Sashe 11
Rantsatstsen Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO 🦋 ✨
PAGE 1️⃣2️⃣
Mamee bata kai ga rufe baki ba, wata budurwa ta buɗe kofan ta shigo kanta tsaye batare da sallama ba, ciki ciki tace "barka da dare mamy"
"Barka" ta amsa mata a taƙaice.
Inda su Adeel suke ta kalla "maza ku tashi mommy na kiran ku"
Ko kallo Maryamah bata isheta ba duk da ta ɗan kalleta a fusge, amma badai zata shaida ya take ba, tsakanin ita da zuhura babu wanda ya tanka wani a cikin su, haka ta tasa ƙeyansu suka fice.
Mamy sama ta nunawa su Fadil alamun su haye, sannan ta maida kallonta ga Maryamah Kije ki kwanta kinji, akwai gajiya tare dake, sai da safe.
"Toh Allah ya kaimu" Ta kalli Zuhura tace "Saida safe"
Zuhura kam zumɓuro mata baki tayi "Nifa ba ruwana dake,tunda wariya kike nuna min"
Murmushi tayi cikin rashin sakewa ta bata haƙuri.
Mamy ce ta katse zuhura dake shirin magana "yi tafiyarki abinki, ki tabbatar kinyi bacci, banda tunanin baba" ta ƙarasa maganar da murmushi a fuskar ta.
Sallama sukayi, kowa ya nufi makwancin sa amma su mamy parlour dake sama suka nufa, hira suka dasa ta tsakanin ƴa da uwa.
Koda taje ɗaki, ta samu iya Lami ta gama komai da zatayi har ta shige ɗaki, da sallamanta ta shiga tana mata sannu.
"Sannu ƴar nan sannu da baƙunta"
Murmushi ta mata kawai tayi kasa da kanta.
Iya tace "Da alama kinzo da ƙafar dama gidan nan, tunda naga yaran gidan sunayin ki, duk da daman nan ɓangaren basu da matsala, sukam ɗayan ɓangaren ne dai azabar duniya" iya tayi maganar cike da sigar son bada labari.
"Uhmmn" kawai tace ta wuce inda wayanta take caji, ta ɗauka cike da zumuɗi ta kunna wayan, dan so take tayi waya da babanta taji ya yake.
Bayan wayar ta kawo komai ya saitu daidai, ta fara kiran layin babanta, tanajin ringing ɗin amma a ƙagare take, Ka ɗauka babana tayi maganar ƙasa ƙasa tamkar me shirin sakin kuka.
Ai kuwa cikin sa'a ya ɗaga ɗin da sallama, tanajin ya ɗaga ta saki siririn kuka mai haɗe da dariya "Babana, baban Maryamah"ta kira sunan shi wasu hawayen na kara zubo mata.
Shima a nashi ɓangaren ajiyar zuciya ya sauke "Zinariyar babanta ce?"
Ɗaga kai tayi kamar yana ganinta "Zinariyar kace babana, ina matuƙar kewan ka babana"
Nima ina kewan zinariya ta, toh yakike ? ya kukaje? Ya kika samu sabon wurin?” Duk ya jera mata tambayoyin a lokaci ɗaya, yayi shiru alamun yana jiran ta amsa mishi duka.
Dariya ta saki cikin hawayen tace "Babana duka tambayoyin nan mani ni kaɗai"
Shima a nashi ɓangaren dariyan yayi yace "ɗiyar babanta, to ai na rasa me zance ne"
Murmushi take tayi "To baba duk lafiya lau alhamdulillah, wurin zama kuma, baba, gashi nan, shima alhamdulillah muna fatan dacewa"
"Allah yasa mun dace ɗin"
"Ameen, baban Maryamah, ya mutanen gidan, yasu Zainab da Muktar?”
"Duk suna nan lafiya lau, mutanen gida kam tunda na dawo ma ban koma ba sai zuwa ɗan anjima, tunda kuka sauka mukayi waya da Malam Sale, yake faɗamin kun sauka lafiya"
"Haka ne baba"
"Masha Allah ki kwanta kiyi bacci, kiyi addu'a kinji, sannan kiyi aiki da gaskiya, banda taɓa abin wani"
Inshaa Allah, da haka sukayi sallama cikin kewar juna.
