← Book details Sakayyah Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 38

Sashe 36

Sakayyah Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Suna isa asibitin Dr Jameel da kansa ya karɓeta kana yayi mata duk gwaje-gwajen daya kamata nan yaga ashe tana da ciki har na tsawon uku batare da sun sani ba cike da farin ciki ya ɗagata sama ya riƙa juyata kafin ya sauƙeta cikin matsanancin farin ciki yace.
“Sweetheart albishir”.
Tana ɗan lumshe Idanunta tace.
“Goro”.
Wani kallo ya mata still fuskarsa ɗauke da Murmushi yace.
“Wani kalla”.
Ɗan ware idanunta tayi da kuma yanda zazzaɓin ya fara sauƙa tace.
“Fari ƙall”.
Sake rungumeta yayi kana yace.
“Ciki ne fa dake Sweetheart?”.
Cikin mamaki da wani irin farin ciki data kasa tantance yanayin da take ciki tace.
“Ciki?da gaske?”.
Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“Wallahi da gaske Sweetheart kina ɗauke da cikina ajikin cikin da muke muradi da mararin samu”.
Ahankali tace.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un?wata nawa?”.
Cikin farin cikin daya kasa ɓoyuwa asaman fuskarsa yace.
“Har wata uku fa”.
Da wani irin sauri ta ɗauki waya ta kira Ummi Ummi na ɗagawa tace.
“Ummi Ummi ina da ciki har na wata uku”
Cike da matsanancin farin ciki da jin daɗi Ummi tace.
”Alhamdulillah³ nayi farin ciki Ubangiji Allah ya raba lafiya kice na kusa zuwa”.
Murmushi Asma'u tayi kana tace.
“Yawwa Ummi dama kin daɗe baki zoba tun sunan Ayman baki sake zuwa ba dan haka kima fara shiri kin kusa zuwa”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh Allah yakai mu da lokacin rai da lafiya”.
Ameen ta amsa tare da katse kiran ta kira Khausar ta sanar mata murnan da Khausar tayi ba a cewa komai.

Ummi na gama waya da Asma'u ta kalli Bashir da Haiydar dake zaune gabanta wanda zuwa yanzu sun zama manyan Samari sun mallaki hankalin kansu.
Wanda tuni an gama maganar Auren Raudat da Bashir.
Haiydar kuma ya auri ƴar Aunty Ruƙayya.
sosai sukayi farin ciki jin Asma'u nada ciki kana atake awajen suka kirata suka tayata murna...

Zuwa yanzu kuwa Khausar ta haife cikinta, an samu ɗiya mace, ansa mata sunan Didi suna kiranta Eeman

Bayan watanni Allah ya sauƙi Asma'u lafiya ta samu ƴa mace wacce taci sunan mahaifiyar Dr Jameel A'isha suna kiranta Ishmah.
Anyi suna lafiya an gama Alhamdulillah Ummi da Mommy sunzo wajen suna.

*BAYAN SHEKARU ASHIRIN*
Alhamdulillah ƴaƴan su sun girma sun mallaki hankalin kansu an haɗa Auren Keyah da Ishmah ƴar Asma'u.
Sai Ayman da Mifra ƴar Ibraahim.
Alhamdulillah Raudat ma ta haifi ƴaƴanta mata biyu duk sun girma Hakeem ɗan Lalla Hafsat ya Auri Fatma ƴar Dija Haiydar kuma ya Auri Ruƙayya yarinyar Rahama.

Alhamdulillah rayuwa ta cigaba da tafiya tamkar yanda ake buƙata.
Bayan anyi biki an watse.
Ahankali Khausar ta shirya cikin shiga ta alfarma sai baza ƙamshi take sanye take cikin wasu tausasan rigar bacci masu masifar kyau da santsi idan ka ganta zaka yi zaton yau akayi Aurenta duk da cewa sun Aurar da ƴaƴan su amma tana da kyakkyawan jiki wanda Babu wanda zai ce ita ta haifi wannan yaran ga autarma Eeman an zama manyan ƴan mata wacce ba abinda ya bari na mahaifiyarta har rawan kan.

Anutse ta tura ƙofan bedroom ɗin ta ta shiga idanunta suka sauƙa akan Moddibo daya sake zama magidanci baza kayi zaton ya wuce 45years ba saboda kyawun jikinsa nutsuwa, jin daɗi kwanciyar hankali sun sake wanzuwa acikin rayuwarsu yana ganinta ya buɗe mata hannunsa anutse ta ƙara sa tsakiyan tare da faɗawa jikinsa ya mata wani Amintaccen runguma ahankali yake cusa yatsun ƙafansa aƙasan nata ganin haka yasa ta ɗaura ƙafafunta asaman rumfar ƙafansa anutse ya riƙa tafiya da ita har yaje bakin kofa yana isa ya rufe ƙofar saurin kallonsa tayi tare da cewa.
“Yah Mu'allim ya zaka rufe ƙofa”.
Goshinsu ya haɗe waje ɗaya still ƙafafunta na kan nasa yace.
“Um Minha Vidaa (My life) rufe wa zamuyi saboda kada _Aysha Aliyu Garkuwa_ ta shigo ta samu abin rubutawa Fan's ɗinta”...

