Sashe 16
Sakayyah Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Nan ya sake yi musu tofi cikin zam-zam ɗin na wasu keɓantattun ayoyi da sauri kamar haka.
*Al-araf ayata 117, 118, 119, 120, 121 da kuma 122. Sai Suratul Yunus daga ayata 79, 80, 81, 82, Sai kuma suratul Ta-ha aya ta 65 66, 67, 68, 69, 70, Sai kuma suratul al-Kafurune gaba ɗayanta, da kuma suratul al-ikhlas dukanta sai suratul al-falaq itama dua da kuma suratul An-nas itama dukanta da forko zaki samu zam-zam ki zuba mai yawa a tsabtacecen mazubi ko roba ko kwarya, ki tabbatar zam-zam ɗin zai ishe ki sha da kuma yin wanka, sai zuba a robar kana kisa kanyen magariyar guda bakwai an fison ɗanye Amman busheshenma ba matsala zaki daka guda bakwai in ɗanyen nema ki daka bakwai, sai ki zuba a Zam-zam ɗin kana ki karanta ayoyin Alkur'ani mai tsarkin dana lissafa Miki da surorin ki ɗan motsashi zakiga ya ɗan buga kumfa sai ki ɗiba a cup wanda zakisha ki ƙoshi kuyi gyatsa, sai ki zauna bisa yaƙini da niyar Allah ya yaye Miki matsalarki ko wacce iri yace Sihiri, ko tsafi, Sammu, ko kambun baka, ko cutar da ba'a gane kantaba ko sharrin iska. Kisha koyi hamdala kana ki ɗauki sauran na cikin robar ki samu sarkakekken wurin da babu najasa kiyi niya da duk matsalarki kiyi wanka. Wlh da izinin Ubangiji zakiji sauƙi ki samu sauyi anaso na farko dai kiyishi da Zam-zam inda hali duk bayan wata shida ko shekara ɗaya kiyi kiyiwa yaranki da mijinki dan makarine mai girma in ba hali saboda tsadar da Zam-zam keyi in kinyi na forkon da Zam-zam to na biyu kiyi da ruwan sama na uku da duk ruwan da ya sauwaƙa gareki, inda hali ko yaushe da Zam-zam in ba hali ayi na forkon da Zam-zam in bai samuba ayi da ruwan sama na roƙon da na biyun da na ukun, kiyishi maƙo maƙo ko wata wata ana dai son duk bayan wata shida ko shekara ɗaya kiyi, yar uwa ko ɗanki, ƴarki mijinki ƙanwarki ƴaƴan yar uwa ki ko ɗan uwa duk inda kukaga yaro ko yarinya sun cika rashin ji gagara rawan kai gardama da alamun kwaucewa hanya kuyi masu yanada matuƙar fa'ida da falala, sadakace fisabilillahi idan kinji daɗinshi kiyi niya kiyiwa Mahaifiyata Fatima Dedde na ƙu'huwa ƙafa uku da fatan Allah ya jiƙanta ya kai haske da ni'ima Qabarinta. Ni kuma inada wata buƙata mai girma da falala da daraja a wurin Allah kuyi min addu'a kisa yaranki suyi min addu'a kice su roƙawa Aysha Aliyu Muhammad Garkuwa Allah ya biya mata buƙatarta akan alkhairi, ya raya mata ƴaƴanta Muhammad Jabeer da Maimuna Ikhram da Ibraahim ya shirye su ya basu ilimi mai amfani da albarka yasa su zama abin alfahari ga Musulunci da Musulmai mazan ya basu mata na gari da zuraya ɗaiyi ba, macen ya bata miji na gari da zuri'a ɗaiyiba, kana Allah ya bani wasu ƴaƴan masu albarka da nisan kwana tagwaye inyiwa Deddena takwara da Babana in samu Aliyu Haiydar da Fatima Khausar in samu auta A'isha takwarar kakata mafi soyuwa*
Man Lima da Hajja Nana ma bayan sunyi sallar la'asar da Baffa Liman da Yah Abba suka kama hanyar komawa Jauro Yaya.
Acan ɓangaren Hajiya Bunayya ma tunda tasha wannan ruwan tofin sai tsutsotsin suka yawaita fita yayin da suke cinta da gasken gaske sai dai tana shiga ruwan ɗumi zai lafa amma bazai wuce awa biyu zuwa uku ba zai sake dawowa haka tayi wannan yinin ranan zunibi da sakayyan aikinta na bibiyarta.