Bayan ta gama magana dashi ne ta kira numbern Aisha itama cike da zumuɗi.
Aikam kamar mai jira Aisha ta ɗauka, dan tun ɗazun take trying ana ce mata switch off.
Tana ɗagawa ta fara mita "Shine kika barni inata jiran kiranki har hawan ruwana sai da ya tashi"
"Au haba, kice hawan ruwanki ne ya tashi"
"Ki bari kawai, duk motsina sai nace sahiba ana can yanzun, ko kin isa, ko har kin fara aikin, ko mutanen sunada mutunci?"
Dariya ce sosai ta ƙwace wa Maryamah jin a yanda tayi mata maganar "Gaskiya Allah ya yaye miki yanzun wannan tunanin duk ke kadai" ta faɗa tana wata dariyan.
Itama Ai'shan dariya tayi "Ke Allah gaba ɗaya hankalina da tunani na yana wajen ki"
A nan suka shashance suna hiransu cike da nishaɗi har sai da akayi masu warning sannan sukayi sallama.
Itakam, iya Lami ashe tana gefe ta buga tagumi tana kallonta, a ranta take jinjina girman kaunar da wannan uba da ƴar suke ma junan su, ga kuma wata ma da batasan ya suke da ita, ba amma dai tasan sunada kusanci mai girman gaske, gaskiya.
Juyowa tayi taga iya na kallonta ɗan saita kanta tayi, sannan ta shiga toilet saboda wanka takesonyi, kunsan mutuniyar ku da wanka kamar kwaɗo, ganin bata gane kan abun ba dan ko ɗazun da ta shiga, iya ce ta taran mata ruwa a buta tayi alwallah, ganin bata san yanda zatayi ba, kuma bata son tayi karambani, shiyasa ta fito ta nemi wuri ta zauna.
Iya ta kalleta tace "Ba wanka zakiyi ba?"
Ƙasa tayi da kanta "Shi zanyi"
"Naga kin nemi waje kin zauna"
Sai lokacin ta ɗago kanta kaman zatayi kuka tace mata "Bansan ya ake amfani da bayin ba"
Iya ta riƙe baki da mamaki "Ikon Allah ƴar nan shine kuma kika nemi waje kika zauna maimakon kiyi magana"
Shiru Maryamah tayi, tayi ƙasa da kanta.
Wannan yarinyar dai inajin miskila ce, maganar ma kamar akan dole take yinta,
haka nan tace, tashi muje in nuna miki yanda yake.
Godiya tayi mata, tare da bin bayanta.
Bayan sun shiga ta nuna mata duk yanda zatayi amfani da abubuwan banɗakin, sanann ta fito ta barta, ita kuma tayi wankanta tsaff ta fito, jikinta ɗaure da zani da ƙaramin hijab.
Bayan tayi shirin bacci ne ta nemi wuri ta rakuɓe saboda basan ya zasuyi ba, kuma bata son baba taga zakewar ta.
Saida baban tace, Ki kwanta mana, ai gadon zai ishemu.
Haka ta kwanta a ɗarare tayi addu’an bacci, da yake tanada bashin baccin jiya da bata samu tayi sossai ba saboda zullumin barin gida, ga kuma gajiyar hanya, kasancewar bata taɓa doguwar tafiya ba, tana kwanciya bacci yayi gaba da ita.
Asubah tagari Maryamahn babanta....
★★★★
Asubar fari ta farka, ita kanta tayi mamakin baccin da tayi dan batayi zaton zata samu bacci har haka ba, jin anata kiran sallah ne yasa ta shiga bayi dauro alwallah, tazo ta kabbara sallah tayi nafila, Tana zaune tana lazimi har akayi kira na biyu, ta tashi ta kabbara raka'atan fajr har ta kabbara sallar asbah, iya bata tashi ba, Sai bayan da ta sallame sallah sannan ta ɗan bubbuga gefen iya kanta tashi tayi sallah.
Tashi tayi tana salati tace, Har anyi sallah, yar nan.
Kanta ta gyaɗa mata.
Nayi ta shige bata jima ba ta fito ta ta kabbara sallah.
Bayan ta idar ne, Maryamah ta maida kallonta ga iya tace mata, "Ina kwana?"
