Sashe 6
Rantsatstsen Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kamar wadda akayi wa dole ta buɗe baki ta yi sallama ciki-ciki, domin yau zuciyarta a sama take, da ba don sanin muhimmancin sallamar ba wallahi da baza tayiba.
Zaune ta samesu suna magana da Hajja da Baba Zainu, amma da suka gan ta sai suka yi shiru, ba ta kalli inda suke ba, ta shige ɗaki domin yau jinta take dai-dai da su, Ganin ba ta tankasu ba yasa Hajja ta fara masifar da ta saba tana cewa, "Shegiya, kin shigo kin same mu amma kallo ba mu isheki ba? To wallahi ni dai in kika mani jafaru kika yiwa, tunda ko banza ni na haifi abina, yar malafar uba"
Baba Zainu kam sai cewa tayi, "Ke ma dai Hajja, in ta gaishe mu ai munada ƙima a idonta, Ai halinta halin uwarta, kaff baƙin halin uwarta ta kwaso, ba ta rage komai ba sai ma ƙari datayi"
Sosai zuciyarta take zafi jin yanda suke aibata umminta wadda tun da ta haifeta ma ko fuskarta ba ta kalla ba ta koma ga Mahaliccinta, amma wai ita za su zaga ta dalilinta, duk da yanda zuciyar take azalzalar ta haka ta danne dan tayi alwashin yau ba za ta kula su ba balle su ƙara fadin maganganun banza a kan mahaifiyarta.
Uniform ɗinta ta cire, ta ɗauki soson wankanta da sabulu ta fita. Nan ma tari batai musu ba, fuskarta a ɗinke taja ruwa ta shige bayi, ta barsu da halinsu, duk da tana jin basu fasa ba ai bata ta da mahaifiyar ta ba.....
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO ✨ 🦋
BY RABI'ATU KABIR ACHADU (FULANI)
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE KI HALIMA HASHEEM (MIEMIEN HABIBI)&❤️ TARE DA KAI HABIBI NA AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI)♥️
FULANI ❣️
08082101373
✨🦋RANTSATSTSEN RABO 🦋 ✨
PAGE7️⃣
Bayan fitowar tawanka ta shige ɗaki tana jin su, har lokacin basu dena zagi da aibata ta ba, a ranta ta ayyana aiki ya same ku kukam, haka ta shirya cikin kaya masu sauƙin nauyi, dan tana da jin zafi, duk da bata da wani jiki sosai, amma Allah yayita da mugun jin zafi, zama tayi ta fara haɗa kayanta, dan yau ko takan abinci bata bi ba domin she’s not in the mood, kuma cikinta a cinkushe yake, dan ko tace zata ci abinci ma tasan ba shiga zaiyi ba, zuciyarta a kuntace take.
Jakar kayanta ta jawo ta fara zuba kayan a ciki, kasancewar tana da wadatar sutura, saboda babanta na matuƙar ƙoƙari wajen yi mata ɗinki da siya mata kayan gwanjo, kayanta sun kai kusan kala goma sha biyar, a haka ma dan ita ba mai daɗewa da sutura ba ce, tana samun wasu take bada wasu, bata jima ba ta jerasu tsaf cikin jaka.
Tana gama haɗa kayan ta ɗakko litattafanta na makaranta suma ta haɗasu waje ɗaya, tana cikin haɗawa ne ta ji sallamar Aisha a tsakar gidan.
Fitowa tayi tana amsa mata "Ashe da gaske kike zakizo" ta faɗa cikin sakewa kaɗan.
Taɓe baki tayi ta bata amsa "Ai kin koya mini rashin saɓa alƙawari"
Kallon Hajja tayi tace, "Hajja ina yini" domin ta ci darajar kasancewarta kakar Maryamah, ko dan baba zata gaidata.
