Sashe 7
Rantsatstsen Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Share hawayensu suka yi suka lallashi junansu.
Daga nan ta miƙe tace, "Umma bari naje gida dare yayi, sai da safe nagode Allah ya ƙara muku lafiya da nisan kwana"
Umma tace "Maryamah, godiyanki ta isa haka, keda Aisha duk ɗaya kuke a wajena abinda zan yi wa Aisha shi zanyi miki, koba dan abotar dake tsakaninku da Aisha ba, ko dan zaman mutuncin da mukayi da mahaifiyarki, tunda Allah ya sa suka zo garin nan, mun yi mutunci da ita har zuwa ranar da ta bar duniya, Allah ya jiƙanta, mace mai matuƙar mutunci da yakana, ga haƙuri da gudun zuciya, Kuje kawai, dare yayi Allah ya yi miki albarka, ya tsareki da tsarewarsa"
Ameen duk suka haɗa baki suka amsa. Aisha na binta don ta ɗan taka mata…..
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO 🦋✨
BY RABIA'TU KABIRU ACHADU (FULANI)
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE KI HALIMA HASHEEM (MIEMIEN HABIBI)&❤️ AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI)♥️
FULANI ❣️
08082101373
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO 🦋 ✨
PAGE 8️⃣
A hanya ma haka suke ji tamkar kar su rabu amma ba yanda suka iya sunzo daidai inda ba nisa daga nan zuwa gidansu Maryamah da kuma ita Aishan
Dakatawa sukayi da tafiya suka riƙe hannun juna.
A'isha ce ta kalleta tace "Sahiba ji nake kamar na biki mu tafi tare"
Murmushi tayi "kinjita kamar gaske"
yar dariya tayi "Allah da gaske"
Ganin A'ishan tayi kalar tausayi ne yasa ta fara mata magana cikin sigar tsoakana "Ba wani abu kika sani ma, koda naje ƙura ta lafa na gudo in dawo gida, ko in naga mutanen gidan basu da kirki wallahi guduwa zanyi dan ba yanda za ayi na tsaya a wulaƙantani, ke kinsan ma zuciyata bazata dauka ba"
Yanda maryaman tayi magana ne yasa tayi dariya "Sauran kije kina musu girman kai da wulakanci in miki ta bakin Hajjah"
Kusan a tare suka saki dariya "saifa abinda suka gani, nidai bazan ɗauki wulaƙanci ba, duk kuɗin mutum atohhhh"
"Insha Allah ma mutanen kirki ne zakiji dadin zama a cikinsu"
"Allah yasa kije gida kawai gobe kafin mutafi ko kinje school zan biki can in kara ganinki"
"Tabb ai wallahi gobe babu inda zani sai naga tashin motan ku dan har tasha zan biku"
Murmushi Maryamah tayi tana jinjina girman ƙaunar da Aisha ke mata, itafa zata iya sadaukar da komai saboda ita kuma tun suna yara suka tashi haka suna masu tsananin ƙaunar junansu, saboda Aisha take surutu, kasancewar ta bakin ta baya shiru, koba kayi niyyar magana ba saita saka ka kayi dolen ka, kuma saboda ita ta koyi buɗe baki ta mayar da magana in su Hajjah sun mata abu, wanda da ko kasheta zasuyi akan abun da batayi ba bazata bud6e baki ta kare kanta ba sai dai in an gama jibgarta ta shiga daki taci kuka ta gode Allah, Aisha ce in a mata take maidawa bayan sun keɓe su biyu kuma tayi ta mata bala'i akan ita bazata iya taɓuka komai ba, a haka a haka har itama ta fara maidawa daga kawaye har yan gida ya zamana ba ayi mata tayi shiru kamar da, daga baya kuma sai ya zama ƙawaye na shakkar yi mata saboda wani lokacin fuskanta kawai in mutum ya kalla yaga yanda take ɗinke ta sai yaji shakkan yi mata magana bare rashin mutunci, su Hajjah ne dai har yanzun suke fafatawa amma suma kaso 70 cikin 100 ya ragu na abunda suke mata da sbd sun san bazata ɗauka ba.
