Sashe 8
Rantsatstsen Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yace "Nagode ma Allah da wannan baiwar da yayi mani ta yarinya, ma tsananin biyayya gareni, Ina rokon Allah kema ya baki waɗanda zasuyi miki biyayya kamar yanda kike min Allah ya shiga cikin al’amarinki, ya kula min dake"
A zuciyarta ta amsa da amin.
Ya ciga ba da cewa, "Allah yasa inda zakije ya kasance kinsamu rayuwa wadda baki samu ba a nan, ki dage da addu’a, ki riqe mutuncinki, ki kama kanki, Inshaa Allah zakiyi rayuwa wadda tafi wadda kikeyi a nan, a jikina nake jin inda zaki rayuwarki zata inganta kamar yanda nake mafarki da fata"
"Allah yasa babana, amma zuciyata zata kasance cikin kewan abunda tafi ƙauna da muradi"
Murmushi yayi yace "Da taji tana muradin babanta ta kirashi a waya, shiɗin zai kasance mai karfafa mata guiwa har ta cimma nasara a rayuwa..."
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO 🦋 ✨
BY RABIA'TU KABIRU ACHADU (FULANI)
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE KI HALIMA HASHEEM (MIEMIEN HABIBI)❤️ & AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI) ♥️
FULANI ❣️
08082101373
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO 🦋 ✨
PAGE 9️⃣
Kasancewar baya son hankalin zainu ya dawo kansu balle taji ko da kaɗan ne daga shirin su, duk da ma komai yazo ƙarshe, amma so yake ya shayar da su mamaki daga ita har Hajjah, domin so yake sai sun fito zata tafi kawai suji labari, dan yasan lokacin zasu tabbatar da ya shammace su, Shi ya sa yace mata ta tashi taje ta cigaba da shiryawa, shi zai je wurin Malam Sale yaji tafiyar tana nan karfe goma ɗin ko kuwa, dan shi hankalin shi ba zai kwanta ba sai ya tabbatar da ta bar garin.
Da toh ta amsa mishi ta miƙe suka fito kusan tare.
Dogon tsaki Baba Zainu taja cike da masifa tace "Aini ba za'a burgeni ba sai naga ka maidata ciki sannan zan tabbatar da girman son da kake mata, aikin banza kawai"
Girgiza kanshi yayi ya ficewar shi ya barta tana ɓaɓatu ita kaɗai domin Hajjah har lokacin bata fito ɗaki ba.
Itama ma Maryamah hanyar ɗakin ta tayi, dan da gaske take yau bata da lokacin matar, in kuma ta buɗe bakinta akan ta tofa abunda zai fito daga bakinta ita kanta sai tayi danasanin tankawa balle kuma ita baban, cire kayan jikinta tayi ta ɗaura zani ta fito zata shiga wanka, amma yanda ta samu bayin takaici sai da ya kusan sakata kuka, domin kaca-kaca haka yayi saboda yau batayi sammakon wankewa ba kuma ba za'a samu wani ko Zainab ta sanya ruwa ta kora dattin ciki ba, saida ta tsaya ta wanke bayin tass sannan ta shiga wankan, Bayan ta fito ta shirya cikin atamfarta ta sallah mai sauƙin kuɗi, kasancewar su masu rangwamen ƙarfi, amma duk da haka babanta na iya bakin ƙoƙarin shi wurin yi mata sutura, saboda yace ai macece ita kuma mace sai da sutura domin sutura ita ce mutum, haka ta shirya tsaf abunta kuma tayi masifar kyau duk da damuwar dake cin ranta, a hakan be hana kyawunta fitowa ba. fuskarta tayi fayau, kwalli ta shafa ta sanya man leɓe kasancewar bata mu’amala da hoda.