Daddare bayan sallar Isha'i Moddibo ne da Dr Jameel zaune afalon Hajiya Bunayya tana zaune Sai murtsukuku take yi akan kujeran jin yanda tsutsotsin ke cinta yayin da Amina ke zaune gefenta bisa duk kan alamu Alhamdulillah ta fara samun sauƙi har nishinma duk ta daina .
Anutse Dr Jameel ya kalli Hajiya Bunayya kana yace.
“Akwai tests ɗin da za'a Miki.
Sai kiyi ƙoƙari kije asibitu aduba ki acan”.
Cikin sanyi tace .
“Nagode Nagode Dr Jameel Allah ya saka da Alkhairi ”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Bakomai”.
Kana suka miƙe suka fita dai-dai lokacin kuma Dr Zakariyya da Asiya ne zaune amota suna hira fitowa su Dr Jameel ne yasa Asiya yiwa Dr Zakariyya sallama ta fita kana Dr Jameel ya shiga Motar.
Moddibo kuwa bayan Khausar dake shiga Side ɗin Momy ya nufa yana shiga falon yaga ba kowa sai Raudat dake kallon Catoon yace.
“Raudy ina Addah Khausy?”.
Hankalinta na kan kallon tace.
“Tana ɗakinta”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Momy fa?”.
Still idanunta na kan tv tace.
“Tana gidan Ummin Jameel Yah Haiydar ya kaita”.
Kai ya gyaɗa kana ya shiga ɗakin Khausar zaune ya sameta agaban Weldrop ɗin ta gabanta littafaine tana ta duddubawa.
Da mamaki ta kallesa kana tace.
“Yah Mu'allim har nan kuma?”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh ai gidan mune”.
Kai ta gyaɗa hannunta na kan littafin tace.
“Eh nasani ai yanzu in Momy tazo ta same mufa?”.
Murmushi yayi tare da shafa sajensa kana yace.
“Eh dai-dai kenan idan Momy tazo ta ganni zata san ina buƙatar matata zata kora min ke mu tafi tun da ke yanzu kin iya gardama da taurin kai ”.
*Al-araf ayata 117, 118, 119, 120, 121 da kuma 122. Sai Suratul Yunus daga ayata 79, 80, 81, 82, Sai kuma suratul Ta-ha aya ta 65 66, 67, 68, 69, 70, Sai kuma suratul al-Kafurune gaba ɗayanta, da kuma suratul al-ikhlas dukanta sai suratul al-falaq itama dua da kuma suratul An-nas itama dukanta da forko zaki samu zam-zam ki zuba mai yawa a tsabtacecen mazubi ko roba ko kwarya, ki tabbatar zam-zam ɗin zai ishe ki sha da kuma yin wanka, sai zuba a robar kana kisa kanyen magariyar guda bakwai an fison ɗanye Amman busheshenma ba matsala zaki daka guda bakwai in ɗanyen nema ki daka bakwai, sai ki zuba a Zam-zam ɗin kana ki karanta ayoyin Alkur'ani mai tsarkin dana lissafa Miki da surorin ki ɗan motsashi zakiga ya ɗan buga kumfa sai ki ɗiba a cup wanda zakisha ki ƙoshi kuyi gyatsa, sai ki zauna bisa yaƙini da niyar Allah ya yaye Miki matsalarki ko wacce iri yace Sihiri, ko tsafi, Sammu, ko kambun baka, ko cutar da ba'a gane kantaba ko sharrin iska. Kisha koyi hamdala kana ki ɗauki sauran na cikin robar ki samu sarkakekken wurin da babu najasa kiyi niya da duk matsalarki kiyi wanka. Wlh da izinin Ubangiji zakiji sauƙi ki samu sauyi anaso na farko dai kiyishi da Zam-zam inda hali duk bayan wata shida ko shekara ɗaya kiyi kiyiwa yaranki da mijinki dan makarine mai girma in ba hali saboda tsadar da Zam-zam keyi in kinyi na forkon da Zam-zam to na biyu kiyi da ruwan sama na uku da duk ruwan da ya sauwaƙa gareki, inda hali ko yaushe da Zam-zam in ba hali ayi na forkon da Zam-zam in bai samuba ayi da ruwan sama na roƙon da na