A ɗage ta amsa mata da lafiya, tana kauda kai gefe, saboda ita a rayuwarta bata ƙaunar taga wani ya raɓi Maryamah, dan ita fa a duniya bataƙi ace Maryamah ta zama mujiya ba, ya kasance kowa yana gudunta, amma hakan bai samu ba, dan Maryamah ba mai sakewa ba ce da jama'a, duk da haka kuma tana da farin jinin mutane, kawai dai baƙin miskilancinta da wulaƙanci da shegen girman kai (amma fa inji su Hajja ) shine yake hanata mu'amala da mutane.
★★★★
Ɗaki suka shige Aisha na cewa "Kai ashe ma har kin gama, ina ta sauri"
Hmmmnn kawai tace mata ba tare data bata amsa ba.
"Danaje gida na samu ummanmu na masa da kuli, shine fa na tsaya na taho miki da ita, tunda nasan mutuniyar ki ce sosai" ta faɗa da murmushi sosai a fuskar ta, so take ta saka maryamah farin ciki, bata sonta cikin wannan damuwar.
Nanma dai hmmnn ɗin kawai tace.
Harta cire rai da zata bata amsa taji muryarta ƙasa ƙasa tana bata amsa.
"A'isha bakina ɗaci yake, bazan iya ciba"
Bata rufe baki ba itama ta tari numfashin ta "wallahi sai kinci, ni zaki watsawa ƙasa a ido inyi dakon abu tun daga gida kizo kiƙici? Ah haba, ai wallahi baki isa ba"
Murmushi tayi naji jarababbiya"
Itama murmushin tayi "Yauwa to koke fa yanzun naga sahibata a tare dani"
Maryamah tace "Toh dawa kike gani?"
"Someone else" yanda A'ishahn ta bata amsa ne yasa duk suka yi dariya.
Fita tayi ta wanke hannun ta zata fara ci, Aisha ma tashi tayi ta wanke hannu ta sauko zata ɗauki wainar.
Da sauri Maryamah ta ɗauke tana cewa "Ban gane ba malama, menene haka? kema kin san baki isa ba, kici taki a gida kizo kice zakici tawa?" Ta ƙare maganar tana zabga mata harara.
Bata bata amsa ba sai ƙoƙarin ƙwata da take a hannun ta, sosai suke kokawar ƙwatar wainar, Aisha ta dage sai taci, itama maryamah tana batazaci mata ba, ai tasan tatace ita kaɗai, ummanta ta bada a kawo mata.
Sosai zukatansu suka samu nishaɗi, wanda Aisha tana sane ta aikata hakan, dan tasan abinda zai faru kenan, Zuwa can ta zauna tana sauke numfashi, wadda ta ɗauka ta saka a baki tace, "aidaman nace sai na ci"
Maryamah ƙasa ƙasa ta kalleta tace "My kawai"
Hmmm
"Ki fito kanki tsaye kice min mayya, bawai my ba"
Sosai Maryamah ta ji daɗin zuwan Aisha, ko banza ta rage mata wani nauyin zuciya.
Haka suka yi ta hira. Bayan ta gama ci ta wanke hannu ta dawo, nan suka cigaba da haɗa kayan har aka kira la’asar. Suka fita sukayi alwala, anan taga su Zainab tace su yi maza su yi sallah su kama hanyar Islamiyya, ita yau bazata ba.
Ba yaran bama, har baba da Hajja sun yi mamakin jin wai yau ita ce bazata Islamiyya ba, a yadda take ƴar allazi makaranta, Da toh Addah Zainab ta amsa ta tashi tana shirin alwala. Ita kuma Maryamah ta shige ɗaki ta bar su, baba na binta da ido, kuma ba damar bin ba’asin abin da ya hanata zuwa makarantar, tunda sun sanba wannan mutuncin a tsakaninsu.
Itakam haka suka zauna ana ta hiran bankwana da Aisha har aka kira magrib, sai bayan sunyi sallar magrib ne suka fito zata raka Aisha, lokacin matan gidan sun shiga ɗaki.