Haka sukayi sallama, kowwa ta kama hanyar gidansu a ransu sunajin matukar kewan junansu tun kafin ma su rabu.
Washegari, asubar fari, haka ta tashi sukuku duk bata da kuzari tafita tayo uzurinta ta ɗauro alwalah, nafila tayi ta zauna tana istigfari har akayi kira na biyu, tashi tayi tai raka'atan Fajr ta ɗora da sallar Asbah, bayan ta idar tayi duk abubuwan da ta sabayi na ibada dukda bata cikin yanayi mai kyau ranar, ko ayyukan da takeyi na gida bata samu daman yinsu ba. Haka ta zauna ta rafka uban tagumi, ita batama san tunanin me ya kamata tayi ba.
Ita kuwa Baba Zainu tana can, ta saki hanɗa da ganɗa tana ta sharar bacci sai uban Munshari take saki kamar wata bujimar saniya, tana tunanin baiwarta na can na mata aikin gida kamar yanda ta saba. Daman sallah sai 7 da wani abu take tashi tanayinta daga ita har yaranta, balle hassu da ba kullum take kwana a gidan ba, wani lokacin sai ace ta kwana gidan ubanta ne.
Sai ƙarfe 7 da minti shabiyar ta tashi, haka ta fito tsakar gidan tana faman mutsikka ido tana sakin hamma da miƙa, Idonta be sauka akan ko ina ba sai wurin murhu taga ba alamar ma anje wurin tun jiya. Kallon tsakar gidan tayi taga ba a share ba komai nanan yanda ta barshi jiya.
Cike da takaici tace "Kenan yau wannan yar iskar yarinyar ba Abinda tayi a gidan" Kasancewar tasan ko batayin ba, bata da yanda zatayi da ita tunda yanzun ba kamar da bane, da in batayi ba zata kamata ta jiba kuma ta sanya ta tayin dole koda bata so, sanin babu abinda zata iya akaine yasa kawai taje ta rarumi buta ta fada bayi, bayan tayo uzurinta tafito aka batsaltsala Alwallah aka shige ɗaki.
Faka-faka ta bubbuga sallah tayo waje dan tasan yaran yau sai sun makara kuma waccan shegiyar ɗiyar da ubanta bazasu bari tace kada suje ba, lokacin da take kiciniyar hura wuta, su kuma yaran suka tashi.
Ganin sai lokacin ma ake hura wuta sukace "Babarmu, yau zamusha dukan latti"
Ashar ta ɗura musu tana me daka masu tsawa akan su ɓace mata da gani dan a matukar fusace take da abunda Maryamah tayi yau, naƙin aikin gidan kuma tasan ba yanda za ayi tayi ma yarinyan magana.
Itakam Maryamah tana zaune bata ma san lokaci yaja ba ta faɗa duniyar tunani har sai da taga hasken rana ya hudo ta cikin ɗakin, yaye labulen dakin tayi tana kallon hasken ranar da yake haskaka fuskanta amma zuciyanta cike da duhu, tanaji kamar duniya ta juya mata baya in har ta tafi tabar babanta.
"Anya zan iya barin garin nan kuwa, inda na tashi tun yarinta har kawo yau, uwa uba kuma ran danafi ƙauna sama da komai a duk faɗin duniyar nan yana cikin shi wato mahaifina?!" Ta tambayi kanta cikin shakkar barin garin, amma wata zuciyarta na faɗa mata "Maryamah dole kibar garin nan kobadan kanki ba kodan kwanciyar hankalin mahaifinki, saboda halin da zuciyan mahaifinki take cikin na tsoron abunda ka iya faruwa da rayuwanki a dalilin zaman ki a garin" Wannan zuciyar nata itace ta bata ƙwarin guiwa kan cewa zata bar garin don mahaifinta da gobenta da kuma ilimin da take kwaɗayin samu, zata tafi amma ita kanta tasan zuciyanta tana tare da babanta a ko ina domin tana matuƙar ƙaunar shi sama da komai da kowwa shi ɗin duniyarta ne!!!.
