Sashe 18
Rantsatstsen Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Share su tayi bata ce masu komai ba, dan tanaji da miskilanci, kuma ita har yanzun bata ga dalilin da zai sanya ta biye masu ba.
Mamy ce ta shigo "Cutie shine kika bama kowa, ko ki tuna dani koh? To nagode"
Cikin sauri tace "Kiyi haƙuri mamy, banyi tunanin kina parlour bane ai"tun bata karasa mata bayani ba ta ɗau plate tana zuba mata.
"Aida ni har nayi zuciya nace bazanci ba"
"Kiyi haƙuri mamy kici" tayi maganar tana miƙa mata plate ɗin haɗi da marairaice fuska.
Karɓa tayi "shikenan nagode, sannun ku da ƙoƙari, kunata shan aiki"
Kan Iya ta maida kallon ta "gobe inaga ba sai anyi breakfast ba, kawai ki barsu kowa yasha tea, sai ku fara aikin girkin da wuri, dan jirgin 12 su Alhaji zasu sauka. So nasan sai yayi azahar zai shigo cikin gida, kafin lokacin nakeso a gama komai dan Allah"
"Sai fruit juice da nake so a haɗa wa "Son kinsan baya san company made yafi son natural juice, ban sani ba shi ko yau zaku haɗa shi ko sai goben, Inajin shiɗin ma saidai ke kiyi, iya kinsan son, ba kowa ke abu yanaci ba, Idan kuma daughter ta iya sai ki bata tayi" ta ƙarasa tana maida kallonta kan Maryamah.
Ba iya su dijee ba, har ita kanta Maryamah jin sunan tayi wani iri da Hajiyan ta kirata da shi.
Itakam hajiya shauƙin ka6unar ɗiyar da takeji ne yake sanya, take manta matsayinta a gidan, Allah ya sani tana son yarinyar, kuma tanada plan sosai a kanta, fatanta Allah yasa komai ya tafi mata yanda ya dace, ba tare da samun tangarɗa ba.
Ƙasa Maryamah tayi da kanta, ganin har lokacin hajiyan bata ɗauke idonta akanta ba, "Insha Allah zan gwada, nasan bazai gagara ba"
"Yauwa da kyau ɗiyata Allah yayi muku albarka"
Ƙasa ƙasa ta amsa da Amin.
Kan iya ta maida kallon ta "goben sai ki bata duk abinda ya dace ɗin"
Insha Allah iya ta amsa mata.
Allah ya taimaka daga haka ta fita daga kitchen ɗin ɗauke da plate ɗin danbum namanta.
Bayan fitar ta, su sahura suka ƙara shaƙa har suna haɗa baki, gurin cewa Hmm, uhmm, yau muke ganin abu a gidan nan.
Dije tace "anya kuwa ba sanya hannu a lamarin nan?"
"Kemadai kyace amma dai ai ba girin irin ba tayi mai" cewar sahura tana zuba mata harara.
Iya tace "Allah ya shirye ku ya rabaku da hassada, domin ita hassada taki ce, kunayi mata zakuga tana ƙara haɓaka kowa da kuke gani, arziƙin shi yake ci bame cin arziƙin wani"
"Kodai dai da rana ɗaya kada ki biye musu, kinji?" Tayi maganar idonta kan maryamah.
Inshaa Allah, Iya, nagode....
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/JHxZP3j1IIr6O5UZj4Csq5?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/JHxZP3j1IIr6O5UZj4Csq5?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATTSEN RABO ✨ 🦋
BY RABI'ATU KABIR ACHADU FULANI
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE HALIMA HASHEEM (MIEMIEN HABIBI)❤️& AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI)♥️
FULANI ❣️
08082101373
✨🦋 RANTSATTSEN RABO 🦋 ✨
PAGE2️⃣0️⃣
Washegari ma da aiki tashi, Ita dai Maryamah shara tayi da goge-goge, sai wuraren 11 ta shiga kitchen gurin su Iya, tana shiga Iya tace ta ɗauki cup ta haɗa tea taje ta tasha, idan ta karya sai ta zo ta haɗa ma Alhaji ƙarami lemon da hajiya tace ta hada mishi.