A ƙofar gida suka haɗu da baba zai shigo, nan Aisha ta tsugunna har ƙasa ta gaida shi, Ya amsa yana faɗin, "Aisha, anzo bankwana da ƙawar taki ne?"
"Eh baba"
Ganin yanda ta amsa ne yasa shi cewa "Toh duk muyi haƙuri, haka Allah ya tsara, dama Allah ya rigada ya tsara cewa zata tafi wani waje daban tabar mu" "Hakane baba"
Maryamah ya kalla "kiyi maza ki rakata ki dawo"
"Toh babana" Da haka suka wuce.
★★★★
Sai da ta rakata har gida, don tana so tayi wa ummansu sallama, sanda suka shiga sun samu umma ta idar da sallah. Maryamah ta shiga cikin nutsuwa tana gaida umman.
Amsa mata tayi haɗi da cewa "Maryamah idonki kenam?"
Sunnar da kai ƙasa tayi tana murmushi tace "Umma kiyi haƙuri"
Itama umma murmushi tayi tace, "Anya kuwa zan iya wannan haƙurin?"
"Zaki iya Allah umma, ai uwa bata fushi da ɗiyarta"
"Ai fa kin iya daɗin baki" inji umma.
"Aa fa ummana"
"To aishikenan, na haƙura" cewar umma.
Gyara zama tayi kallon maryamah tayi ta kira sunan ta da muryar dake nuna duk maganar da zata mata ne muhimmanci ce.
"Maryamah ashe kuma abinda yafaru kenan ɗazun Aisha ta dawo take faɗa min" Hawaye ne suka cika idonta tace, "Eh wallahi umma" ƙoƙarin maida hawayen idonta take amman ina saida suka zubo akan fuskar ta.
"Kiyi haƙuri ki ɗauki hakan a matsayin ƙaddararki kinji, ni kaina bansan meyasa ba, tunda Aisha ta faɗa min naji a raina kamar hakan alkhairi ne a gareki, wallahi ko kaɗan banji ina fargabar tafiyanki ba, hasalima ni daɗin hakan naji, da ikon Allah wannan tafiyar sai mun ce gara da akayi ta"
Shiru tayi tana ƙoƙarin danne tausayin maryamahn dayake taso mata jin yanda take ta sauke ajiyar zuciya, ga hawaye tamkar an buɗe famfo haka suke zarya akan kumatun ta.
"Ki kwantar da hankalinki, sannan in kinje ki riƙe mutuncinki, ki kama kanki ki kama mutuncin kanki, kada abin wani ya burgeki, ban sanki da kwaɗayi ba, don Allah ki cigaba da hakan, karki bari halin ki ko guda ɗaya ta canza.
"In sha Allah umma" ta bata amsa tana goge hawayen dayake zubo mata.
Itama Aisha na gefe tana matse nata hawayen.
Ɗorawa tayi daga inda ta tsaya "ki kuma dage da addu’a, in kuma kin fara makaranta kamar yadda muke sanya rai, dan girman Allah ki tsaya ki yi abinda ya dace da rayuwarki, banda shashanci, duk da nasan ba halinki bane, ba ruwanki da rayuwar yaran masu kuɗi, ki riƙe maraicinki da talaucinki, sannan ki iya talaucinki, kada kuma ki wulaƙanta kanki a wajen kowa ta hanyar nuna son abin hannun wani"
Jinjina kanta tayi cikin kuka tace "Nagode sosai umma, Allah ya ƙara girma, haƙiƙa ke ɗin uwace wadda har ɗan wani ta maida nata, In sha Allah bazan baku kunya ba, zan yi amfani da dukkan nasiharki gareni, nagode, nagode" bata ƙara sa maganar ba kuka ya kuɓce mata.
Tsam Aisha ta taso ta rungumeta suka cigaba da kukan tare, ita kanta umma ƙarfin hali kawai take yi amman sosai take tausayin maryamahn.