Haka ta fito tsakar gidan tana
ƙarewa yaran da suke zaune suna shan koko kallo, da saurinsu har suna hada baki wajen faɗin "Addah ina kwana"
Lafiya lau ta amsa musu ta ɗora da kuyi hakuri yau na jawo maku makara, bansan time ya tafi haka ba.
Yaran take faɗawa saboda a ganinta sune dolenta, amma uwar yaran ce ta bata amsa.
wadda daman tun fitowarta take watsa mata harara da faɗan "Muguwa da baki fito kinyi musu abun karin ba ninayi, sauƙinta ma Allah ya wadatani da hannu da kuma lafiyan da zan musu ɗin" ta ƙarashe tana buga uban tsaki.
Kawar da kai Maryamah tayi saboda bata da lokacin maganganunta, ta barta ma taji da abinda ke ɗawainiya da rayuwanta mana.
Saboda kawai ta ƙara ƙular da ita tace
"Baba ina kwana" bata jira cewar taba ta wuce ɗakin babanta.
Kaman yanda tayi tsammani kuwa yaji tana zazzaga mata masifa.
Itakam ko gajiya batayi abinda ke ba Maryamah mamaki, ita bakinta da kanta baya mata ciwo matar nan kullum in ta fara masifa tun safe har dare, kai ita kam kodan kunnuwata su huta ma taji ta amince da barin gidan nan, haba ayita abu ɗaya kaman cin ƙwan makauniya.
Da wannan tunanin ta ƙarasa ƙofar ɗakin babanta tayi sallama, bata shiga ba sai da taji ya amsa yace "Shigo Maryamah"
Shiga tayi da wata gajeriyar sallama a bakinta, zama tayi kusa dashi tace "Ina kwana baba"
"Lafiya Ya kwanan fargaba?"
Ɗan murmushi tayi tace "Ai banyi ba baba"
"Anya kuwa? Idon nan naki ya nuna har kuka kinyi"
wasu hawayen ke shirin zubo mata, tana mai ƙarajin soyayya da tausayin babanta a ranta domin tasan shi kanshi ƙarfin hali yakeyi, a zuciyar ta take jinjina soyayyar mahaifin nata, shidai daban yake daga shigowar ta ya gane cewan har lokacin tana cikin dmauwa, har ma da kukan data kusan kwana tanayi, ita ko waccan baƙar matar da alama ba abunda ta fahimta, saima tuhumar ta da take akan taƙi ta fita ta mata bautan da ta saba ba tare da uzuri ba.
Haka ta zauna sukayi yar maganar da zasuyi.
"Nasan bakici abinci ba?" Ya tambaye ta yana kallon fuskar ta.
"A'a baba naƙoshi"
Murmushi yayi ya miƙa mata nashi "ga nawa nan kici babarku nasan bai zama lallai ta baki ba saboda yau baki fito kin mata aiki ba"
Cike da tausayin shi tace "A'a baba kaci nina ƙoshi"
"Karki damu kici ni yau da azumi ma na tashi na neman Allah, yasa inda zaki ya zamar miki alherin rayuwa duniya da lahira"
Cike da jin daɗi ta amsa da "Ameen babana"
Badab ranta naso ba saidan ta faranta ran mahaifin nata, ta ɗan tsakuri ɗumamen kaɗan ta kora da ruwan koko.
Bayan ta gama, baba ya kalle ta yace "Har yau baki tambayeni dalilin da yasa nace kibar gari ba?"
Ƙasa tayi da kanta tace "Ka isa ne babana, kuma ko wane hukunci ka yanke akan zinariyarka daidai ne, ita ɗin me biyayya ce gareka" Murmushi yayi yana me ƙarajin tsananin ƙaunar ɗiyar tashi da kuma tausayinta mai girman gaske akan biyayyar ta gareshi, rauni ne ke mamaye zuciyan shi amma yana ƙoƙarin karfafa ta.