"Iya ki kawo kawai nayi yanzu ai bana jin yunwa"
"A'a kije kici abinci kiyi wanka sai kizo ki haɗa dan Alhaji ƙarami idan ya sameki a haka, akace mishi ke kika haɗa abinda zai ci tabbas bazaici ba, yanada tsantseni duk tsaftar mutum ba kowacce ke gamsar dashi ba"
Toh kawai tace ta juya tana jinjina iyayin bawan Allah nan, ita kam zata so ta ganshi, haka nan kuma sai takejin tsoron haɗuwar su har tana insha Allah ma ni bazamu taɓa haɗuwa ba, kada yayi min masifa, ta faɗi tana ɗan tura baki.
Tana shiga da wanka ta fara dan daman jikin ya isheta, bayan ta fito ta shirya cikin wata doguwar rigan atampha, taje kanta tayi wanda duk ya dameta, tana son a ɗan ɗaure mata shi, amma bata san ya zatayi ba, amman tabari idan Iya ta shigo zata tambayeta inda ake musu kitso, ƙaramin hijab ta ɗauka wanda ya kai mata guiwa ta sanya tafita, ta samu Iya a kitchen.
Iya tace, "Har kinyi wanka?" "Eh yanzun tea kawai zan sha sai inzo in haɗa abinda hajiya tace a haɗa yau"
"To shikenan ki gama saina nuna miki abubuwan da zaki buƙata"
Tea ɗin ta haɗa ta zauna a kitchen ɗin tana sha a hankali, cike da nutsuwa.
Su Dije suna gefe suna gulmar wai ta cika iyayi har sahura, na cewa "wannan da ace ubanta yafi haka kudi, daza aga wulakanci da taƙama, Ita komai nata cikin isa da izza takeyi, amma na banza tunda basu da kosisi, karshe ma an ƙare a aikatau"
Dije ta care dacewa "yanzun haka ubanta fah mugun matsiyaci ne, amma tazo tana mana feleƙe"
Miƙewa tayi ta ƙarasa gaban su, dan tanaji tabbas yau anzo gaɓar da zata tanka masu, tunda suka sanya mahaifinta a cikin shirmen su.
Koda ta ƙarasa gaban su, diriricewa sukayi domin wani kwarjini na musamman sukaga yarinyar ta masu.
Kallan su tayi tsaff a tsanake, sannan dakyar ta buɗe bakinta kamar bata son yin magana "a da nasa a raina komai zakuce baku kai matsayin da zan tanka muku ba, amma a yau kuma ayanzun sainaga cewar kun isa gaɓar da dole nayi maku magana wadda koda ita kadai nabarku ta isheku, abinda nake so ku sani shine, Maryamah da mahaifinta ba matsiyata bane, Infact bama mu haɗa hanya da tsiya ba, domin rufin asirin Allah dai dai gwargwado munada shi, tunda a tsawon rayuwata ba ataba ɗora tukunya ƙasa da sau 3 ba a gidanmu, kunga kam in babu ne ta rashin ci zaisa na fito nema to tabbas bana tare dashi, In kuma na fito hakika na tabbata mara godiyar Allah"
"Sai abu na biyu kuma, sutura itama ba sai na faɗa muku ba, tunda koda nazo gidan nan ba a cikin wulaƙantacciyar shiga kuka ganni ba, wanda har inda yanzun take kayan da mahaifina yayi man ne a jikina, bana uban wani ba, kuma ina so ku sani duk talaucin mahaifina, yanada wadatar zucin da abun wani da abun duniya duka basu tsone mishi ido ba, hakan yasa ya tashi, bame kwaɗayin abun duniya ba"
Shiru tayi tana maida numfashi.
