Sashe 7
Sakayyah Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Washe gari bayan sun kammala breakfast da duk wani abu da za suyi Kai tsaye sashen su Didi suka shiga bakinsu ɗauke da sallama suka shiga bayan sun gaigaisa Moddibo ya kalli Didi tare da cewa.
“Didi zamu je wurin Momy”.
Kai Didi ta gyaɗa kana tace
“Ok sai munzo muma yanzu Ummin Jameel zata zo mu taho tare”.
Kai ya gyaɗa yana ɗan matsa hannun Khausar yace.
“Toh shikenan sai kun zo”.
Daga nan suka miƙe suka fito da kansa ya shiga mazaunin driver, kana ta shiga gefen mai zaman banza, cikin nitsuwa yaja suka tafi anutse yake driving yana Jin wani yanayi na daban.
Titinan garin ya zubawa ido lokaci ɗaya kuma tunanin J ɗinsa ya faɗo masa sai kuma yake tuna Lokuta da dama Idan yana tuƙi J na gefensa ko kuma J na tuƙi shi yana gefensa jikinsa ne yayi sanyi, tafin hannunta ya riƙo tare da mannawa kan cikinta yayi shiru kwayar idanunsa na tsats-tsafo da ruwan hawaye.
Tuni ta fahimci yanayin da yake ciki cikin sanyi da rauni tace.
“Allah ya jiƙan Yah Jameel Allah ya mishi Rahma Allah ya gafarta masa”
Araunane yace.
“Ameen Ya Allah Minha”.
Tana matsa hannunsa dake cikin nata tace.
“Yah Jameel yanzu baya buƙatar kukan nu addu'ar mu yake buƙata”.
Cikin ƙoƙarin hana hawayen sa zuba yace.
“Nima haka nakeso ina ta ƙoƙarin hana zuciyata da Idanuna kuka akan J sai dai muyi ta mishi addu'a Amman wasu lokutan ina gaza hana kaina hawaye a kanshi saboda nayi rashine da har yau ban samu madadinsa ba”.
Cikin tausasawa tace.
“Na sani Yah Mu'allim to Amman Allah ya fimu sonshi, kuma dama shi ya bamu shi dan haka addu'a kawai zamuyi ya mishi”.
Cikin sanyi yace.
“In sha Allah za muyi masa”.
A kuma Dai-dai lokacin mai gadi ya buɗe musu gate ɗin gidan Lamiɗo Parking yayi kana suka fita da sauri ta nufi harabar gidan da nufin gudu,
saurin riƙo hannunta yayi cikin tsira mata idanu ya langwaɓar da kai yace.
“Kar kiyi gudu mana wai ke bakya jin tsoron ki faɗine”.
Kai ta ta gyaɗa tace.
“Toh ai sauri nake inje inga Momy".
Sake langwaɓar da kai yayi yace.
“Ai zaki ganta Minha ba sai kinyi gudu ba tun da gaki cikin gidan”.
Ko gama rufe baki baiyi ba ta hango Raudat riƙe da Comb da kifiya bisa alamu kitso zata tafi.
Da sassarfa ta nufeta tana kiranta,
Ita kuwa Raudat jin muryar Adda Khausy tane yasa ta ɗago kanta aiko ganinta ne yasa ta buga tsalle cike da matsanancin farin ciki tace.
“Addah Khausy”.
Da wani irin sauri Khausar ta janye hannunta dake cikin nasa ta ruga da gudu.
Atsorace ya sanya tafin hannunsa biyu ya dafe kansa kana ya motsa laɓɓansa tare da faɗin.
“Ya Salam ki daina gudun nan”.
Ina bata saurareshi ba da gudu ta rungume Raudat Raudat kuwa tsalle ta riƙa yi ajikinta tana cewa.
“Oyoyo! Oyoyo Addah Khausy!, Mommy Addah Khausy!! Tazo Addah Khausy!!!,Oyoyo”.
Cike da matsanancin farin ciki Khausar ta ɗaga ta sama ta riƙa juyawa da ita a tsakiyar gida wanda hakan ne yasa baki ɗaya mutanen gida suka san cewa Khausar tazo.
Dai-dai lokacin kuma Haiydar ya fito daga ɗakinsa.
Da gudu Sulaiman ma ya fito daga sashen Hajiya Bunayya atare suka rungumeta suna faɗin.
“Oyoyo Addah Khausy ”.
Khausar kuwa cike da matsanancin farin ciki take jujjuyawa atsakiyarsu ruggume da Raudat tsam a jikinta.
