← Book details Sakayyah Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 38

Sashe 4

Sakayyah Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Ana gobe zasu tafi da misalin karfe goma na dare Moddibo ne kwance a gefen Khausar yana romance ɗin ta tare da shafa cikinta ahankali ya ɗago Idanunsa ya kalleta tare da cewa.
“Gobe idan munje Nigeria gidan Innayi zamu sauƙa” .
Idanunta dake shanye kamar na mai jin bacci ta buɗe tare da tura baki tace.
“Yah Mu'allim gidan ku kuma? Nikam dai inje gidan Momyna ”.
Da sauri ya ware idanunsa tare da dafe ƙirjinsa kana yace.
“Na isa ki tafi kibarni da waye idan kin tafi gidan Momy?”.
Cikin tura baki tace.
“In barka da Innayin ka mana”.
Kissing ɗin goshinta yayi tare da cewa.
“Innayi zata bani abinda kike bani ne Minha?
Innayi bazata bani abinda kike bani ba Minha sabida duk duniya babu wanda yake bani abinda kike bani fa Minha ya za'a yi kice dan ina tare da wasu za kiyi nesa dani ai bazan iya jura ba”.
Ahankali ta fesar da numfashi tare da cewa.
“Kai Yah Mu'allim Kuma fa kasan nayi missing na Momy”.
Tafin hannunta ya riƙe cikin nasa yana matsawa yace.
“Nayi miki alƙwari idan munje kullum zan na kaiki ki wuni amma kwana bazan barki ba.
Babyna ma bazai iya ba saboda yana son ɗumin jikin Abbansa”.
Ta buɗe baki da niyar magana ta fasa jin wayarsa na ruri ahankali ya miƙe tare da janyota jikinsa yana shafa bayanta ganin number Sheikh Jabeer yasa ya dauka muryansa can ƙasa yace.
“Kai baka san dare yayi bane?".
Ware idanu Sheikh Jabeer yayi tare da cewa.
“Ƙaniyarka ne ni kake faɗawa dare yayi?”
Cikin kwaɓe fuska Modibbo yace.
“Toh Amman dai kasan inada iyali ko?”.
Wani irin murmushin mai cike da tuna baya Sheykh Jabeer yayi tare da cewa.
“Hmmm yaro man kaza da kake cemin bansan dare yayi bane shin baka san cewa duk abinda ɗanyen ganye ya sani ya kuma ganiba bushesh-she ya riga saba".
Murmushi Moddibo yayi tare da cewa.
“Can maka dai da karin maganar ka Ni ban fahimci me keke nufi ba".
Dariya Sheikh Jabeer yayi kana yace.
“Ai baza ka fahimta ba,
amma dai kasani duk abinda kake tunanin kasan shi na fika sanin shi kai abayana kake”.
Moddibo kuwa hannu ya cusa cikin sumar kan Khausar yace.
“Toh naji Ni dai yanzu ka faɗa min me yake tafe da kai ina da abinyi”.
Cikin so na kaka da jika Sheykh Jabeer yace
“Eh Ya maka kyau.
Dama akan batun number motar da kuka turo min ne tun jiya nayita kiranka baka ɗauka ba bansan me kake ba”.
Cikin sauri Moddibo ya dai-daita nutsuwarsa tare da cewa.
“Kuma banga Miss call ɗin ba”.
Cikin fesar da numfashi Sheik Jabeer yace.
“An samu motar cikin motocin da aka kamo sannan acikin mutanen ana so gane su waye ke amfani da motar dan mutanen kusan su ashirin da biyar aka kama.
Toh muna so mu gane su waye ke amfani da wannan motar sannan su waye suka sace Jameel suka kashe sa”.
Cikin fesar da numfashi da kuma rauni Moddibo yace.
“Alhamdulillah in Sha Allahu Jinin J bazai tafi abanza ba”.
Kai Sheikh Jabeer ya jinjina tare da faɗin.
“Yanzu shine abinda muke so tunda har ita mai ɗakin ka ta gansu tasan Fuskarsu tunda jibi kuna hanya idan kun iso kafin ku wuce sai munje kun gan su”.
Cikin sauri Moddibo ya runtse idanunsa yace.
“Yah Sheikh bana son ganinsu”.
Ahankali Sheikh Jabeer yace.
”Meyesa?”.
Araunane ya girgizar kai tare da cewa.
“Bana son ganin waɗanda suka kashe min J idan na gansu bansan me zanyi musu ba, kar nazo nima nayi abinda bashi bane, bansan mai zan musu ba, na tabbatar dai in na zan ga wanda ya kashe J.
Bazan iya barinshi arayeba zan iya yi musu komai”.
Cike da nutsuwa da dattako Sheikh Jabeer yace.
“In sha Allah babu abinda zaka musu dole zaku zo ku gansu ”.
Idanunsa na tara hawaye yace.
“Bazan gansu ba bazan iya ba har abada bana ƙaunar ganinsu.
Babu wa'anda na tsani gani a duniya sama dasu”.
Ahankali Khausar ta miƙe ta zauna Sheikh Jabeer kuwa ahankali yace.
“Toh ba laifi ku dai ku shirya idan kun zo sai kun biya nan”.
Kai ya gyaɗa tare da katse kiran sai kuma ya maida kallonsa kan Khausar cike da rauni lokaci ɗaya mutuwar Jameel ya dawo masa sabo idanunsa muryansa cike da sanyi da kuma rauni yace.
“Kinji fa waifa cewa yayi inje in Kalli waɗanda suka kashe min J.
Ina zan iya kallonsu?”.
Hannunta tasa ta tallafo kansa tare sa ɗaura aƙirjinta kana tace.
“Yah Mu'allim zamuje ko domin mu tabbatar da cewa suɗin ne suka kashe sa sannan mu tabbatar da cewa suɗinne an kamasu, sannan ayi musu hukunci dai-dai da laifinsu.
Ni na tabbatar muddin na gansu wallahi zan gane su da Izinin Ubangiji”.
Araunane ya girgiza kai tare da cewa.
“Muje kuma Minha?, Minha bazan iya ganin suba fa”.
Kansa ta tallafe tana ɗan shafa bayansa alamar kontar da hankali tace.
“Yah Mu'allim zamu iya zamu iya ganinsu kodan ahukuntasu abinsa cutar damu da sukayi”.
Zuciyarsa na ƙuna yace.
“Minha zan iya musu abinda basuyi tunani bafa”.
Sake tallafo kansa tayi tare da cewa.
“Yah Mu'allim babu abinda zaka musu hukumane za tayi aiki akansu kamar yanda Shari'a ta tsara”.
Ta ida maganar tana shafa kansa ganin yanda mutuwar Jameel ya dawo masa sabo ahankali ta haɗe lips ɗin su waje ɗaya wani gauron numfashi ya saki tare da janyo jikinsa ya fara shafa sassan jikinta ahankali ya ɗago kai ya kalleta tare da yin murmushi kana yayi ƙasa da rigar baccin jikinta muryansa ashaƙe yace.
“Minha kina ganin gaba ɗaya abin nan sai sake girma suke”.
Shanyayyun idanunta ta ɗago ta kallesa tare da sakin murmushi hannunta na shafa kansa tace.
“Yah Mu'allim ba dole su sake girma ba gaba ɗaya ka buwaye su ka gigita su sannan ka hanasu nutsuwa da kwanciyar hankali ”.
Hancinta ya lakace yace.
“Ba dole ba waɗan'nan kayan marmarin ai ba'a barinsu Minha suna da matsayi babba dama rashin samun hannu ne shiyasa basa girma sosai yanzu kuma kinga sun samu”.
Dariya tayi haka tayi ta yi masa abubuwan da suka mantar dashi damuwa da kuncin daya shiga haka suka kwana cikin farin ciki...