Acan gidan Dr Jameel kuwa Asma'u ce zaune tare da ƴaƴanta wa'anda ta haifa bayan ta haifi Ishmah ƴaƴa maza guda biyu wanda ɗaya an yiwa Moddibo ta kwara suna kiransa da Moddibo sai takwaran Abban Jameel suna kiransa da Abba ahankali tace.
“Yah Moddibo”.
Anutse ya kalleta cike da girmamawa yace.
“Na'am Ummina”.
Tana gyara zamanta tace.
“Yaushe zakaje Nigeria ne?”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Ummi kwanan nan dai nake son zuwa amma nafi son mu tafi da Abba idan ya gama exams ɗinsa”.
Kai ta gyaɗa tare da faɗin.
“Toh ba matsala nima dama nayi kewar Ummina idan yaso zamu tafi tare”.
Dr Jameel dake gefe yai mata wani kallo mai cike da so kauna yace.
“Nima ɗin dani za'a je saboda nayi kewar Abbana da Ummina”.
Hira suka cigaba dayi mai cike da farin ciki da ƙaunar junansu...
Acan bangaren Ibraahim rayuwa tayi musu daɗi da matarsa.

Haka bangaren Asiya ma Alhamdulillah rayuwa na tafiya cikin farin ciki da kwanciyar hankali ɗan ta ya Auri ƴar Amina da suka haifa da tsohonta...
Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya hankali ya kwanta ya kowanne ɓangaren...

_TAMAT BIHAMDULILLAHI..._ Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Na godewa Allah daya bamu aron rai da lfy da lokaci da dama ya nuna mana forkon littafin nan lfy tare da aramana daman ganin ƙarshensa lfy dani daku masu karatu. Toh Alhamdulillah. Yah Allah mun gode maka, muna kuma neman yafiyarka da gafararka da rahamar ka, Yah Allah ka yafe min kurakuran dake cikin wannan littafin ka shafe zunubaina kayi min gafara da rahama da jinƙai dani da masu karatu. Abinda mai dai-dai Ya Allah ka haɗamu a kan ladan, ya Allah ka nuna mana forkon wanda zan fara lfy da ƙarshensa duk lfy, ya hayyu ya ƙayyum kasa al'ummar Annabi su amfana da alkhairan dake cikin littatafai na ka tsaresu da sharrin dake ciki.
*Yafiya! Yafiya!! Yafiya!!!*
*Ina mai neman yafiyarku makarantan littatafai na, mace ko namiji babba ko yaro wacce muka taɓa mgn da ita da wacce bamu taɓa mgn da ita, na kusa dani dana nesa. Wala Allah akwai abinda nai Miki ko nai maka ko cikin rashin sani ko ajizanci ko kuma yanayin gajiyawa da raunin ɗan adam ki kuma yanayin ɗan fusatan lissafi ko gaza danne fushi, Ka! Ku! Ki! Haƙuri ku yafe min, kuyi min azurun na fama da yawan jama'a, ni na yafewa duk wacce taimin abu cikin rashin sani, Amman wlh ban yafewa masu fitarmin littafina su tura a wasu groups ɗin ba domin misali ka bawa ɗan uwanka mutum ɗaya biyu wannan da banner da turawa a groups mutum dari ko sari biyu ko uku ku dari hudu ai wannan kai kankama kasan me sunanka madadin samun wani suyi Murmushin group a kuma kwashi zunubi*

*Littafin Sakayya dai kowa ya sani na kuɗine, in ma kin ganshi a wani wurin to na satane kika karanta 1k ne kacal, 0661110170 GTBANK Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyanki ta Whatsapp number na 09097853276. In tura Miki littafin complete Kisha karatun ki ba haƙin kowa a kanku*

*Gareku masu son kayan mata ko turarukan wuta da kulacca da su Humra a wannan no ɗin ne zakuyi min mgn 08069423567 in kuma kuɗi zaki tura to ta account in na na Jaiz bank zaki tura. 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min shaidar biyanki ta Whatsapp number na na 08069423567, in haɗa Miki kayanki in tura Miki shi duk state da kike nama lfy fata lfy**WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_
_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 08069423567 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._

🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*
Chapter 36 · 0% Book details