Tana cikin shirin ta jiyo sallamar Aisha a tsakar gida, inda kuma ta jiyo muryar Baba Zainu tana cewa "wai zaryar uban me ake mana a cikin gida tun jiya? Ni fa munafurci ne, bana so tunda ai ba zuwa kike ba da ko yanzun wani munafuncin ake ƙullawa yasa kiketa faman yi mana zarya"
Ƙaramin tsaki Aisha taja tayi wucewarta ɗakin Maryamah.
"Kinwa uwar ki buntalo tsaki bani ba, shegiyar yarinya mai kama da shaiɗanu"
Hayaniyar tace ta fito da Hajjah tana faɗin "Ke kam Zainu baki taɓa bari mutum ya rintsa, yanzun gidan ke kaɗai ma sai kin yi hayaniya, dan nasan dai yara sun tafi makaranta haka waccan kafurar ma yar allazee boko"
"Ina fa ta tafi? yau bansan munafurcin daya hanata zuwa makarantar da take jin ta kamar ɗakin uwarta ba, shine waccan shegiyar yarinyar ta wajen buntalo ta zo ita kuma tana nata rashin tarbiyya, kin san ba tarbiyya gareta ba daga nace wai zaryar me take mana a gida tun jiya, shine yarinyar nan ta kalle ni ta buga tsaki"
★★★
Aisha kam da shigarta Maryamah ta tareta da "uwar ƴan ɗaukar magana, gashinan kin jawo ma ummana zagi da farar safiya"
"Ke kyale karyar can tayi tayi, aita saba, ko bance komai ba sai tayi, shiyasa ma nayi mata tsakin dan tayi da hujja"
"Aikin kyauta da kika jawo magana"
Zama sukayi suna gaisawa.
"Ƙarfe nawa ne tafiyar?" "Toh baba dai yace jiya Baba Sale yace mishi ƙarfe goma amma yaje yaji abunda zai ce"
"Ai goma ta kusa" ƙara kallon Maryamah tayi tace "sahiba Allah gara ma kibar gidan nan ko kunnuwanki su huta da jin mugun alƙaba’in matar can"
“Hmmn kibari kawai sahiba, ni kaina abunda nace kenan ɗazun da ta fara" ta bata amsa tana ɓata fuska.
Suna ciki sukaji maganar Hajjah tana fadin "ni bari na shiga barka gidan azumi, jikanyarta ta haihu, daman cewa nayi in bari sai ɗagawar hantsi.
A dawo lafiya Baba Zainu ta mata tana ci gaba da aikin da take, dan yau awara take son yi tunda Hassu tace yau zata dawo, daman gidan babanta taje ta kwana biyu.
Bayan fitar baba ko minti ashirin batayi ba baba ya shigo gidan da sallama.
Banza baba Zainu tayi dashi dan a ciki take dashi.
Shima bebi ta kanta ba ya karasa ƙofar ɗakin Maryamah yana faɗin, "Zainariya in kin shirya ki fito mu tafi, Malam Sale na jiranmu"
Ai kamar da baba yake tayi saurin sakin abunda take ta juyo gaba ɗaya hankalinta na a akanshi, shi kuma yayi kamar besan da wanzuwarta ba. Mamaki be isa kasheta ba sai da taga Maryamah ta fito da jaka ta kuma sanya kayan sallarta alamar garin dai zata bari, gaba ɗaya ta ma rasa me zata ce, ƙoƙari take ta kamo bakin zaren amma ta kasa.
Bayan fitowar Maryamah da Aisha ne Aishan tana tsugunna ta gaida baba, ya amsa yace "kinzo yima ƴar uwarki rakiya kenan?"
"Eh baba"
Gaba ɗaya fa Baba Zainu ta shiga duhu, to wai me malam yake nufi ne? Yarinyar nan garin zata bari ko kuwa wani wuri zata ta dawo? Bata kai ƙarshen tunaninta ba taji muryar Malam na magana kaman ya shiga zuciyar ta.