"Daga yau idan zakuyi shashancinku, ina so ya tsaya akan Maryamah, In kuma kukace zaku saka Mahaifin Maryamah a shirmen ku, tabbas zaku gane shayi ruwa ne, dan billahillazee sai na manta da tazarar shekarun dake tsakaninmu na muku abinda har ku kwanta dama bazaku manta dani ba, Ina dau6kan komai amma bana daukan wulaƙanci da cin mutunci, Kuma da kuka ga kunayi, ina share ku inasawa a raina ne cewan ku ai baku isa ku wulaƙantani ba"
"Da ace wadanda nake ma aiki ne suke min haka ko kwana ɗaya bazanyi ba a gidan su, dan ni ba wulaƙantacciya bace kuma bana ɗaukan shi daga gun kowa, amma kasancewar naga kune kuma ba wasu kayan gabas bane, sai nake ɗaukan abinda kukeyi a matsayin shirme"
"Daga rana irin ta yau sai kusan yanda zaku mu'amalance ni dan shirun da kukaga, ina maku bawai dan ina tsoron ku bane, bakusan dalilin zuwana aiki ba dan haka ba zaman ku nake ba ku kama mutuncin kanku tun kafin nayi maku abinda zakuyi dana sani mara amfani Useless human being"
Dogon tsaki taja musu tabar inda suke zuwa gurin da ta tashi, tana jiran su tankata yau ta nunamasu asalin colour nata.
Mamy datazo zata shiga kitchen ɗin tun sanda Dije take maganar ta ta karshe, ta tsaya ganin Maryamah ta nufi inda suke, dan ita da batama fahimci da waye suke ba, taji daɗin gargaɗin da yarinyar ta masu, takuma nuna tasan darajar iyayenta, tasan koda zasu kara mata wani abu, badai yanzun ba, juyawa tayi tabar kitchen ɗin, dan daman zuwa tayi taga in sun gama aikin nasu, dan yanzun za a tafi airport tarban su daddy, A ranta take tunanin kenan matsama yarinyar suke, har taki yau sun mata wanda ta kasa haƙuri ta tanka masu, tabar maganar a ranta da niyya, zata sanya musu ido in suka cigaba, zata ɗauki mataki a kansu.
Ita kam Maryamah cikin natsuwa ta koma ta cigaba da shan tea ɗin ta.
Iya tace mata "Kinyi daidai kin nuna kinsan darajar iyayen ki." Ta kalli su Dije "Kunga abinda nake faɗa muku akan ku ja girman ku kunƙi, gashi yanzun har ya kai ga ƙaramar yarinya ta zauna ta sille ku tass, Kuma in har haka tacigaba da faruwa, bansan kuma mezai iya faruwa ba, dan haka dan Allah tun wuri ku kama girman ku"
Banza sukayi da ita, zuciyar su tana tafasa, domin iya cin fuska yarinyar ta masu, abin mamaki kuma yau ɗaya sai sukaga ta rikiɗe masu ta koma kalar tsiwa, dan gani suke duk da rashin maganar ta, zatayi masifa, shakkar tanka mata sukaji, dan gudun rashin kunyar da zata iya ƙarayi masu, amma a ransu sun sa bata yi a banza ba, zata gane bata da wayau.
Itakam bayan ta gama shan tea ɗin ta, ta ɗauraye cup ɗin.
Iya ta fito mata da fruit ɗin da zatayi fruit juice, ta nuna mata juicer da yanda ake amfani da ita, godiya tayi mata ta fara aikinta cikin natsuwa.
Pineapple ta wanke da apple ta yanka su, sai kuma coconut itama ta fasata da wani engine da iya ta nuna mata na fasa kwakwa da yanda akeyi, Itama yankata tayi, ta hade su tayi blending gaba ɗaya, ta tace su ta wanke na'ana'a da ginger suma tayi blending, tace su tayi akan wancan ruwan fruit ɗin da ta tace flavour ta sanya mai ƙamshin Pineapple and coconut, ta nemi tambulan mai masifan kyau garai-garai ta zuba a ciki.
"Iya bansan ya yanayin son zaƙin shi yake ba, amma duk da haka bari na ɗan saka cokali biyu na sugar, idann yasha beyi ba sai a ƙara"
"Bema son zaƙi sosai"
Ta bata amsa.