Jin sowarsunw yasa Momy dake zaune falonta ta miƙe da sauri ta fito jin sautin muryansu na tashi cak ta tsaya ta riƙe ƙafan Falon tare da tsirawa Khausar idanu tana kallonta cike da so, ƙauna, bege, kewa irin na uwa da yarta.
Khausar kuwa sai juyawa take dasu tana ƙyalƙyala dariya sai kuma tayi saurin sake su ta nufi Momy tana gudu tare da faɗin.
“Oyoyo Momyna”.
Runtse idanunsa yayi sai kuma ya ɗan ɗaga saitin muryansa yace.
“Dan Allah Momy kice mata ta daina gudun nan zata yiwa kanta Illah fa”.
Murmushi Momy tayi tare da kallon Khausar kallo ɗaya ta mata ta fahimci tana da ciki wanda har ya ɗan tasa ga wani irin kyau da tayi sai ƙelli take zubawa ga ɗan cikinta daya turo gwanin kyau ya zauna a jikinta cib da cib sai ƙugunta da ya ƙara faɗi.
Cikin sauri da bege Minti ta rungumeta asanda ta isa gareta sau kuna tace.
“Ke meyesa bakya girmane. Khausar wannan guje-guje har yanzu baki barshi ba”.
Murmushi tayi tare da sake Momy sai kuma ta sake rungumeta kana ta sake ta ta kuma sake rungumeta ɗan turata Momy tayi tare da faɗin.
“Ni matsa ahanya Bismillah Moddibo shigo".
Sai alokacin Haiydar ya miƙawa Moddibo hannu kana yace.
“Yah Moddibo Bismillah mu shiga”.
Kai Moddibo ya gyaɗa suka shiga bayan sun zauna a falo Momy da kanta ta kawo musu Drinks da Snacks da ruwa ta ajiye musu agabansu.
Raudat kam cike da farin ciki ta kwanta kan Khausar tana ta nuƙurƙusata,
ahankali Moddibo ya riƙo tafin hannunta yace.
“Kiyi haƙuri Aunty Raudiy adaina danne Adda Khausy kar aji mata ciwo”.
Cikin jin daɗi Momy ta kawar da kanta jin yanda yake mata magana cike da kulawa sai kuma ta miƙe tace.
“Bismillah kusha ruwa bari nazo ”.
Ta ƙarashe maganar tana fita kai tsaye bedroom ɗin ta ta wuce.
Acan ɓangaren Hajiya Bunayya kuwa a dai-dai lokacin zaune take aruwan zafi idanu ta tsirawa ruwan tana kallon ƙananun tsutsotsin farare masu jajayen kai wanda ga duk kan alamu sune suke addabar ta da jarabar ƙaiƙayi wanda zuwa yanzu tsakaninta dubaranta da gabanta ya wawake tuni sun fafeta ta kashin ta da gabanta ya haɗe saboda masifar ƙaiƙayi da yanda suke cinta taje asibiti har ta gode Allah abanza kana ta kira matar data haɗa su da Boka Gillaw.
Taje ta faɗawa Boka Gillaw ga abinda yake faruwa yace wannan sakamakon aikin su suke girba babu abinda zai iya kada su sake kiransa, dama shi ya gaya musu idan buƙata ta biya su biya kuɗi idan kuma bai biya ba shikenan suji da kansu.
Matar ta tambaye shi mai zai basu amma yace babu abinda zai basu wannan Sakayyar sune babu wanda ya isa ya kawar da Sakayyar zunubansu ne ya sauka akan su Babu ruwansa suji da kansu shima yaji da kansa.
Tuno waɗanan maganganun ne yasa ta fashe da marayan kuka mai cike da nadama mara amfani, tana cikin kukan ta jiyo sautin muryoyi ana cewa Oyoyo Addah Khausy ahankali ta juye ruwan tana kallon tsutsotsin masu masifar gudu da ƙaiƙayi dole sai ta shiga ruwan ɗumin ne take ɗan jin sauƙi.
Tana fitowa daga Bathroom ɗin ta zaune gefen Amina dake kwance kan gadon wacce ta rame ta zama wata halitta daban kamar ƙwarangwal tana nan tamkar wacce babu numfashi ajikinta kuka ta fashe dashi tare da cewa.
“Amina kinga Sakayyar abinda mukayi ko. Ubangiji ya kama mu tun a duniya Allah ya kamu da Sakayyar tarin zunubanmu Amina ya zamuyi?”.