"Toh Zainu, Maryamah zata bar miki gidan yau dai saiki sakata ki wala, dan naga kamar ta tare miki iskan shaƙa, sannan abinda nake so ki sani shine, shi sharri ɗan aike ne, yanda ya tafi haka zai dawo wa meshi, kuma ɗa dakike gani na kowwa ne ba ki san mejin ƙanki ba,ƙila ita da kike gani a wulaƙance ita ce zata ja ki zuwa gaba, kuma kin matuƙar bani mamaki akan abunda naji kuna shiryawa, nina riƙe taki ƴar da amana amma ke kin gagara riƙe tawa, ke kenan kullum cikin neman hanyar da zata tozarta, toh da izinin Allah Maryamah ba zata taɓa kauce hanya ba, kuma a duk inda take addu’ata tana tare da ita, zata tafi zata barmiki gidan kici uwar da zakici da shi"
Yana gama faɗin haka ya sanya hannu ya ɗauki jakar Maryamah yace "ku shige mu je"
Ko zarafin magana be bata ba, toh ta ina ma zata iya magana bayan tayi freezing, atoh tayi freezing mana gaba ɗaya ta daskare , abubuwa ne suka taru suka haɗe mata, na farko barin da Maryamah zatayi ma garin ba tare da ta cika burinta ba, na biyu yanda aka shammaceta akan tafiyan, sai kuma na ƙarshe wanda shi yafi komai, wato maganganun da Malam ya fada mata.
A haka suka tafi suka barta ba cikin hayyacinta ba.
Suna fita sukaga Malam Sale tsaye yana jiransu, su duka biyun suka tsugunna har ƙasa suka gaida shi, ya amsa haɗi da cewa Ah ƴan uwan juna anzo sallama ne, kasancewar duk inda ya gansu haka yake ce masu domin sun riga da sun zama ƴan uwa tun haihuwarsu.
Rankayawa sukayi suka nufi titi suka tsaida mai ɗan sahu da zai kai su tasha, Suna cikin tafiyan ne Malam Jafaru ya ciro wayar shi daga aljihu yace "Maryamah bari na baki wannan wayar, ni in Allah ya buɗe sai na siya wata"
Zatayi magana Malam Sale ya rigata "A'a ka bari kafin mu isa tasha sai a tsaya a siyan mata tata itama, saboda kaga nace maka Hajiya ta turo da kuɗin mota kuma abunda ta turo dashi zai isa a siyan mata, har kaima a baka wani abu ka rike a hannunka"
"Wai saida ta turo ɗin? Ni fa wallahi ba dan kuɗi nake son tafiyan Maryamah ba" cewan Malam Jafaru.
Shima Malam Sale yace "Toh tunda ta turo ai ba za a maida mata ba" Da haka yace ma mai ɗan sahun, dan Allah in sun je bakin tasha ya tsaya wurin shagon wayoyin nan.
Da isarsu wurin aka tsaya suka fito, da zasu shiga ta kalli Malam Sale kamar zatayi kuka tace "Baba dan Allah a siya da Aisha, in kuma kuɗin ba zasu isa ba a siyan mata ita, ni inna je in ina son magana da ku sai in ara waya na kiraku"
Cikin sauri Malam Sale yace "A'a zasu isama in Allah ya yarda, ai dubu hamsin ta turo Hajiyan" Haka suka shiga aka zabar masu wayoyin keypad guda biyu aka faɗa musu kuɗin suka biya, haka suka tsaya aka siya layi aka yi masu register, sim din be zama set ba suka tafi amma su duka sun rubuta lambar junan su a paper. Ita Maryamah daman ta haddace ta babanta duk da ba wayan kiran shi gareta ba a lokacin.
Da isar su tasha sauran mutum huɗu ake jira motar Katsina ta cika, kasancewar ita zasu hau domin daga Charanci ba a samun motar Abuja direct, dole sai kaje Katsina.