Daga nan ta miƙe tace, "Umma bari naje gida dare yayi, sai da safe nagode Allah ya ƙara muku lafiya da nisan kwana"
Umma tace "Maryamah, godiyanki ta isa haka, keda Aisha duk ɗaya kuke a wajena abinda zan yi wa Aisha shi zanyi miki, koba dan abotar dake tsakaninku da Aisha ba, ko dan zaman mutuncin da mukayi da mahaifiyarki, tunda Allah ya sa suka zo garin nan, mun yi mutunci da ita har zuwa ranar da ta bar duniya, Allah ya jiƙanta, mace mai matuƙar mutunci da yakana, ga haƙuri da gudun zuciya, Kuje kawai, dare yayi Allah ya yi miki albarka, ya tsareki da tsarewarsa"
Ameen duk suka haɗa baki suka amsa. Aisha na binta don ta ɗan taka mata…..
FULANI
08082101373
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
https://chat.whatsapp.com/Kqi1tusHnZa6SHgbTgFqlr?mode=gi_t
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO 🦋✨
BY RABIA'TU KABIRU ACHADU (FULANI)
YOUNG TALANTED WRITER'S ASSOCITION YOTA
SADAUKARWA GARE KI HALIMA HASHEEM (MIEMIEN HABIBI)&❤️ AHMAD JAMIL AHMAD (HABIBI)♥️
FULANI ❣️
08082101373
✨🦋 RANTSATSTSEN RABO 🦋 ✨
PAGE 8️⃣
A hanya ma haka suke ji tamkar kar su rabu amma ba yanda suka iya sunzo daidai inda ba nisa daga nan zuwa gidansu Maryamah da kuma ita Aishan
Dakatawa sukayi da tafiya suka riƙe hannun juna.
A'isha ce ta kalleta tace "Sahiba ji nake kamar na biki mu tafi tare"
Murmushi tayi "kinjita kamar gaske"
yar dariya tayi "Allah da gaske"
Ganin A'ishan tayi kalar tausayi ne yasa ta fara mata magana cikin sigar tsoakana "Ba wani abu kika sani ma, koda naje ƙura ta lafa na gudo in dawo gida, ko in naga mutanen gidan basu da kirki wallahi guduwa zanyi dan ba yanda za ayi na tsaya a wulaƙantani, ke kinsan ma zuciyata bazata dauka ba"
Yanda maryaman tayi magana ne yasa tayi dariya "Sauran kije kina musu girman kai da wulakanci in miki ta bakin Hajjah"
Kusan a tare suka saki dariya "saifa abinda suka gani, nidai bazan ɗauki wulaƙanci ba, duk kuɗin mutum atohhhh"
"Insha Allah ma mutanen kirki ne zakiji dadin zama a cikinsu"
"Allah yasa kije gida kawai gobe kafin mutafi ko kinje school zan biki can in kara ganinki"
"Tabb ai wallahi gobe babu inda zani sai naga tashin motan ku dan har tasha zan biku"
Murmushi Maryamah tayi tana jinjina girman ƙaunar da Aisha ke mata, itafa zata iya sadaukar da komai saboda ita kuma tun suna yara suka tashi haka suna masu tsananin ƙaunar junansu, saboda Aisha take surutu, kasancewar ta bakin ta baya shiru, koba kayi niyyar magana ba saita saka ka kayi dolen ka, kuma saboda ita ta koyi buɗe baki ta mayar da magana in su Hajjah sun mata abu, wanda da ko kasheta zasuyi akan abun da batayi ba bazata bud6e baki ta kare kanta ba sai dai in an gama jibgarta ta shiga daki taci kuka ta gode Allah, Aisha ce in a mata take maidawa bayan sun keɓe su biyu kuma tayi ta mata bala'i akan ita bazata iya taɓuka komai ba, a haka a haka har itama ta fara maidawa daga kawaye har yan gida ya zamana ba ayi mata tayi shiru kamar da, daga baya kuma sai ya zama ƙawaye na shakkar yi mata saboda wani lokacin fuskanta kawai in mutum ya kalla yaga yanda take ɗinke ta sai yaji shakkan yi mata magana bare rashin mutunci, su Hajjah ne dai har yanzun suke fafatawa amma suma kaso 70 cikin 100 ya ragu na abunda suke mata da sbd sun san bazata ɗauka ba.
