu sai dai kawai aga 蓷aga hannu da take wa yaran da suke wasa

Ahaka tayi ta tafiya har ta 茩ara so kofar gidan lokacin akwai mutane a zaune dan haka ta tsugunna har 茩asa ta gaishe su ,amsa mata sukai fuskar su cike da fara'a Sannan ta tashi ta shiga gidan
Daga daga cikin mutanan da ke wajan a zaune ne yace

"Kai masha Allah kaga yarinyar nan kamar ba ita ba gaskiya abin yayi kyau Allah ya tsare gaba

Lokacin da ta shiga cikin gidan ba kowa dan haka tun daga tsakar gida take rada sallama amma ba'a amsa mata ba, cike da gajiya ta shiga dakin ta tana aje jakar hannun ta da take cike da littafan addini Sannan ta cire hijja bin jikin ta bakin gado ta samu ta zauna tana sauke ajiyar zuciya ,jin alamar tawowa zuwa dakin da take ciki ne yasa ta tashi tsaye tana juyowa

jidda na gani sosai abin ya bani mamaki yaushe ta koma Malama gaba 蓷aya yana jinta ya sauya kamar ba jidda mai kau蓷in nan ba, umman zeey ce ta shigo 蓷akin tana fadin

"Ashe kin dawo dama yanzu muna shigowa nake cewa yaci ace kin dawo ai

"Eh wallahi umman zeey na dawo ina ta sallama naji gidan shiru nima shigowa ta kenan

"Ai dole kiji gidan shiru tunda kunyi 拼a ina zama
Cewar maman jidda da tashigo yanzu

"Wayyo Allah umma kar kuce min zeey ta haihu wayyo dadi kashe ni nima yanzu na zama momy
Ta 茩ara sa maganar cike da matsanancin farin ciki

Ganin lamarin nata zaiyi nisa ne yasa iyayan suka bar mata 蓷akin
Sauri tayi ta shirya cikin doguwar rigar aftar drees sai rawar jiki take domin abinda take so yanzu irin taje taga abinda zeey ta haifa

"Yar banza yanzu zeey ta zama umma kenan itama ta 蓷an 蓷ana taji ai kuwa zan tambaye ta idan sa wahala
Ita kadai take ta faman surutu tana shirya wa

Lokacin da ta fito ne umma take tambayar ta ina zuwa haka da magariba
"Umma yanzu fa kuka cemin zeey ta haihu wajan ta zan tafi na babyn
Chapter 32 · 0% Book details