Ranan dasu tafi Misalin 12:00pm jirginsu ya tashi daga kasar Morocco zuwa Nigeria.
Kasancewar Private Jet ne shida Khausar suna First class daga can ƙarshe Zakariyya,Dr Jameel, Abualeey, Galadima, Waziri, suma na cikin First class daga gaba sai Innayi kana Didi, Lalla Khadijah da Lalla Hafsat duk suna baya.
Misalin ƙarfe biyar dai-dai jirginsu ya sauka a Adamawa kai tsaye motoci suka zo suka ɗauke su daga Airport zuwa fadan Mai martaba sarki Jabeer Nuruddeen Bubayaro.
Kyakkyawan masauki na musamman aka basu anan suka kwana bayan anyi musu tarbar na mutuntaka Didi takasance ga Mahaifiyarta da Mahaifinta sannan ga Ummi Kakarta Ummei Jakadiyarsu.
Washe gari da safe Misalin ƙarfe bakwai na safe Sheikh Jabeer da kansa ya wuce Masauƙin da aka bawa Moddibo da Khausar yana shiga ya samu Moddibo na haɗa mata tea.

Juyawa Moddibo yayi ya kallesa tare da faɗin.
“Wai ya kake shigo mana haka ba neman izini”.
Kallonsa Sheikh Jabeer yayi tare da cewa.
“Ka manta nan Fada tace ba Fadar kuba da zaka ce sai na nemi izini”.
Murmushi Moddibo yayi yana mikawa Khausar tea ɗin yace.
“Toh me kake nema da sanyi safiyar nan da kazo mana?”.
Sheikh Jabeer na gyara tsayuwar sa yace.
“Tashi zakuyi mu tafi inda zamuje”.
Langwaɓar da kai Moddibo yayi tare da faɗin.
“Ni bazan jeba”.
Cikin sauri Khausar tace.
“Kayi haƙuri Yah Mu'allim muje”.
“Gwara kam ki faɗa mishi muje mu tabbatar dan kada aɗaurawa wasu laifin da bana su ba”.
Haka dai suka ta lallaɓa Moddibo har ya amince suna fita sai ga Amintaccen Hadimin Sheikh Jabeer ya ɗauke su a mota suka tafi kurkukun dake cikin Yola suna isa bisa sirri akayi musu jagora da iso, aka wuce da ciki.
Chapter 4 · 0% Book details