Mamy ce ta shigo "Cutie shine kika bama kowa, ko ki tuna dani koh? To nagode"
Cikin sauri tace "Kiyi haƙuri mamy, banyi tunanin kina parlour bane ai"tun bata karasa mata bayani ba ta ɗau plate tana zuba mata.
"Aida ni har nayi zuciya nace bazanci ba"
"Kiyi haƙuri mamy kici" tayi maganar tana miƙa mata plate ɗin haɗi da marairaice fuska.
Karɓa tayi "shikenan nagode, sannun ku da ƙoƙari, kunata shan aiki"
Kan Iya ta maida kallon ta "gobe inaga ba sai anyi breakfast ba, kawai ki barsu kowa yasha tea, sai ku fara aikin girkin da wuri, dan jirgin 12 su Alhaji zasu sauka. So nasan sai yayi azahar zai shigo cikin gida, kafin lokacin nakeso a gama komai dan Allah"
"Sai fruit juice da nake so a haɗa wa "Son kinsan baya san company made yafi son natural juice, ban sani ba shi ko yau zaku haɗa shi ko sai goben, Inajin shiɗin ma saidai ke kiyi, iya kinsan son, ba kowa ke abu yanaci ba, Idan kuma daughter ta iya sai ki bata tayi" ta ƙarasa tana maida kallonta kan Maryamah.
Ba iya su dijee ba, har ita kanta Maryamah jin sunan tayi wani iri da Hajiyan ta kirata da shi.
Itakam hajiya shauƙin ka6unar ɗiyar da takeji ne yake sanya, take manta matsayinta a gidan, Allah ya sani tana son yarinyar, kuma tanada plan sosai a kanta, fatanta Allah yasa komai ya tafi mata yanda ya dace, ba tare da samun tangarɗa ba.
Ƙasa Maryamah tayi da kanta, ganin har lokacin hajiyan bata ɗauke idonta akanta ba, "Insha Allah zan gwada, nasan bazai gagara ba"
"Yauwa da kyau ɗiyata Allah yayi muku albarka"
Ƙasa ƙasa ta amsa da Amin.
Kan iya ta maida kallon ta "goben sai ki bata duk abinda ya dace ɗin"
Insha Allah iya ta amsa mata.
Allah ya taimaka daga haka ta fita daga kitchen ɗin ɗauke da plate ɗin danbum namanta.
Bayan fitar ta, su sahura suka ƙara shaƙa har suna haɗa baki, gurin cewa Hmm, uhmm, yau muke ganin abu a gidan nan.
Dije tace "anya kuwa ba sanya hannu a lamarin nan?"
"Kemadai kyace amma dai ai ba girin irin ba tayi mai" cewar sahura tana zuba mata harara.
Iya tace "Allah ya shirye ku ya rabaku da hassada, domin ita hassada taki ce, kunayi mata zakuga tana ƙara haɓaka kowa da kuke gani, arziƙin shi yake ci bame cin arziƙin wani"
"Kodai dai da rana ɗaya kada ki biye musu, kinji?" Tayi maganar idonta kan maryamah.
Inshaa Allah, Iya, nagode....
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/JHxZP3j1IIr6O5UZj4Csq5?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/JHxZP3j1IIr6O5UZj4Csq5?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATTSEN RABO ✨ 🦋
BY RABI'ATU KABIR ACHADU FULANI
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE HALIMA HASHEEM (MIEMIEN HABIBI)❤️& AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI)♥️
FULANI ❣️
08082101373
✨🦋 RANTSATTSEN RABO 🦋 ✨
PAGE2️⃣0️⃣
Washegari ma da aiki tashi, Ita dai Maryamah shara tayi da goge-goge, sai wuraren 11 ta shiga kitchen gurin su Iya, tana shiga Iya tace ta ɗauki cup ta haɗa tea taje ta tasha, idan ta karya sai ta zo ta haɗa ma Alhaji ƙarami lemon da hajiya tace ta hada mishi.