Araunane Amina ta ɗago kanta cikin muryanta da baki ɗaya ya koma na wata halitta ta kalleta duk ta disashe baki ɗaya kamanninta da siffofinta ya fara zama na maciji ne ko menene dai ho da kyar ta buɗe bakinta tace.
“Umma munemi gafarar wa'anda muka cutar tun kafin dare ya mana ”.
Cikin rauni da zubda hawaye Hajiya Bunayya tace.
“Dole ma mune mi gafarsu su yafe mana nasani wannan Sakayyar abinda nata yiwa wannan baiwar Allah ne, da abinda nayi wa ƴarta da kuma yanda nayi ta zubar mata da ciki sannan nasa aka kashe Ramadan yanzu shine Allah ya jarabceni da wannan abin”.
Kuka sosai Amina ta fashe dashi tana ji kamar adawo mata da lokacin baya ta gyara kuskurenta.
Ita ma Hajiya Bunayya kuka ta fashe dashi Asiya ce ta shigo ta zauna gefen su ta shiga rera kuka cikin rauni da tausayinsu tace.
“Umma ku nemi gafarar Momyn Khausar da Khausar duk wanda ku kasan kun cutar kunemi gafarar su Allah gafururrur rahim ne shima zai yafe muku sai kuma ku nemi gafarar Allah akan shirka da kuka yi Allah ya yafe muku ”.
Cikin raunin Murya da shesh-sheƙa Amina ta gyaɗa mata kai tare da faɗin.
“In sha Allah zamu nema amma Addah Asiya ki taya mu basu haƙuri ”.
Kai Asiya ta gyaɗa tare da cewa.
„In sha Allah yanzu ma mukayi waya da Samira Sani take cemin itama jiya baki ɗaya Momyn ta kwana tayi tana ta ihu acikin gida gaba ɗaya tazama kamar mahaukaciya, ita tana jin tsoro yanzu zata dawo nan ma”.
Atsorace Hajiya Bunayya ta dafe kuncinta tace.
“Yau sun shiga ukunsy Hajiya Lami fa ta haukacene”.
Cikin sanyi da zubda hawaye Asiya tace.
“Haka dai alamu suka nuna Umma Allah ya yaye muku ya dubeku da idon Rahama”.
Cikin rauni da tarin tsoro Hajiya Bunayya tace.
“Ameen”.
Amina kam sai hawaye take tana nadama da danasanin abinda ta aikata.
“Didi zamu je wurin Momy”.
Kai Didi ta gyaɗa kana tace
“Ok sai munzo muma yanzu Ummin Jameel zata zo mu taho tare”.
Kai ya gyaɗa yana ɗan matsa hannun Khausar yace.
“Toh shikenan sai kun zo”.
Daga nan suka miƙe suka fito da kansa ya shiga mazaunin driver, kana ta shiga gefen mai zaman banza, cikin nitsuwa yaja suka tafi anutse yake driving yana Jin wani yanayi na daban.
Titinan garin ya zubawa ido lokaci ɗaya kuma tunanin J ɗinsa ya faɗo masa sai kuma yake tuna Lokuta da dama Idan yana tuƙi J na gefensa ko kuma J na tuƙi shi yana gefensa jikinsa ne yayi sanyi, tafin hannunta ya riƙo tare da mannawa kan cikinta yayi shiru kwayar idanunsa na tsats-tsafo da ruwan hawaye.
Tuni ta fahimci yanayin da yake ciki cikin sanyi da rauni tace.
“Allah ya jiƙan Yah Jameel Allah ya mishi Rahma Allah ya gafarta masa”
Araunane yace.
“Ameen Ya Allah Minha”.
Tana matsa hannunsa dake cikin nata tace.
“Yah Jameel yanzu baya buƙatar kukan nu addu'ar mu yake buƙata”.
Cikin ƙoƙarin hana hawayen sa zuba yace.
“Nima haka nakeso ina ta ƙoƙarin hana zuciyata da Idanuna kuka akan J sai dai muyi ta mishi addu'a Amman wasu lokutan ina gaza hana kaina hawaye a kanshi saboda nayi rashine da har yau ban samu madadinsa ba”.
Cikin tausasawa tace.
“Na sani Yah Mu'allim to Amman Allah ya fimu sonshi, kuma dama shi ya bamu shi dan haka addu'a kawai zamuyi ya mishi”.
Cikin sanyi yace.
“In sha Allah za muyi masa”.