Lafiya lau ta amsa mata tana fadin "Ya kwanan bakunta?"
"Alhamdulillah" Maryamah tace tana cigaba da lazimi, bayan ta gama tayi azkar sai ta fara karatun Qur'ani cikin zazzakar muryarta.
Iya ma tashi tayi ta tafi kitchen dan ta fara nata aikin.
Bayan Maryamah ta gama karatun, ta tashi ta nunke abun sallah ta fito, tayi hanyar dataga iya na yawan fitowa da shiga tana kyautata zaton nan ne kitchen ɗin.
Shiga tayi ta samesu su 3 sunata aiki kowa da abinda yakeyi, gaishe da sauran tayi, suka amsa duk suna binta da ido, suna mata kallon ƙurilla, abunda tafi komai tsana a rayuwarta kenan, kallo bata son shi ko kaɗan....
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO ✨ 🦋
BY RABIA'TU KABIRU ACHADU (FULANI)
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE KI HALIMA HASHEEM (MIEMIEN HABIBI)❤️ & AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI)♥️
FULANI ❣️
08082101373
PAGE 1️⃣3️⃣
Ƙarasawa inda iya take, tayi tana tambayar ta "Iya mai zan taya ki da shi?"
"A'a keda zakije kiyi naki aikin yar nan, kije kawai ki fara naki aikin, babu yawa ai aikin"
"Bansan mai zanyi ba iya, tunda kinga jiya Hajiya bata faɗa min abinda zanyi ba, tadai ce shara da goge goge, to kuma bansan inda zan ringa sharewa"
Shiru Iyan tayi na ɗan lokaci kafin tace "toh tunda basu kai ga sakkowa ba, inaga koki fara gyara parlour na ƙasa kafin su sauko, sai kiji ina da ina zakiyi"
"Amma bansan inda kayan aikin suke ba ai"
Ajiye ludayin hannunta tayi "Eh kuma fa haka ne, muje na nuna miki inda suke"
Zuwa tayi ta ɗakko mata engine ɗin da keyin sharan da duk kayan buƙata, su mopping stick da sauran su.
Tsayawa tayi tana kallon abinda iya ta nuna mata, wai dashi zatayi shara ta tambayi kanta cike da mamaki.
"Ban iya amfani da wannan ba, in akwai tsintsiya a bani kawai sai inyi da ita"
"Ai parlour da ɗakunan nan sun miki girma, ace kiyi shara da tsintsiya wannan ɗin dai zaifi sauƙi, bari kiga yanda ake amfani dashi"
Nan Iya ta kunna mata, ta nuna mata. Da yake mai saurin ɗauke abuce, yasa tayi saurin fahimtar yanda ake amfani dashi, tayi ma iya godiya, ta fara aikin nata cike da kuzarinta.
Kafin karfe 7 ta gama gyara parlourn tsaff, tayi shara, tayi goge-goge. Tana cikin sanya turaren wuta da burner (kasancewar har shi Iya ta nuna mata yanda zatayi), taji saukowan mamy su Fadil na biye da ita.
Cike da murmushi da kuma jin daɗin ganin Maryaman na aiki tace "Kai Masha Allah, wai har kin tashi kin fara aiki kenan Maryamah?"
Da sauri ta tsugunna ƙasa "Ina kwana Hajiya"
Da lafiya ta amsa mata tace ta tashi daga tsugunnon da take haka, ya kwanan baƙon waje.
Da Alhamdulillah ta amsa tana ƙara yin ƙasa da kanta ganin irin kallon da take mata.
Cike da burgewa mamy take kallon ta dan ita dai haka nan yarinyan ta kwanta mata a rai, kuma da ƙari da tarbiyyar da ta kula yarinyar nada ita.
Cike da tsokana tace "Allah dai yasa baki kwana kina kuka ba"
Da murmushi a fuskarta bata amsa da a'a.
"Toh alhamdulillah, ashe har kin fara aikin ma, sannu kinji da ƙoƙari"
"Iya ce ta nuna mini inda zan fara, tace kafin ki sauko sai ki faɗa mini sauran wuraren"
"Aikam ta kyauta, yanzun sauran parlour sama da ɗakina, Zuhura ita ke gyara ɗakin ta dana su twins"
PAGE 1️⃣2️⃣
Mamee bata kai ga rufe baki ba, wata budurwa ta buɗe kofan ta shigo kanta tsaye batare da sallama ba, ciki ciki tace "barka da dare mamy"
"Barka" ta amsa mata a taƙaice.