Haka sukayi sallama, kowwa ta kama hanyar gidansu a ransu sunajin matukar kewan junansu tun kafin ma su rabu.
Washegari, asubar fari, haka ta tashi sukuku duk bata da kuzari tafita tayo uzurinta ta ɗauro alwalah, nafila tayi ta zauna tana istigfari har akayi kira na biyu, tashi tayi tai raka'atan Fajr ta ɗora da sallar Asbah, bayan ta idar tayi duk abubuwan da ta sabayi na ibada dukda bata cikin yanayi mai kyau ranar, ko ayyukan da takeyi na gida bata samu daman yinsu ba. Haka ta zauna ta rafka uban tagumi, ita batama san tunanin me ya kamata tayi ba.
Ita kuwa Baba Zainu tana can, ta saki hanɗa da ganɗa tana ta sharar bacci sai uban Munshari take saki kamar wata bujimar saniya, tana tunanin baiwarta na can na mata aikin gida kamar yanda ta saba. Daman sallah sai 7 da wani abu take tashi tanayinta daga ita har yaranta, balle hassu da ba kullum take kwana a gidan ba, wani lokacin sai ace ta kwana gidan ubanta ne.
Sai ƙarfe 7 da minti shabiyar ta tashi, haka ta fito tsakar gidan tana faman mutsikka ido tana sakin hamma da miƙa, Idonta be sauka akan ko ina ba sai wurin murhu taga ba alamar ma anje wurin tun jiya. Kallon tsakar gidan tayi taga ba a share ba komai nanan yanda ta barshi jiya.
Cike da takaici tace "Kenan yau wannan yar iskar yarinyar ba Abinda tayi a gidan" Kasancewar tasan ko batayin ba, bata da yanda zatayi da ita tunda yanzun ba kamar da bane, da in batayi ba zata kamata ta jiba kuma ta sanya ta tayin dole koda bata so, sanin babu abinda zata iya akaine yasa kawai taje ta rarumi buta ta fada bayi, bayan tayo uzurinta tafito aka batsaltsala Alwallah aka shige ɗaki.
Faka-faka ta bubbuga sallah tayo waje dan tasan yaran yau sai sun makara kuma waccan shegiyar ɗiyar da ubanta bazasu bari tace kada suje ba, lokacin da take kiciniyar hura wuta, su kuma yaran suka tashi.
Ganin sai lokacin ma ake hura wuta sukace "Babarmu, yau zamusha dukan latti"
Ashar ta ɗura musu tana me daka masu tsawa akan su ɓace mata da gani dan a matukar fusace take da abunda Maryamah tayi yau, naƙin aikin gidan kuma tasan ba yanda za ayi tayi ma yarinyan magana.
Itakam Maryamah tana zaune bata ma san lokaci yaja ba ta faɗa duniyar tunani har sai da taga hasken rana ya hudo ta cikin ɗakin, yaye labulen dakin tayi tana kallon hasken ranar da yake haskaka fuskanta amma zuciyanta cike da duhu, tanaji kamar duniya ta juya mata baya in har ta tafi tabar babanta.
"Anya zan iya barin garin nan kuwa, inda na tashi tun yarinta har kawo yau, uwa uba kuma ran danafi ƙauna sama da komai a duk faɗin duniyar nan yana cikin shi wato mahaifina?!" Ta tambayi kanta cikin shakkar barin garin, amma wata zuciyarta na faɗa mata "Maryamah dole kibar garin nan kobadan kanki ba kodan kwanciyar hankalin mahaifinki, saboda halin da zuciyan mahaifinki take cikin na tsoron abunda ka iya faruwa da rayuwanki a dalilin zaman ki a garin" Wannan zuciyar nata itace ta bata ƙwarin guiwa kan cewa zata bar garin don mahaifinta da gobenta da kuma ilimin da take kwaɗayin samu, zata tafi amma ita kanta tasan zuciyanta tana tare da babanta a ko ina domin tana matuƙar ƙaunar shi sama da komai da kowwa shi ɗin duniyarta ne!!!.