Haka suka shiga gaba ɗayan su, Ita batama yi tunanin su baba zasu raka su har Katsina ba, amma taga sun shiga motar ai a take farin ciki ya kama ta, cike da jin daɗi tace "Baba har can zaku kaini?"
A zuciyarta ta amsa da amin.
Ya ciga ba da cewa, "Allah yasa inda zakije ya kasance kinsamu rayuwa wadda baki samu ba a nan, ki dage da addu’a, ki riqe mutuncinki, ki kama kanki, Inshaa Allah zakiyi rayuwa wadda tafi wadda kikeyi a nan, a jikina nake jin inda zaki rayuwarki zata inganta kamar yanda nake mafarki da fata"
"Allah yasa babana, amma zuciyata zata kasance cikin kewan abunda tafi ƙauna da muradi"
Murmushi yayi yace "Da taji tana muradin babanta ta kirashi a waya, shiɗin zai kasance mai karfafa mata guiwa har ta cimma nasara a rayuwa..."
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO 🦋 ✨
BY RABIA'TU KABIRU ACHADU (FULANI)
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE KI HALIMA HASHEEM (MIEMIEN HABIBI)❤️ & AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI) ♥️
FULANI ❣️
08082101373
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO 🦋 ✨
PAGE 9️⃣
Kasancewar baya son hankalin zainu ya dawo kansu balle taji ko da kaɗan ne daga shirin su, duk da ma komai yazo ƙarshe, amma so yake ya shayar da su mamaki daga ita har Hajjah, domin so yake sai sun fito zata tafi kawai suji labari, dan yasan lokacin zasu tabbatar da ya shammace su, Shi ya sa yace mata ta tashi taje ta cigaba da shiryawa, shi zai je wurin Malam Sale yaji tafiyar tana nan karfe goma ɗin ko kuwa, dan shi hankalin shi ba zai kwanta ba sai ya tabbatar da ta bar garin.
Da toh ta amsa mishi ta miƙe suka fito kusan tare.
Dogon tsaki Baba Zainu taja cike da masifa tace "Aini ba za'a burgeni ba sai naga ka maidata ciki sannan zan tabbatar da girman son da kake mata, aikin banza kawai"
Girgiza kanshi yayi ya ficewar shi ya barta tana ɓaɓatu ita kaɗai domin Hajjah har lokacin bata fito ɗaki ba.
Itama ma Maryamah hanyar ɗakin ta tayi, dan da gaske take yau bata da lokacin matar, in kuma ta buɗe bakinta akan ta tofa abunda zai fito daga bakinta ita kanta sai tayi danasanin tankawa balle kuma ita baban, cire kayan jikinta tayi ta ɗaura zani ta fito zata shiga wanka, amma yanda ta samu bayin takaici sai da ya kusan sakata kuka, domin kaca-kaca haka yayi saboda yau batayi sammakon wankewa ba kuma ba za'a samu wani ko Zainab ta sanya ruwa ta kora dattin ciki ba, saida ta tsaya ta wanke bayin tass sannan ta shiga wankan, Bayan ta fito ta shirya cikin atamfarta ta sallah mai sauƙin kuɗi, kasancewar su masu rangwamen ƙarfi, amma duk da haka babanta na iya bakin ƙoƙarin shi wurin yi mata sutura, saboda yace ai macece ita kuma mace sai da sutura domin sutura ita ce mutum, haka ta shirya tsaf abunta kuma tayi masifar kyau duk da damuwar dake cin ranta, a hakan be hana kyawunta fitowa ba. fuskarta tayi fayau, kwalli ta shafa ta sanya man leɓe kasancewar bata mu’amala da hoda.
Tana cikin shirin ta jiyo sallamar Aisha a tsakar gida, inda kuma ta jiyo muryar Baba Zainu tana cewa "wai zaryar uban me ake mana a cikin gida tun jiya? Ni fa munafurci ne, bana so tunda ai ba zuwa kike ba da ko yanzun wani munafuncin ake ƙullawa yasa kiketa faman yi mana zarya"
Ƙaramin tsaki Aisha taja tayi wucewarta ɗakin Maryamah.
