← Book details Rabon Kwado Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 24

Sashe 24

Rabon Kwado Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read

To Nana rayuwa take da dadi ba dadi gidan auren ta haryanzu babu abinda yasauya zani tsakanin su kuma babu wanda yataba sani har kawo iyau sau daya muhammad yabar meenal taje gurin nana shima don yaji labarin baya nan ne yousep din,
Kimanin wata uku kenan da tafiyar yousep din training na Army shima ze gaji mahaifin sa, yau takama friday kuma ze dawo, tunda suka tashi ake shirya masa abin cin cika kala kala, kullum cikin mom cikin tsuma sirikar tata take da magun guna dagyarata hakan kuwa yasoma yima nana aiki sosai, tarasa yadda zatayi ta fadawa mom irin zaman dasukeyi da dan nata, ga magun gunan datake dirka mata suna sakata feeling sosai, seda suka gama aiki ne zataje tayi wanka mom takirata dakin ta kamar kullum tabata wani abu a bowl tace tashanye shi kafin ta tafi,
Kallon bowl din nana tafara kamar tayi kuka saboda tagaji kam gaskiya, da mamaki mom tace." Wai nana meyasa ke bakisan gyara kanki ne kamar ba wayay ya, sekace bakisan yadda mazan nan na zamani suke bah mussam man nawa dan ma a gurinki kullum burina shine na kankaro miki mutumci amma ke gani kike kamar ina takura miki " jikin nana a sanyaye tasoma magana don dole yau tasanar mata abinda yake faruwa bazata yadda ta cuci kanta aita dirka mata abinda ze ringa hanata bacci tana fama da ciwon mara." Mom kiyi hakuri bahaka bane wlh baki fahimce ni bane inasone mugama daidaita tsakanin mu dashi tukunna komeye mah senayi"

Mikewa mom tayi cikin wani yanayi tace "nana mekike nufi?" shiru tayi mata kawai ta sukuyar dakanta kasa, cikin tsareta da idanu mom tace nana gaya min tsakaninki da Allah yousep yataba kwanciya dake ko a ah Kada yimin karya ki gayamin gaskiya,
Jikin nana a sanyaye ta girgiza mata kai, cikin kaduwa kuwa mom tasaki bowl din hannun nata tana salati, idonta taf da kwallah tace." Lallai yousep yau ka tabbatar min da kai ba yaron arziki bane aikuwa wlh kataro wa kanka yau zaka hadu dani sena bala in bata maka rai mara mutumcin yaro, kiyi hakuri nana tunfar ko dakin yimin nayani daban ringa baki abubuwa bah haka"
Jikin nana a sanyaye tace." Bakomai mom pls kada kiyi masa maganar ranshi ya baci insha Allah zamu daidaita kanmu" sakin baki mom tayi tana kallonta cikin zuciyanta kuwa tana jara gidewa Allah daya bawa dan nata mata me kaunarshi da gaskiya,
Cikin shan mur mom tace." Kina nufin nakyaleshi muzuba muku ido yana daukar alhakin ki,sam naze yiwubah" idon nana tafda kwallah tace "Na rokeki mom ki kyaleshi karkice mishi komai zamu daidai ta ni baya daukar alhaki nah ina yimasa uzuri" ganin nana dagaske take ta dage ne yasata kyaleta tashiga wanka....

TAKU A KULLUM NANA BMB

08147110349

TSOKACI!!

Daga sabon book dina mesuna.

JARABTAR MU

Love story

Hannu yasa yakama kuma tunta gami da sakar mata murmushin dayake tafiya da zuciyan ta aduk sanda yayi shi,cikin sanya yay yar muryar sa yace." my beautiful wife ya kike?" kasa jurema kallon sa tayi ta lumshe idanun ta, seda yakare mata kallo tukunna ya hura mata iska a face din tata bashiri tabude idonta, murmushin kawai yayi yakoma kan kujera yazauna gami da gyaran murya yace." mufeeda ina mummy? kafin tayi magana sukaji saukowan ta daga sama yakuwa zuba mata idanu harta zauna shikuma yasauka kasa yazauna yana me gaisheta, sedai ko inda yake bata kalla bah don dama tuni annurin fuskarta yadauke na ganin shi datayi, ita da mufeeda TV kawai suka zubawa ido duk da ita rabin hankalin ta nakanshi tana satar kallon shi, seda ya sauke ajiyan zuciya yace." mummy kinga JARAFTAR MU! mu kuma" muryanshi sosai ta canza kamar zeyi kuka yacigaba dacewa" Heedaya ta haifamin 'yan uku yau"
Suduka cikin firgici suke kallon sa, tsam mufeeda ta mike tazo ta tsugunna gefensa tace." Ya adnan kasan abinda kake cewa kuwa? kuka mummy tafara tana cewa." Allah ya isanmu Adnan shikenan ka gurbata mana zuri armu ka lalata mana suna, 'ya'yan zina a cikin family din mu! INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI UN! shikawai take nana tawa, " Kacuci rayuwarka Adnan da tuni matarka mufeeda keda wan nan yaran! tahanyar zina zaka fara tara naka iyalin wan nan waca irin kaddarar rayuwace?.....

LITTAFIN JARABTAR MU! NA KUDINE ZEZO MUKU A FARASHI ME SAUKI👌

ALLAH KASA MU DACE DUNIYA DA LAHIRA!
Chapter 24 · 0% Book details