"Iya ki kawo kawai nayi yanzu ai bana jin yunwa"
"A'a kije kici abinci kiyi wanka sai kizo ki haɗa dan Alhaji ƙarami idan ya sameki a haka, akace mishi ke kika haɗa abinda zai ci tabbas bazaici ba, yanada tsantseni duk tsaftar mutum ba kowacce ke gamsar dashi ba"
Toh kawai tace ta juya tana jinjina iyayin bawan Allah nan, ita kam zata so ta ganshi, haka nan kuma sai takejin tsoron haɗuwar su har tana insha Allah ma ni bazamu taɓa haɗuwa ba, kada yayi min masifa, ta faɗi tana ɗan tura baki.
Tana shiga da wanka ta fara dan daman jikin ya isheta, bayan ta fito ta shirya cikin wata doguwar rigan atampha, taje kanta tayi wanda duk ya dameta, tana son a ɗan ɗaure mata shi, amma bata san ya zatayi ba, amman tabari idan Iya ta shigo zata tambayeta inda ake musu kitso, ƙaramin hijab ta ɗauka wanda ya kai mata guiwa ta sanya tafita, ta samu Iya a kitchen.
Iya tace, "Har kinyi wanka?" "Eh yanzun tea kawai zan sha sai inzo in haɗa abinda hajiya tace a haɗa yau"
"To shikenan ki gama saina nuna miki abubuwan da zaki buƙata"
Tea ɗin ta haɗa ta zauna a kitchen ɗin tana sha a hankali, cike da nutsuwa.
Su Dije suna gefe suna gulmar wai ta cika iyayi har sahura, na cewa "wannan da ace ubanta yafi haka kudi, daza aga wulakanci da taƙama, Ita komai nata cikin isa da izza takeyi, amma na banza tunda basu da kosisi, karshe ma an ƙare a aikatau"
Dije ta care dacewa "yanzun haka ubanta fah mugun matsiyaci ne, amma tazo tana mana feleƙe"
Miƙewa tayi ta ƙarasa gaban su, dan tanaji tabbas yau anzo gaɓar da zata tanka masu, tunda suka sanya mahaifinta a cikin shirmen su.
Koda ta ƙarasa gaban su, diriricewa sukayi domin wani kwarjini na musamman sukaga yarinyar ta masu.
Kallan su tayi tsaff a tsanake, sannan dakyar ta buɗe bakinta kamar bata son yin magana "a da nasa a raina komai zakuce baku kai matsayin da zan tanka muku ba, amma a yau kuma ayanzun sainaga cewar kun isa gaɓar da dole nayi maku magana wadda koda ita kadai nabarku ta isheku, abinda nake so ku sani shine, Maryamah da mahaifinta ba matsiyata bane, Infact bama mu haɗa hanya da tsiya ba, domin rufin asirin Allah dai dai gwargwado munada shi, tunda a tsawon rayuwata ba ataba ɗora tukunya ƙasa da sau 3 ba a gidanmu, kunga kam in babu ne ta rashin ci zaisa na fito nema to tabbas bana tare dashi, In kuma na fito hakika na tabbata mara godiyar Allah"
"Sai abu na biyu kuma, sutura itama ba sai na faɗa muku ba, tunda koda nazo gidan nan ba a cikin wulaƙantacciyar shiga kuka ganni ba, wanda har inda yanzun take kayan da mahaifina yayi man ne a jikina, bana uban wani ba, kuma ina so ku sani duk talaucin mahaifina, yanada wadatar zucin da abun wani da abun duniya duka basu tsone mishi ido ba, hakan yasa ya tashi, bame kwaɗayin abun duniya ba"
Shiru tayi tana maida numfashi.