"Kinwa uwar ki buntalo tsaki bani ba, shegiyar yarinya mai kama da shaiɗanu"
Hayaniyar tace ta fito da Hajjah tana faɗin "Ke kam Zainu baki taɓa bari mutum ya rintsa, yanzun gidan ke kaɗai ma sai kin yi hayaniya, dan nasan dai yara sun tafi makaranta haka waccan kafurar ma yar allazee boko"
"Ina fa ta tafi? yau bansan munafurcin daya hanata zuwa makarantar da take jin ta kamar ɗakin uwarta ba, shine waccan shegiyar yarinyar ta wajen buntalo ta zo ita kuma tana nata rashin tarbiyya, kin san ba tarbiyya gareta ba daga nace wai zaryar me take mana a gida tun jiya, shine yarinyar nan ta kalle ni ta buga tsaki"
★★★
Aisha kam da shigarta Maryamah ta tareta da "uwar ƴan ɗaukar magana, gashinan kin jawo ma ummana zagi da farar safiya"
"Ke kyale karyar can tayi tayi, aita saba, ko bance komai ba sai tayi, shiyasa ma nayi mata tsakin dan tayi da hujja"
"Aikin kyauta da kika jawo magana"
Zama sukayi suna gaisawa.
"Ƙarfe nawa ne tafiyar?" "Toh baba dai yace jiya Baba Sale yace mishi ƙarfe goma amma yaje yaji abunda zai ce"
"Ai goma ta kusa" ƙara kallon Maryamah tayi tace "sahiba Allah gara ma kibar gidan nan ko kunnuwanki su huta da jin mugun alƙaba’in matar can"
“Hmmn kibari kawai sahiba, ni kaina abunda nace kenan ɗazun da ta fara" ta bata amsa tana ɓata fuska.
Suna ciki sukaji maganar Hajjah tana fadin "ni bari na shiga barka gidan azumi, jikanyarta ta haihu, daman cewa nayi in bari sai ɗagawar hantsi.
A dawo lafiya Baba Zainu ta mata tana ci gaba da aikin da take, dan yau awara take son yi tunda Hassu tace yau zata dawo, daman gidan babanta taje ta kwana biyu.
Bayan fitar baba ko minti ashirin batayi ba baba ya shigo gidan da sallama.
Banza baba Zainu tayi dashi dan a ciki take dashi.
Shima bebi ta kanta ba ya karasa ƙofar ɗakin Maryamah yana faɗin, "Zainariya in kin shirya ki fito mu tafi, Malam Sale na jiranmu"
Ai kamar da baba yake tayi saurin sakin abunda take ta juyo gaba ɗaya hankalinta na a akanshi, shi kuma yayi kamar besan da wanzuwarta ba. Mamaki be isa kasheta ba sai da taga Maryamah ta fito da jaka ta kuma sanya kayan sallarta alamar garin dai zata bari, gaba ɗaya ta ma rasa me zata ce, ƙoƙari take ta kamo bakin zaren amma ta kasa.
Bayan fitowar Maryamah da Aisha ne Aishan tana tsugunna ta gaida baba, ya amsa yace "kinzo yima ƴar uwarki rakiya kenan?"
"Eh baba"
Gaba ɗaya fa Baba Zainu ta shiga duhu, to wai me malam yake nufi ne? Yarinyar nan garin zata bari ko kuwa wani wuri zata ta dawo? Bata kai ƙarshen tunaninta ba taji muryar Malam na magana kaman ya shiga zuciyar ta.