Cikin ƙarfin hali tace "K
kaji shashanci to meye abin kuka, sai kace waɗanda in suka rabu sun rabu kenan. Ke da ya kamata ki ƙarfafa mata guiwa ma, zaki zauna kuna kuka tare"
Zaune ta samesu suna magana da Hajja da Baba Zainu, amma da suka gan ta sai suka yi shiru, ba ta kalli inda suke ba, ta shige ɗaki domin yau jinta take dai-dai da su, Ganin ba ta tankasu ba yasa Hajja ta fara masifar da ta saba tana cewa, "Shegiya, kin shigo kin same mu amma kallo ba mu isheki ba? To wallahi ni dai in kika mani jafaru kika yiwa, tunda ko banza ni na haifi abina, yar malafar uba"
Baba Zainu kam sai cewa tayi, "Ke ma dai Hajja, in ta gaishe mu ai munada ƙima a idonta, Ai halinta halin uwarta, kaff baƙin halin uwarta ta kwaso, ba ta rage komai ba sai ma ƙari datayi"
Sosai zuciyarta take zafi jin yanda suke aibata umminta wadda tun da ta haifeta ma ko fuskarta ba ta kalla ba ta koma ga Mahaliccinta, amma wai ita za su zaga ta dalilinta, duk da yanda zuciyar take azalzalar ta haka ta danne dan tayi alwashin yau ba za ta kula su ba balle su ƙara fadin maganganun banza a kan mahaifiyarta.
Uniform ɗinta ta cire, ta ɗauki soson wankanta da sabulu ta fita. Nan ma tari batai musu ba, fuskarta a ɗinke taja ruwa ta shige bayi, ta barsu da halinsu, duk da tana jin basu fasa ba ai bata ta da mahaifiyar ta ba.....
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO ✨ 🦋
BY RABI'ATU KABIR ACHADU (FULANI)
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE KI HALIMA HASHEEM (MIEMIEN HABIBI)&❤️ TARE DA KAI HABIBI NA AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI)♥️
FULANI ❣️
08082101373
✨🦋RANTSATSTSEN RABO 🦋 ✨
PAGE7️⃣
Bayan fitowar tawanka ta shige ɗaki tana jin su, har lokacin basu dena zagi da aibata ta ba, a ranta ta ayyana aiki ya same ku kukam, haka ta shirya cikin kaya masu sauƙin nauyi, dan tana da jin zafi, duk da bata da wani jiki sosai, amma Allah yayita da mugun jin zafi, zama tayi ta fara haɗa kayanta, dan yau ko takan abinci bata bi ba domin she’s not in the mood, kuma cikinta a cinkushe yake, dan ko tace zata ci abinci ma tasan ba shiga zaiyi ba, zuciyarta a kuntace take.
Jakar kayanta ta jawo ta fara zuba kayan a ciki, kasancewar tana da wadatar sutura, saboda babanta na matuƙar ƙoƙari wajen yi mata ɗinki da siya mata kayan gwanjo, kayanta sun kai kusan kala goma sha biyar, a haka ma dan ita ba mai daɗewa da sutura ba ce, tana samun wasu take bada wasu, bata jima ba ta jerasu tsaf cikin jaka.
Tana gama haɗa kayan ta ɗakko litattafanta na makaranta suma ta haɗasu waje ɗaya, tana cikin haɗawa ne ta ji sallamar Aisha a tsakar gidan.
Fitowa tayi tana amsa mata "Ashe da gaske kike zakizo" ta faɗa cikin sakewa kaɗan.
Taɓe baki tayi ta bata amsa "Ai kin koya mini rashin saɓa alƙawari"
Kallon Hajja tayi tace, "Hajja ina yini" domin ta ci darajar kasancewarta kakar Maryamah, ko dan baba zata gaidata.
A ɗage ta amsa mata da lafiya, tana kauda kai gefe, saboda ita a rayuwarta bata ƙaunar taga wani ya raɓi Maryamah, dan ita fa a duniya bataƙi ace Maryamah ta zama mujiya ba, ya kasance kowa yana gudunta, amma hakan bai samu ba, dan Maryamah ba mai sakewa ba ce da jama'a, duk da haka kuma tana da farin jinin mutane, kawai dai baƙin miskilancinta da wulaƙanci da shegen girman kai (amma fa inji su Hajja ) shine yake hanata mu'amala da mutane.