A kuma Dai-dai lokacin mai gadi ya buɗe musu gate ɗin gidan Lamiɗo Parking yayi kana suka fita da sauri ta nufi harabar gidan da nufin gudu,
saurin riƙo hannunta yayi cikin tsira mata idanu ya langwaɓar da kai yace.
“Kar kiyi gudu mana wai ke bakya jin tsoron ki faɗine”.
Kai ta ta gyaɗa tace.
“Toh ai sauri nake inje inga Momy".
Sake langwaɓar da kai yayi yace.
“Ai zaki ganta Minha ba sai kinyi gudu ba tun da gaki cikin gidan”.
Ko gama rufe baki baiyi ba ta hango Raudat riƙe da Comb da kifiya bisa alamu kitso zata tafi.
Da sassarfa ta nufeta tana kiranta,
Ita kuwa Raudat jin muryar Adda Khausy tane yasa ta ɗago kanta aiko ganinta ne yasa ta buga tsalle cike da matsanancin farin ciki tace.
“Addah Khausy”.
Da wani irin sauri Khausar ta janye hannunta dake cikin nasa ta ruga da gudu.
Atsorace ya sanya tafin hannunsa biyu ya dafe kansa kana ya motsa laɓɓansa tare da faɗin.
“Ya Salam ki daina gudun nan”.
Ina bata saurareshi ba da gudu ta rungume Raudat Raudat kuwa tsalle ta riƙa yi ajikinta tana cewa.
“Oyoyo! Oyoyo Addah Khausy!, Mommy Addah Khausy!! Tazo Addah Khausy!!!,Oyoyo”.
Cike da matsanancin farin ciki Khausar ta ɗaga ta sama ta riƙa juyawa da ita a tsakiyar gida wanda hakan ne yasa baki ɗaya mutanen gida suka san cewa Khausar tazo.
Dai-dai lokacin kuma Haiydar ya fito daga ɗakinsa.
Da gudu Sulaiman ma ya fito daga sashen Hajiya Bunayya atare suka rungumeta suna faɗin.
“Oyoyo Addah Khausy ”.
Khausar kuwa cike da matsanancin farin ciki take jujjuyawa atsakiyarsu ruggume da Raudat tsam a jikinta.
Jin sowarsunw yasa Momy dake zaune falonta ta miƙe da sauri ta fito jin sautin muryansu na tashi cak ta tsaya ta riƙe ƙafan Falon tare da tsirawa Khausar idanu tana kallonta cike da so, ƙauna, bege, kewa irin na uwa da yarta.
Khausar kuwa sai juyawa take dasu tana ƙyalƙyala dariya sai kuma tayi saurin sake su ta nufi Momy tana gudu tare da faɗin.
“Oyoyo Momyna”.
Runtse idanunsa yayi sai kuma ya ɗan ɗaga saitin muryansa yace.
“Dan Allah Momy kice mata ta daina gudun nan zata yiwa kanta Illah fa”.
Murmushi Momy tayi tare da kallon Khausar kallo ɗaya ta mata ta fahimci tana da ciki wanda har ya ɗan tasa ga wani irin kyau da tayi sai ƙelli take zubawa ga ɗan cikinta daya turo gwanin kyau ya zauna a jikinta cib da cib sai ƙugunta da ya ƙara faɗi.
Cikin sauri da bege Minti ta rungumeta asanda ta isa gareta sau kuna tace.
“Ke meyesa bakya girmane. Khausar wannan guje-guje har yanzu baki barshi ba”.
Murmushi tayi tare da sake Momy sai kuma ta sake rungumeta kana ta sake ta ta kuma sake rungumeta ɗan turata Momy tayi tare da faɗin.
“Ni matsa ahanya Bismillah Moddibo shigo".
Sai alokacin Haiydar ya miƙawa Moddibo hannu kana yace.
“Yah Moddibo Bismillah mu shiga”.
Kai Moddibo ya gyaɗa suka shiga bayan sun zauna a falo Momy da kanta ta kawo musu Drinks da Snacks da ruwa ta ajiye musu agabansu.
Raudat kam cike da farin ciki ta kwanta kan Khausar tana ta nuƙurƙusata,
ahankali Moddibo ya riƙo tafin hannunta yace.
“Kiyi haƙuri Aunty Raudiy adaina danne Adda Khausy kar aji mata ciwo”.
Cikin jin daɗi Momy ta kawar da kanta jin yanda yake mata magana cike da kulawa sai kuma ta miƙe tace.
“Bismillah kusha ruwa bari nazo ”.
Ta ƙarashe maganar tana fita kai tsaye bedroom ɗin ta ta wuce.
