← Book details Sakayyah Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 38

Sashe 8

Sakayyah Part 3 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Acan Falon Momyn kuwa bayan Moddibo yasha ruwa kana yaci Snacks da Drinks Momy ta fito suka gaisa bayan sun gaisa ta kallesa da kulawa tace.
“Ina su Didi kuma?”.
Sake sunkuyar da kansa yayi tare da cewa.
“Momy su Didi suna gida amma sunce zasu ɗan fito zuwa azahar, sannan zasu fara ta gidan su Ummu kafin suzo”.
Dai-dai lokacin kuma Asma'u ta shigo Falon bakinta ɗauke da sallama kasancewar Haiydar ya kirata ya sanar mata Khausar tazo gida.
Khausar na ganinta ta miƙe da tsalle kana ta haɗa da gudu suka rungume juna da Asma'u suka fara juyawa atsakiyaar Falon.
Cikin tsuke fuska Moddibo ya kalli Asma'u tare da faɗin.
“Asmau me haka ki sake ta?”.
Ahankali Asma'u ta sunkuyar da kanta ƙasa sai kuma ta saki Khausar ta tsugunna gefen Moddibo cike da ladabi tace.
“Yah Moddibo sannu da zuwa Ina yini”.
“Lafiya”.
Ya faɗa yana ɗan sake Fuskara sai kuma yace.
“Ke baki ga yanayin yanda ƙawar taki take bane kike mata irin wannan rungumar?”.
Dariyar dake cinta ta danne ganin yanda Khausar ta Cunno baki kana tace.
“Yah Moddibo ayi haƙuri”.
Yana murmushi yace.
“In sha Allah yanzu dai akiyaye”.
Kai ta gyaɗa tare da miƙewa ta riƙe hannun Khausar suka nufi bedroom ɗin ta.
Ganin haka yasa ya miƙe tare da cewa.
“Momy bari in fita dan su Dr Jameel na jirana zamuje gida Abban Jameel ”.
Mommy na gyara mayafinta tace.
“Ayyah ai nima Jameel ɗin nan ina so akawo minshi in ganshi Haiydar yata bani labarinsa”.
Cike da girmamawa yace.
“In sha Allahu Momy za'a kawo miki shi”.
Murmushi tayi tare da faɗin.
“Toh ka gaishe su”.
Amsawa yayi kana ya fita.

A dai-dai lokacin kuma Didi, Lalla Khadijah, Lalla Hafsat, Suna gidan Ummin Jameel duk sun gaisa da ƴan Uwanta wanda suka fara taruwa saboda bikin bayan sun gama suka fito zuwa gidansu Momyn Khausar.

Suna shiga Falon dai-dai lokacin Asma'u da Khausar na kitchen Khausar har mamakin kanta take saboda ƙosai da kunun gyaɗan da taci da safe, kana yanzu kuma Asma'u da kanta ta tuƙa mata tuwan Semovita da miyar ɗanyen kuɓewa aƙaramin dining Dake kitchen ɗin suke zaune.
Khausar kam ta kasa daina mamakin kanta yanda take cin tuwon sosai kallon Asma'u da itama tayi wani irin kyau na ban mamaki tayi ta fito a asalin amarya tace.
“Wallahi Asma'u har mamakin kaina na keyi rabona da abinci hakafa nafi wata huɗu”.
Murmushi Asma'u tayi tare da cewa.
“Ikon Allah baby ɗan albarka yasan yazo garinsu kenan”.
Murmushi Khausar tayi tare da sunkuyar da kanta ta ɗan kalli cikin,
dai-dai lokacin kuma suka jiyo sallamarsu Didi sun shigo gidan cikin wani irin...

By
*GARKUWAR MARUBUTA**SAKAYYAH Book 3 PAGE 3*

NA
*Aysha Aliyu Garkuwa*

KAZAURE COLLEGE OF NURSING SCIENCES (KCONS)
Lafiya Uwar jiki, Kuma sai da lafiya ake morar rayuwa. Kazaure College Of Nursing Sciences (KCONS) ta kawo muku ingantaccen tsarin koyar da jinya da unguwar zoma, mun himmatu wajen samar da kwararrun ma'aikatan jinya da unguwar zoma a fadin Nigeria da ma matakin duniya baki daya, a KCONS mun tanadar muku kwararrun malamai, ingantaccen yanayi da tsarin koyo da koyarwa kai harma da tsarin e-learning, ka zalika akwai tabbataccen tsaro a dakunan kwanan dalibai maza da mata, bugu da kari kudin makaranta dai-dai aljuhu, KCONS munanan a lamba 5 layin fadar sarki dake kan hanyar kano zuwa daura a Kazaure jahar Jigawa, za'a iya samummu a shafikanmu na facebook da instagram @KCONsciences domin bayani, za'a iya tuntubanrmu a wadannan lambobin, 07066542055, 08035298851, ko shafin mu na yanan gizo @ http://kcons.edu.ng/admission KCON sciences kan turbar aiki da kwarewa muka shahara.
Chapter 8 · 0% Book details