Haka ta fito tsakar gidan tana
ƙarewa yaran da suke zaune suna shan koko kallo, da saurinsu har suna hada baki wajen faɗin "Addah ina kwana"
Lafiya lau ta amsa musu ta ɗora da kuyi hakuri yau na jawo maku makara, bansan time ya tafi haka ba.
Yaran take faɗawa saboda a ganinta sune dolenta, amma uwar yaran ce ta bata amsa.
wadda daman tun fitowarta take watsa mata harara da faɗan "Muguwa da baki fito kinyi musu abun karin ba ninayi, sauƙinta ma Allah ya wadatani da hannu da kuma lafiyan da zan musu ɗin" ta ƙarashe tana buga uban tsaki.
Kawar da kai Maryamah tayi saboda bata da lokacin maganganunta, ta barta ma taji da abinda ke ɗawainiya da rayuwanta mana.
Saboda kawai ta ƙara ƙular da ita tace
"Baba ina kwana" bata jira cewar taba ta wuce ɗakin babanta.
Kaman yanda tayi tsammani kuwa yaji tana zazzaga mata masifa.
Itakam ko gajiya batayi abinda ke ba Maryamah mamaki, ita bakinta da kanta baya mata ciwo matar nan kullum in ta fara masifa tun safe har dare, kai ita kam kodan kunnuwata su huta ma taji ta amince da barin gidan nan, haba ayita abu ɗaya kaman cin ƙwan makauniya.
Da wannan tunanin ta ƙarasa ƙofar ɗakin babanta tayi sallama, bata shiga ba sai da taji ya amsa yace "Shigo Maryamah"
Shiga tayi da wata gajeriyar sallama a bakinta, zama tayi kusa dashi tace "Ina kwana baba"
"Lafiya Ya kwanan fargaba?"
Ɗan murmushi tayi tace "Ai banyi ba baba"
"Anya kuwa? Idon nan naki ya nuna har kuka kinyi"
wasu hawayen ke shirin zubo mata, tana mai ƙarajin soyayya da tausayin babanta a ranta domin tasan shi kanshi ƙarfin hali yakeyi, a zuciyar ta take jinjina soyayyar mahaifin nata, shidai daban yake daga shigowar ta ya gane cewan har lokacin tana cikin dmauwa, har ma da kukan data kusan kwana tanayi, ita ko waccan baƙar matar da alama ba abunda ta fahimta, saima tuhumar ta da take akan taƙi ta fita ta mata bautan da ta saba ba tare da uzuri ba.
Haka ta zauna sukayi yar maganar da zasuyi.
"Nasan bakici abinci ba?" Ya tambaye ta yana kallon fuskar ta.
"A'a baba naƙoshi"
Murmushi yayi ya miƙa mata nashi "ga nawa nan kici babarku nasan bai zama lallai ta baki ba saboda yau baki fito kin mata aiki ba"
Cike da tausayin shi tace "A'a baba kaci nina ƙoshi"
"Karki damu kici ni yau da azumi ma na tashi na neman Allah, yasa inda zaki ya zamar miki alherin rayuwa duniya da lahira"
Cike da jin daɗi ta amsa da "Ameen babana"
Badab ranta naso ba saidan ta faranta ran mahaifin nata, ta ɗan tsakuri ɗumamen kaɗan ta kora da ruwan koko.
Bayan ta gama, baba ya kalle ta yace "Har yau baki tambayeni dalilin da yasa nace kibar gari ba?"
Ƙasa tayi da kanta tace "Ka isa ne babana, kuma ko wane hukunci ka yanke akan zinariyarka daidai ne, ita ɗin me biyayya ce gareka" Murmushi yayi yana me ƙarajin tsananin ƙaunar ɗiyar tashi da kuma tausayinta mai girman gaske akan biyayyar ta gareshi, rauni ne ke mamaye zuciyan shi amma yana ƙoƙarin karfafa ta.