Acan ɓangaren Hajiya Bunayya kuwa a dai-dai lokacin zaune take aruwan zafi idanu ta tsirawa ruwan tana kallon ƙananun tsutsotsin farare masu jajayen kai wanda ga duk kan alamu sune suke addabar ta da jarabar ƙaiƙayi wanda zuwa yanzu tsakaninta dubaranta da gabanta ya wawake tuni sun fafeta ta kashin ta da gabanta ya haɗe saboda masifar ƙaiƙayi da yanda suke cinta taje asibiti har ta gode Allah abanza kana ta kira matar data haɗa su da Boka Gillaw.
Taje ta faɗawa Boka Gillaw ga abinda yake faruwa yace wannan sakamakon aikin su suke girba babu abinda zai iya kada su sake kiransa, dama shi ya gaya musu idan buƙata ta biya su biya kuɗi idan kuma bai biya ba shikenan suji da kansu.
Matar ta tambaye shi mai zai basu amma yace babu abinda zai basu wannan Sakayyar sune babu wanda ya isa ya kawar da Sakayyar zunubansu ne ya sauka akan su Babu ruwansa suji da kansu shima yaji da kansa.
Tuno waɗanan maganganun ne yasa ta fashe da marayan kuka mai cike da nadama mara amfani, tana cikin kukan ta jiyo sautin muryoyi ana cewa Oyoyo Addah Khausy ahankali ta juye ruwan tana kallon tsutsotsin masu masifar gudu da ƙaiƙayi dole sai ta shiga ruwan ɗumin ne take ɗan jin sauƙi.
Tana fitowa daga Bathroom ɗin ta zaune gefen Amina dake kwance kan gadon wacce ta rame ta zama wata halitta daban kamar ƙwarangwal tana nan tamkar wacce babu numfashi ajikinta kuka ta fashe dashi tare da cewa.
“Amina kinga Sakayyar abinda mukayi ko. Ubangiji ya kama mu tun a duniya Allah ya kamu da Sakayyar tarin zunubanmu Amina ya zamuyi?”.
Araunane Amina ta ɗago kanta cikin muryanta da baki ɗaya ya koma na wata halitta ta kalleta duk ta disashe baki ɗaya kamanninta da siffofinta ya fara zama na maciji ne ko menene dai ho da kyar ta buɗe bakinta tace.
“Umma munemi gafarar wa'anda muka cutar tun kafin dare ya mana ”.
Cikin rauni da zubda hawaye Hajiya Bunayya tace.
“Dole ma mune mi gafarsu su yafe mana nasani wannan Sakayyar abinda nata yiwa wannan baiwar Allah ne, da abinda nayi wa ƴarta da kuma yanda nayi ta zubar mata da ciki sannan nasa aka kashe Ramadan yanzu shine Allah ya jarabceni da wannan abin”.
Kuka sosai Amina ta fashe dashi tana ji kamar adawo mata da lokacin baya ta gyara kuskurenta.
Ita ma Hajiya Bunayya kuka ta fashe dashi Asiya ce ta shigo ta zauna gefen su ta shiga rera kuka cikin rauni da tausayinsu tace.
“Umma ku nemi gafarar Momyn Khausar da Khausar duk wanda ku kasan kun cutar kunemi gafarar su Allah gafururrur rahim ne shima zai yafe muku sai kuma ku nemi gafarar Allah akan shirka da kuka yi Allah ya yafe muku ”.
Cikin raunin Murya da shesh-sheƙa Amina ta gyaɗa mata kai tare da faɗin.
“In sha Allah zamu nema amma Addah Asiya ki taya mu basu haƙuri ”.
Kai Asiya ta gyaɗa tare da cewa.
„In sha Allah yanzu ma mukayi waya da Samira Sani take cemin itama jiya baki ɗaya Momyn ta kwana tayi tana ta ihu acikin gida gaba ɗaya tazama kamar mahaukaciya, ita tana jin tsoro yanzu zata dawo nan ma”.
Atsorace Hajiya Bunayya ta dafe kuncinta tace.
“Yau sun shiga ukunsy Hajiya Lami fa ta haukacene”.
Cikin sanyi da zubda hawaye Asiya tace.
“Haka dai alamu suka nuna Umma Allah ya yaye muku ya dubeku da idon Rahama”.
Cikin rauni da tarin tsoro Hajiya Bunayya tace.
“Ameen”.
Amina kam sai hawaye take tana nadama da danasanin abinda ta aikata.