Inda su Adeel suke ta kalla "maza ku tashi mommy na kiran ku"
Ko kallo Maryamah bata isheta ba duk da ta ɗan kalleta a fusge, amma badai zata shaida ya take ba, tsakanin ita da zuhura babu wanda ya tanka wani a cikin su, haka ta tasa ƙeyansu suka fice.
Mamy sama ta nunawa su Fadil alamun su haye, sannan ta maida kallonta ga Maryamah Kije ki kwanta kinji, akwai gajiya tare dake, sai da safe.
"Toh Allah ya kaimu" Ta kalli Zuhura tace "Saida safe"
Zuhura kam zumɓuro mata baki tayi "Nifa ba ruwana dake,tunda wariya kike nuna min"
Murmushi tayi cikin rashin sakewa ta bata haƙuri.
Mamy ce ta katse zuhura dake shirin magana "yi tafiyarki abinki, ki tabbatar kinyi bacci, banda tunanin baba" ta ƙarasa maganar da murmushi a fuskar ta.
Sallama sukayi, kowa ya nufi makwancin sa amma su mamy parlour dake sama suka nufa, hira suka dasa ta tsakanin ƴa da uwa.
Koda taje ɗaki, ta samu iya Lami ta gama komai da zatayi har ta shige ɗaki, da sallamanta ta shiga tana mata sannu.
"Sannu ƴar nan sannu da baƙunta"
Murmushi ta mata kawai tayi kasa da kanta.
Iya tace "Da alama kinzo da ƙafar dama gidan nan, tunda naga yaran gidan sunayin ki, duk da daman nan ɓangaren basu da matsala, sukam ɗayan ɓangaren ne dai azabar duniya" iya tayi maganar cike da sigar son bada labari.
"Uhmmn" kawai tace ta wuce inda wayanta take caji, ta ɗauka cike da zumuɗi ta kunna wayan, dan so take tayi waya da babanta taji ya yake.
Bayan wayar ta kawo komai ya saitu daidai, ta fara kiran layin babanta, tanajin ringing ɗin amma a ƙagare take, Ka ɗauka babana tayi maganar ƙasa ƙasa tamkar me shirin sakin kuka.
Ai kuwa cikin sa'a ya ɗaga ɗin da sallama, tanajin ya ɗaga ta saki siririn kuka mai haɗe da dariya "Babana, baban Maryamah"ta kira sunan shi wasu hawayen na kara zubo mata.
Shima a nashi ɓangaren ajiyar zuciya ya sauke "Zinariyar babanta ce?"
Ɗaga kai tayi kamar yana ganinta "Zinariyar kace babana, ina matuƙar kewan ka babana"
Nima ina kewan zinariya ta, toh yakike ? ya kukaje? Ya kika samu sabon wurin?” Duk ya jera mata tambayoyin a lokaci ɗaya, yayi shiru alamun yana jiran ta amsa mishi duka.
Dariya ta saki cikin hawayen tace "Babana duka tambayoyin nan mani ni kaɗai"
Shima a nashi ɓangaren dariyan yayi yace "ɗiyar babanta, to ai na rasa me zance ne"
Murmushi take tayi "To baba duk lafiya lau alhamdulillah, wurin zama kuma, baba, gashi nan, shima alhamdulillah muna fatan dacewa"
"Allah yasa mun dace ɗin"
"Ameen, baban Maryamah, ya mutanen gidan, yasu Zainab da Muktar?”
"Duk suna nan lafiya lau, mutanen gida kam tunda na dawo ma ban koma ba sai zuwa ɗan anjima, tunda kuka sauka mukayi waya da Malam Sale, yake faɗamin kun sauka lafiya"
"Haka ne baba"
"Masha Allah ki kwanta kiyi bacci, kiyi addu'a kinji, sannan kiyi aiki da gaskiya, banda taɓa abin wani"
Inshaa Allah, da haka sukayi sallama cikin kewar juna.
