← Book details Sakayyah Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 38

Sashe 3

Sakayyah Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Morocco Khausar ce kwance akan kujerar bisa alamu da Momy take waya cike da farin ciki ta gyara kwanciyarta tare da cewa.
“Momy In sha Allah mun kusa zuwa".
Murmushi Momy tayi kana tace.
“Toh Khausar me kike so in shirya miki idan kin zo.
Ga Raudhat baki ɗaya lissafinta da tunani Adda Khausy ta kusa daeowa.
da an taɓa ta sai tace sai Addah Khausy tazo, wanka ma ƙinyi tayi yau wai sai Addah Khausy tazo tayi mata”.
Dariya Khausar ta sanya tare da faɗin.
“Yau mun bonu kafin inzo ai datti zai kashe ki Raudat ”.
Ta ƙare faɗin haka jin muryan Raudat ta amshi wayar Raudat kuwa itama cikin dariya tace.
“Addah Khausy datti bazai kashe niba fa zan riƙa fesa turare sannan insa humran Momy saboda nayi kamshi sai kinzo ki min wanka”.
Dariya suka sanya Dukansu daga nan suka cigaba da hira.
Suna gama waya dasu Momy ga Mamaki ta sai ga kiran Hajja Nana ya shigo tana ɗagawa tace.
“My Kakus”.
Baki Hajja Nana ta taɓe tare da faɗin.
“Ƴar tselen Uwa tunda muka dawo sau ɗaya mukayi waya dake baki sake kirana ba”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Kai Hajja Nana kuma abin harda Sherri ne?
kin manta cewa garin ku babu network in baku kuka kira ba baya shiga, kullum fa kina raina”.
Dariya Hajja Nana tayi tare da faɗin.
“A yayi kyau yaushe zaku zo?”.
Cikin sauri tace.
“Next week”.
Cikin so da ƙauna Hajjaj Nana tace.
“Yau da kaina na ɗibo ƙafana har bidhiyar ƙare zancenka saboda inji Labarin Ƴar jikata dan nayi kewarki ina so in San yaushe zakuzo”.
Khausar na murmushi me ɗauke da ƙaunar Kakar tata tace.
“In sha Allah nan da kwana uku dai muna cikin Nigeria”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin.
“Toh Allah Ubangiji ya kawo ku kafiya”.
Bayan ta gama wayar ne ta miƙe ahankali kasancewar tun safe bata leƙa Didi ba kallon jikinta tayi ganin dogon riga ce budadde da mayafinsa babba yasa ta sauƙa falonta ta wuce Side ɗin Didi.

Tana shiga Falon ta samu Didi zaune da ahlinta, Modibbo Sai Zakariyya da Dr Jameel, Sai kuma Lalla Khadijah da Lalla Salma da Hafsat wanda ga duk kan alama sunzo tafiya bikin ne Didi na ganinta ta miƙa mata hannu idanunta akan cikinta,.
Sai lokacin itama ta kalli cikin ta ga Mamaki ta sai taga cikin nata har ya tura rigar ta kaɗan cikin jin kunya ta zauna gefen Didi cike da kulawa Didi tace.
“Barka da yamma?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Yawwa Barka dai Didi”.
Didi na gyara zama tace.
“Yau tun safe nake ta zuba ido zan ganki ban ganki ba ki shigo ba, nace Rahama taje ta du baki data dawo sai tace kina bacci”.
Tana kallon Moddibo tace.
„Eh Didi ina bacci ban daɗe da tashi ba shine nayi wanka sai kuma na ɗanyi waya da Momy na Momy tace in gaishe ki ma”.
Fuska a sake Didi tace.
“Ina amsa wa Masha Allah fatan suna lafiya?".
Kai ta gyaɗa tare da faɗin.
“Lafiya ƙalau”.
Ita kuwa Khausar kallonta ta mayar kan Lalla Khadijah da Lalla Salma da Hafsat cike da girmamawa ta gaishesu cikin sakin fuska suka amsa mata suna tambayar jiki.
Kallonta ta mayar kan Didi jin tana cewa.
“Khausar ya shirye-shiryen tafiya?”.
Dariya Khausar ta sanya tare da faɗin.
“Aini har na gama shirya wa ma”.
Ahankali Moddibo ya ɗago Idanunsa ya kalleta kana yace.
“Toh da kika gama shirin ma ai ke ba zuwa zakiyi ba”.
Zare idanunta tayi sai kuma ta kwaɓe fuska ahankali ta maida kallonta kan Didi dake murmushi tace.
“Didi kiji fa abinda yake cewa".
Ɗan dariya Didi tayi ganin yanda ta kwaɓe fuska yasa tace.
“Rabu dashi waya isa ya hana ki zuwa Mamana ai kece agaba idan baki zoba amaren ma baza su zoba”.
Ware idanu Dr Jameel yayi tare da sanya dariya yace.
“Anya kuwa Didi wannan zai saɓu dan bata jeba ace Amare baza su zoba ai ita ta zauna gidan mijinta mu muje mu ɗauko Matan mu". Cikin murmushi Zakariyya cewa.
“Gaskiya dai kam”.
Dariya Didi ta sanya kana tace.
“A'a Zakariyya har kaima wato zama da Jameelu ya dawo da kai mai surutu da baki”.
Dariya Lalla Khadijah ta sanya tare da faɗin.
“Aikam Didi Hausawa sunce zama da maɗaukin kanwa shi ke kawo farin kai".
Dariya suka sanya Lalla Hafsat ta karɓe da cewa.
“Aikam dai ko kurma ne ya zauna da Dr Jameel Sai ya koyi magana".
Zakariyya kuwa ƙeya ya sosa tare da sunkuyar da kai...

Ɗago kansu sukayi atare tare da kallon Ibraahim dake shigowa cikin mamaki suka haɗa bakin cewa.
“A'a Ibraahim kuma”.
Kai ya gyaɗa tare da buɗawa Rahama hannu wacce ta nufo kansa da gudu da murmushi afuskarsa yace.
“Surprise dama bazata na shirya muku Yah Jameel ba jiya muna waya kana zaton bazan zoba, har kana fushi”.
Ya ƙare maganar tare da ƙarasawa gefen Lalla Khadijah ya zauna kana ya ɗaura kansa kan kafadarta Dr Jameel cikin murmushi yace.
“Aikam da har nayi fushi da kai”.
Jujjuya idanu yayi yace.
“Amma dai yanzu ka huce ko?”.
Kai Dr Jameel ya gyaɗa tare da cewa.
“A na huce tunda kazo”.
Lalla Salma ce tace.
“Toh dama taya za'a yi Auren Yayun ka har biyu baka nan ai dole saida babban ƙanin ango za'a ɗaura Aure”.
Dariya yayi tare da faɗin.
“Aikuwa dai Lalla Salma kin gane”...
Haka dai suka cigaba da hiransu.
Chapter 3 · 0% Book details