★★★★
Ɗaki suka shige Aisha na cewa "Kai ashe ma har kin gama, ina ta sauri"
Hmmmnn kawai tace mata ba tare data bata amsa ba.
"Danaje gida na samu ummanmu na masa da kuli, shine fa na tsaya na taho miki da ita, tunda nasan mutuniyar ki ce sosai" ta faɗa da murmushi sosai a fuskar ta, so take ta saka maryamah farin ciki, bata sonta cikin wannan damuwar.
Nanma dai hmmnn ɗin kawai tace.
Harta cire rai da zata bata amsa taji muryarta ƙasa ƙasa tana bata amsa.
"A'isha bakina ɗaci yake, bazan iya ciba"
Bata rufe baki ba itama ta tari numfashin ta "wallahi sai kinci, ni zaki watsawa ƙasa a ido inyi dakon abu tun daga gida kizo kiƙici? Ah haba, ai wallahi baki isa ba"
Murmushi tayi naji jarababbiya"
Itama murmushin tayi "Yauwa to koke fa yanzun naga sahibata a tare dani"
Maryamah tace "Toh dawa kike gani?"
"Someone else" yanda A'ishahn ta bata amsa ne yasa duk suka yi dariya.
Fita tayi ta wanke hannun ta zata fara ci, Aisha ma tashi tayi ta wanke hannu ta sauko zata ɗauki wainar.
Da sauri Maryamah ta ɗauke tana cewa "Ban gane ba malama, menene haka? kema kin san baki isa ba, kici taki a gida kizo kice zakici tawa?" Ta ƙare maganar tana zabga mata harara.
Bata bata amsa ba sai ƙoƙarin ƙwata da take a hannun ta, sosai suke kokawar ƙwatar wainar, Aisha ta dage sai taci, itama maryamah tana batazaci mata ba, ai tasan tatace ita kaɗai, ummanta ta bada a kawo mata.
Sosai zukatansu suka samu nishaɗi, wanda Aisha tana sane ta aikata hakan, dan tasan abinda zai faru kenan, Zuwa can ta zauna tana sauke numfashi, wadda ta ɗauka ta saka a baki tace, "aidaman nace sai na ci"
Maryamah ƙasa ƙasa ta kalleta tace "My kawai"
Hmmm
"Ki fito kanki tsaye kice min mayya, bawai my ba"
Sosai Maryamah ta ji daɗin zuwan Aisha, ko banza ta rage mata wani nauyin zuciya.
Haka suka yi ta hira. Bayan ta gama ci ta wanke hannu ta dawo, nan suka cigaba da haɗa kayan har aka kira la’asar. Suka fita sukayi alwala, anan taga su Zainab tace su yi maza su yi sallah su kama hanyar Islamiyya, ita yau bazata ba.
Ba yaran bama, har baba da Hajja sun yi mamakin jin wai yau ita ce bazata Islamiyya ba, a yadda take ƴar allazi makaranta, Da toh Addah Zainab ta amsa ta tashi tana shirin alwala. Ita kuma Maryamah ta shige ɗaki ta bar su, baba na binta da ido, kuma ba damar bin ba’asin abin da ya hanata zuwa makarantar, tunda sun sanba wannan mutuncin a tsakaninsu.
Itakam haka suka zauna ana ta hiran bankwana da Aisha har aka kira magrib, sai bayan sunyi sallar magrib ne suka fito zata raka Aisha, lokacin matan gidan sun shiga ɗaki.
A ƙofar gida suka haɗu da baba zai shigo, nan Aisha ta tsugunna har ƙasa ta gaida shi, Ya amsa yana faɗin, "Aisha, anzo bankwana da ƙawar taki ne?"