Bayan ta gama magana dashi ne ta kira numbern Aisha itama cike da zumuɗi.
Aikam kamar mai jira Aisha ta ɗauka, dan tun ɗazun take trying ana ce mata switch off.
Tana ɗagawa ta fara mita "Shine kika barni inata jiran kiranki har hawan ruwana sai da ya tashi"
"Au haba, kice hawan ruwanki ne ya tashi"
"Ki bari kawai, duk motsina sai nace sahiba ana can yanzun, ko kin isa, ko har kin fara aikin, ko mutanen sunada mutunci?"
Dariya ce sosai ta ƙwace wa Maryamah jin a yanda tayi mata maganar "Gaskiya Allah ya yaye miki yanzun wannan tunanin duk ke kadai" ta faɗa tana wata dariyan.
Itama Ai'shan dariya tayi "Ke Allah gaba ɗaya hankalina da tunani na yana wajen ki"
A nan suka shashance suna hiransu cike da nishaɗi har sai da akayi masu warning sannan sukayi sallama.
Itakam, iya Lami ashe tana gefe ta buga tagumi tana kallonta, a ranta take jinjina girman kaunar da wannan uba da ƴar suke ma junan su, ga kuma wata ma da batasan ya suke da ita, ba amma dai tasan sunada kusanci mai girman gaske, gaskiya.
Juyowa tayi taga iya na kallonta ɗan saita kanta tayi, sannan ta shiga toilet saboda wanka takesonyi, kunsan mutuniyar ku da wanka kamar kwaɗo, ganin bata gane kan abun ba dan ko ɗazun da ta shiga, iya ce ta taran mata ruwa a buta tayi alwallah, ganin bata san yanda zatayi ba, kuma bata son tayi karambani, shiyasa ta fito ta nemi wuri ta zauna.
Iya ta kalleta tace "Ba wanka zakiyi ba?"
Ƙasa tayi da kanta "Shi zanyi"
"Naga kin nemi waje kin zauna"
Sai lokacin ta ɗago kanta kaman zatayi kuka tace mata "Bansan ya ake amfani da bayin ba"
Iya ta riƙe baki da mamaki "Ikon Allah ƴar nan shine kuma kika nemi waje kika zauna maimakon kiyi magana"
Shiru Maryamah tayi, tayi ƙasa da kanta.
Wannan yarinyar dai inajin miskila ce, maganar ma kamar akan dole take yinta,
haka nan tace, tashi muje in nuna miki yanda yake.
Godiya tayi mata, tare da bin bayanta.
Bayan sun shiga ta nuna mata duk yanda zatayi amfani da abubuwan banɗakin, sanann ta fito ta barta, ita kuma tayi wankanta tsaff ta fito, jikinta ɗaure da zani da ƙaramin hijab.
Bayan tayi shirin bacci ne ta nemi wuri ta rakuɓe saboda basan ya zasuyi ba, kuma bata son baba taga zakewar ta.
Saida baban tace, Ki kwanta mana, ai gadon zai ishemu.
Haka ta kwanta a ɗarare tayi addu’an bacci, da yake tanada bashin baccin jiya da bata samu tayi sossai ba saboda zullumin barin gida, ga kuma gajiyar hanya, kasancewar bata taɓa doguwar tafiya ba, tana kwanciya bacci yayi gaba da ita.
Asubah tagari Maryamahn babanta....
★★★★
Asubar fari ta farka, ita kanta tayi mamakin baccin da tayi dan batayi zaton zata samu bacci har haka ba, jin anata kiran sallah ne yasa ta shiga bayi dauro alwallah, tazo ta kabbara sallah tayi nafila, Tana zaune tana lazimi har akayi kira na biyu, ta tashi ta kabbara raka'atan fajr har ta kabbara sallar asbah, iya bata tashi ba, Sai bayan da ta sallame sallah sannan ta ɗan bubbuga gefen iya kanta tashi tayi sallah.
Tashi tayi tana salati tace, Har anyi sallah, yar nan.
Kanta ta gyaɗa mata.
Nayi ta shige bata jima ba ta fito ta ta kabbara sallah.
Bayan ta idar ne, Maryamah ta maida kallonta ga iya tace mata, "Ina kwana?"