"Toh Zainu, Maryamah zata bar miki gidan yau dai saiki sakata ki wala, dan naga kamar ta tare miki iskan shaƙa, sannan abinda nake so ki sani shine, shi sharri ɗan aike ne, yanda ya tafi haka zai dawo wa meshi, kuma ɗa dakike gani na kowwa ne ba ki san mejin ƙanki ba,ƙila ita da kike gani a wulaƙance ita ce zata ja ki zuwa gaba, kuma kin matuƙar bani mamaki akan abunda naji kuna shiryawa, nina riƙe taki ƴar da amana amma ke kin gagara riƙe tawa, ke kenan kullum cikin neman hanyar da zata tozarta, toh da izinin Allah Maryamah ba zata taɓa kauce hanya ba, kuma a duk inda take addu’ata tana tare da ita, zata tafi zata barmiki gidan kici uwar da zakici da shi"
Yana gama faɗin haka ya sanya hannu ya ɗauki jakar Maryamah yace "ku shige mu je"
Ko zarafin magana be bata ba, toh ta ina ma zata iya magana bayan tayi freezing, atoh tayi freezing mana gaba ɗaya ta daskare , abubuwa ne suka taru suka haɗe mata, na farko barin da Maryamah zatayi ma garin ba tare da ta cika burinta ba, na biyu yanda aka shammaceta akan tafiyan, sai kuma na ƙarshe wanda shi yafi komai, wato maganganun da Malam ya fada mata.
A haka suka tafi suka barta ba cikin hayyacinta ba.
Suna fita sukaga Malam Sale tsaye yana jiransu, su duka biyun suka tsugunna har ƙasa suka gaida shi, ya amsa haɗi da cewa Ah ƴan uwan juna anzo sallama ne, kasancewar duk inda ya gansu haka yake ce masu domin sun riga da sun zama ƴan uwa tun haihuwarsu.
Rankayawa sukayi suka nufi titi suka tsaida mai ɗan sahu da zai kai su tasha, Suna cikin tafiyan ne Malam Jafaru ya ciro wayar shi daga aljihu yace "Maryamah bari na baki wannan wayar, ni in Allah ya buɗe sai na siya wata"
Zatayi magana Malam Sale ya rigata "A'a ka bari kafin mu isa tasha sai a tsaya a siyan mata tata itama, saboda kaga nace maka Hajiya ta turo da kuɗin mota kuma abunda ta turo dashi zai isa a siyan mata, har kaima a baka wani abu ka rike a hannunka"
"Wai saida ta turo ɗin? Ni fa wallahi ba dan kuɗi nake son tafiyan Maryamah ba" cewan Malam Jafaru.
Shima Malam Sale yace "Toh tunda ta turo ai ba za a maida mata ba" Da haka yace ma mai ɗan sahun, dan Allah in sun je bakin tasha ya tsaya wurin shagon wayoyin nan.
Da isarsu wurin aka tsaya suka fito, da zasu shiga ta kalli Malam Sale kamar zatayi kuka tace "Baba dan Allah a siya da Aisha, in kuma kuɗin ba zasu isa ba a siyan mata ita, ni inna je in ina son magana da ku sai in ara waya na kiraku"
Cikin sauri Malam Sale yace "A'a zasu isama in Allah ya yarda, ai dubu hamsin ta turo Hajiyan" Haka suka shiga aka zabar masu wayoyin keypad guda biyu aka faɗa musu kuɗin suka biya, haka suka tsaya aka siya layi aka yi masu register, sim din be zama set ba suka tafi amma su duka sun rubuta lambar junan su a paper. Ita Maryamah daman ta haddace ta babanta duk da ba wayan kiran shi gareta ba a lokacin.
Da isar su tasha sauran mutum huɗu ake jira motar Katsina ta cika, kasancewar ita zasu hau domin daga Charanci ba a samun motar Abuja direct, dole sai kaje Katsina.
Haka suka shiga gaba ɗayan su, Ita batama yi tunanin su baba zasu raka su har Katsina ba, amma taga sun shiga motar ai a take farin ciki ya kama ta, cike da jin daɗi tace "Baba har can zaku kaini?"