biyun da na ukun, kiyishi maƙo maƙo ko wata wata ana dai son duk bayan wata shida ko shekara ɗaya kiyi, yar uwa ko ɗanki, ƴarki mijinki ƙanwarki ƴaƴan yar uwa ki ko ɗan uwa duk inda kukaga yaro ko yarinya sun cika rashin ji gagara rawan kai gardama da alamun kwaucewa hanya kuyi masu yanada matuƙar fa'ida da falala, sadakace fisabilillahi idan kinji daɗinshi kiyi niya kiyiwa Mahaifiyata Fatima Dedde na ƙu'huwa ƙafa uku da fatan Allah ya jiƙanta ya kai haske da ni'ima Qabarinta. Ni kuma inada wata buƙata mai girma da falala da daraja a wurin Allah kuyi min addu'a kisa yaranki suyi min addu'a kice su roƙawa Aysha Aliyu Muhammad Garkuwa Allah ya biya mata buƙatarta akan alkhairi, ya raya mata ƴaƴanta Muhammad Jabeer da Maimuna Ikhram da Ibraahim ya shirye su ya basu ilimi mai amfani da albarka yasa su zama abin alfahari ga Musulunci da Musulmai mazan ya basu mata na gari da zuraya ɗaiyi ba, macen ya bata miji na gari da zuri'a ɗaiyiba, kana Allah ya bani wasu ƴaƴan masu albarka da nisan kwana tagwaye inyiwa Deddena takwara da Babana in samu Aliyu Haiydar da Fatima Khausar in samu auta A'isha takwarar kakata mafi soyuwa*
Man Lima da Hajja Nana ma bayan sunyi sallar la'asar da Baffa Liman da Yah Abba suka kama hanyar komawa Jauro Yaya.
Acan ɓangaren Hajiya Bunayya ma tunda tasha wannan ruwan tofin sai tsutsotsin suka yawaita fita yayin da suke cinta da gasken gaske sai dai tana shiga ruwan ɗumi zai lafa amma bazai wuce awa biyu zuwa uku ba zai sake dawowa haka tayi wannan yinin ranan zunibi da sakayyan aikinta na bibiyarta.
Daddare bayan sallar Isha'i Moddibo ne da Dr Jameel zaune afalon Hajiya Bunayya tana zaune Sai murtsukuku take yi akan kujeran jin yanda tsutsotsin ke cinta yayin da Amina ke zaune gefenta bisa duk kan alamu Alhamdulillah ta fara samun sauƙi har nishinma duk ta daina .
Anutse Dr Jameel ya kalli Hajiya Bunayya kana yace.
“Akwai tests ɗin da za'a Miki.
Sai kiyi ƙoƙari kije asibitu aduba ki acan”.
Cikin sanyi tace .
“Nagode Nagode Dr Jameel Allah ya saka da Alkhairi ”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Bakomai”.
Kana suka miƙe suka fita dai-dai lokacin kuma Dr Zakariyya da Asiya ne zaune amota suna hira fitowa su Dr Jameel ne yasa Asiya yiwa Dr Zakariyya sallama ta fita kana Dr Jameel ya shiga Motar.
Moddibo kuwa bayan Khausar dake shiga Side ɗin Momy ya nufa yana shiga falon yaga ba kowa sai Raudat dake kallon Catoon yace.
“Raudy ina Addah Khausy?”.
Hankalinta na kan kallon tace.
“Tana ɗakinta”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Momy fa?”.
Still idanunta na kan tv tace.
“Tana gidan Ummin Jameel Yah Haiydar ya kaita”.
Kai ya gyaɗa kana ya shiga ɗakin Khausar zaune ya sameta agaban Weldrop ɗin ta gabanta littafaine tana ta duddubawa.
Da mamaki ta kallesa kana tace.
“Yah Mu'allim har nan kuma?”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh ai gidan mune”.
Kai ta gyaɗa hannunta na kan littafin tace.
“Eh nasani ai yanzu in Momy tazo ta same mufa?”.
Murmushi yayi tare da shafa sajensa kana yace.
“Eh dai-dai kenan idan Momy tazo ta ganni zata san ina buƙatar matata zata kora min ke mu tafi tun da ke yanzu kin iya gardama da taurin kai ”.