Lafiya lau ta amsa mata tana fadin "Ya kwanan bakunta?"
"Alhamdulillah" Maryamah tace tana cigaba da lazimi, bayan ta gama tayi azkar sai ta fara karatun Qur'ani cikin zazzakar muryarta.
Iya ma tashi tayi ta tafi kitchen dan ta fara nata aikin.
Bayan Maryamah ta gama karatun, ta tashi ta nunke abun sallah ta fito, tayi hanyar dataga iya na yawan fitowa da shiga tana kyautata zaton nan ne kitchen ɗin.
Shiga tayi ta samesu su 3 sunata aiki kowa da abinda yakeyi, gaishe da sauran tayi, suka amsa duk suna binta da ido, suna mata kallon ƙurilla, abunda tafi komai tsana a rayuwarta kenan, kallo bata son shi ko kaɗan....
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO ✨ 🦋
BY RABIA'TU KABIRU ACHADU (FULANI)
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE KI HALIMA HASHEEM (MIEMIEN HABIBI)❤️ & AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI)♥️
FULANI ❣️
08082101373
PAGE 1️⃣3️⃣
Ƙarasawa inda iya take, tayi tana tambayar ta "Iya mai zan taya ki da shi?"
"A'a keda zakije kiyi naki aikin yar nan, kije kawai ki fara naki aikin, babu yawa ai aikin"
"Bansan mai zanyi ba iya, tunda kinga jiya Hajiya bata faɗa min abinda zanyi ba, tadai ce shara da goge goge, to kuma bansan inda zan ringa sharewa"
Shiru Iyan tayi na ɗan lokaci kafin tace "toh tunda basu kai ga sakkowa ba, inaga koki fara gyara parlour na ƙasa kafin su sauko, sai kiji ina da ina zakiyi"
"Amma bansan inda kayan aikin suke ba ai"
Ajiye ludayin hannunta tayi "Eh kuma fa haka ne, muje na nuna miki inda suke"
Zuwa tayi ta ɗakko mata engine ɗin da keyin sharan da duk kayan buƙata, su mopping stick da sauran su.
Tsayawa tayi tana kallon abinda iya ta nuna mata, wai dashi zatayi shara ta tambayi kanta cike da mamaki.
"Ban iya amfani da wannan ba, in akwai tsintsiya a bani kawai sai inyi da ita"
"Ai parlour da ɗakunan nan sun miki girma, ace kiyi shara da tsintsiya wannan ɗin dai zaifi sauƙi, bari kiga yanda ake amfani dashi"
Nan Iya ta kunna mata, ta nuna mata. Da yake mai saurin ɗauke abuce, yasa tayi saurin fahimtar yanda ake amfani dashi, tayi ma iya godiya, ta fara aikin nata cike da kuzarinta.
Kafin karfe 7 ta gama gyara parlourn tsaff, tayi shara, tayi goge-goge. Tana cikin sanya turaren wuta da burner (kasancewar har shi Iya ta nuna mata yanda zatayi), taji saukowan mamy su Fadil na biye da ita.
Cike da murmushi da kuma jin daɗin ganin Maryaman na aiki tace "Kai Masha Allah, wai har kin tashi kin fara aiki kenan Maryamah?"
Da sauri ta tsugunna ƙasa "Ina kwana Hajiya"
Da lafiya ta amsa mata tace ta tashi daga tsugunnon da take haka, ya kwanan baƙon waje.
Da Alhamdulillah ta amsa tana ƙara yin ƙasa da kanta ganin irin kallon da take mata.
Cike da burgewa mamy take kallon ta dan ita dai haka nan yarinyan ta kwanta mata a rai, kuma da ƙari da tarbiyyar da ta kula yarinyar nada ita.
Cike da tsokana tace "Allah dai yasa baki kwana kina kuka ba"
Da murmushi a fuskarta bata amsa da a'a.
"Toh alhamdulillah, ashe har kin fara aikin ma, sannu kinji da ƙoƙari"
"Iya ce ta nuna mini inda zan fara, tace kafin ki sauko sai ki faɗa mini sauran wuraren"
"Aikam ta kyauta, yanzun sauran parlour sama da ɗakina, Zuhura ita ke gyara ɗakin ta dana su twins"