"Daga yau idan zakuyi shashancinku, ina so ya tsaya akan Maryamah, In kuma kukace zaku saka Mahaifin Maryamah a shirmen ku, tabbas zaku gane shayi ruwa ne, dan billahillazee sai na manta da tazarar shekarun dake tsakaninmu na muku abinda har ku kwanta dama bazaku manta dani ba, Ina dau6kan komai amma bana daukan wulaƙanci da cin mutunci, Kuma da kuka ga kunayi, ina share ku inasawa a raina ne cewan ku ai baku isa ku wulaƙantani ba"
"Da ace wadanda nake ma aiki ne suke min haka ko kwana ɗaya bazanyi ba a gidan su, dan ni ba wulaƙantacciya bace kuma bana ɗaukan shi daga gun kowa, amma kasancewar naga kune kuma ba wasu kayan gabas bane, sai nake ɗaukan abinda kukeyi a matsayin shirme"
"Daga rana irin ta yau sai kusan yanda zaku mu'amalance ni dan shirun da kukaga, ina maku bawai dan ina tsoron ku bane, bakusan dalilin zuwana aiki ba dan haka ba zaman ku nake ba ku kama mutuncin kanku tun kafin nayi maku abinda zakuyi dana sani mara amfani Useless human being"
Dogon tsaki taja musu tabar inda suke zuwa gurin da ta tashi, tana jiran su tankata yau ta nunamasu asalin colour nata.
Mamy datazo zata shiga kitchen ɗin tun sanda Dije take maganar ta ta karshe, ta tsaya ganin Maryamah ta nufi inda suke, dan ita da batama fahimci da waye suke ba, taji daɗin gargaɗin da yarinyar ta masu, takuma nuna tasan darajar iyayenta, tasan koda zasu kara mata wani abu, badai yanzun ba, juyawa tayi tabar kitchen ɗin, dan daman zuwa tayi taga in sun gama aikin nasu, dan yanzun za a tafi airport tarban su daddy, A ranta take tunanin kenan matsama yarinyar suke, har taki yau sun mata wanda ta kasa haƙuri ta tanka masu, tabar maganar a ranta da niyya, zata sanya musu ido in suka cigaba, zata ɗauki mataki a kansu.
Ita kam Maryamah cikin natsuwa ta koma ta cigaba da shan tea ɗin ta.
Iya tace mata "Kinyi daidai kin nuna kinsan darajar iyayen ki." Ta kalli su Dije "Kunga abinda nake faɗa muku akan ku ja girman ku kunƙi, gashi yanzun har ya kai ga ƙaramar yarinya ta zauna ta sille ku tass, Kuma in har haka tacigaba da faruwa, bansan kuma mezai iya faruwa ba, dan haka dan Allah tun wuri ku kama girman ku"
Banza sukayi da ita, zuciyar su tana tafasa, domin iya cin fuska yarinyar ta masu, abin mamaki kuma yau ɗaya sai sukaga ta rikiɗe masu ta koma kalar tsiwa, dan gani suke duk da rashin maganar ta, zatayi masifa, shakkar tanka mata sukaji, dan gudun rashin kunyar da zata iya ƙarayi masu, amma a ransu sun sa bata yi a banza ba, zata gane bata da wayau.
Itakam bayan ta gama shan tea ɗin ta, ta ɗauraye cup ɗin.
Iya ta fito mata da fruit ɗin da zatayi fruit juice, ta nuna mata juicer da yanda ake amfani da ita, godiya tayi mata ta fara aikinta cikin natsuwa.
Pineapple ta wanke da apple ta yanka su, sai kuma coconut itama ta fasata da wani engine da iya ta nuna mata na fasa kwakwa da yanda akeyi, Itama yankata tayi, ta hade su tayi blending gaba ɗaya, ta tace su ta wanke na'ana'a da ginger suma tayi blending, tace su tayi akan wancan ruwan fruit ɗin da ta tace flavour ta sanya mai ƙamshin Pineapple and coconut, ta nemi tambulan mai masifan kyau garai-garai ta zuba a ciki.
"Iya bansan ya yanayin son zaƙin shi yake ba, amma duk da haka bari na ɗan saka cokali biyu na sugar, idann yasha beyi ba sai a ƙara"
"Bema son zaƙi sosai"
Ta bata amsa.