"Eh baba"
Ganin yanda ta amsa ne yasa shi cewa "Toh duk muyi haƙuri, haka Allah ya tsara, dama Allah ya rigada ya tsara cewa zata tafi wani waje daban tabar mu" "Hakane baba"
Maryamah ya kalla "kiyi maza ki rakata ki dawo"
"Toh babana" Da haka suka wuce.
★★★★
Sai da ta rakata har gida, don tana so tayi wa ummansu sallama, sanda suka shiga sun samu umma ta idar da sallah. Maryamah ta shiga cikin nutsuwa tana gaida umman.
Amsa mata tayi haɗi da cewa "Maryamah idonki kenam?"
Sunnar da kai ƙasa tayi tana murmushi tace "Umma kiyi haƙuri"
Itama umma murmushi tayi tace, "Anya kuwa zan iya wannan haƙurin?"
"Zaki iya Allah umma, ai uwa bata fushi da ɗiyarta"
"Ai fa kin iya daɗin baki" inji umma.
"Aa fa ummana"
"To aishikenan, na haƙura" cewar umma.
Gyara zama tayi kallon maryamah tayi ta kira sunan ta da muryar dake nuna duk maganar da zata mata ne muhimmanci ce.
"Maryamah ashe kuma abinda yafaru kenan ɗazun Aisha ta dawo take faɗa min" Hawaye ne suka cika idonta tace, "Eh wallahi umma" ƙoƙarin maida hawayen idonta take amman ina saida suka zubo akan fuskar ta.
"Kiyi haƙuri ki ɗauki hakan a matsayin ƙaddararki kinji, ni kaina bansan meyasa ba, tunda Aisha ta faɗa min naji a raina kamar hakan alkhairi ne a gareki, wallahi ko kaɗan banji ina fargabar tafiyanki ba, hasalima ni daɗin hakan naji, da ikon Allah wannan tafiyar sai mun ce gara da akayi ta"
Shiru tayi tana ƙoƙarin danne tausayin maryamahn dayake taso mata jin yanda take ta sauke ajiyar zuciya, ga hawaye tamkar an buɗe famfo haka suke zarya akan kumatun ta.
"Ki kwantar da hankalinki, sannan in kinje ki riƙe mutuncinki, ki kama kanki ki kama mutuncin kanki, kada abin wani ya burgeki, ban sanki da kwaɗayi ba, don Allah ki cigaba da hakan, karki bari halin ki ko guda ɗaya ta canza.
"In sha Allah umma" ta bata amsa tana goge hawayen dayake zubo mata.
Itama Aisha na gefe tana matse nata hawayen.
Ɗorawa tayi daga inda ta tsaya "ki kuma dage da addu’a, in kuma kin fara makaranta kamar yadda muke sanya rai, dan girman Allah ki tsaya ki yi abinda ya dace da rayuwarki, banda shashanci, duk da nasan ba halinki bane, ba ruwanki da rayuwar yaran masu kuɗi, ki riƙe maraicinki da talaucinki, sannan ki iya talaucinki, kada kuma ki wulaƙanta kanki a wajen kowa ta hanyar nuna son abin hannun wani"
Jinjina kanta tayi cikin kuka tace "Nagode sosai umma, Allah ya ƙara girma, haƙiƙa ke ɗin uwace wadda har ɗan wani ta maida nata, In sha Allah bazan baku kunya ba, zan yi amfani da dukkan nasiharki gareni, nagode, nagode" bata ƙara sa maganar ba kuka ya kuɓce mata.
Tsam Aisha ta taso ta rungumeta suka cigaba da kukan tare, ita kanta umma ƙarfin hali kawai take yi amman sosai take tausayin maryamahn.
Cikin ƙarfin hali tace "K
kaji shashanci to meye abin kuka, sai kace waɗanda in suka rabu sun rabu kenan. Ke da ya kamata ki ƙarfafa mata guiwa ma, zaki zauna kuna kuka tare"