← Book details Rabon Kwado Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 24

Sashe 20

Rabon Kwado Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sam meenal bata kula da wata auntie safiyya bah se yanzun shikuwa muhammad tun shigowan sa yaganta yasan sunyi gwari, mikewa meenal tayi saboda mamaki tace mamma! wai dama bake bace a parlour? ummi ce!" yanzu muketa hira da ita ba keba!
murmushi tayi tace." To laifine don kunyi hira da ita?" jiki a sanyaye meenal tace a ah, mamaki gaba daya ya dabai bayeta,daddy ne ya kalleta yace." meenal kina nufin har twins basu gane ummin bah?" dariya muhammad yay yace." Wlh daddy bawanda yagane ta sun dage sunata zuba mata shagaba"

Dariya sosai daddy yayi yace." Kai ammad dai safiyya 'ya'yanki sunji kunya wlh" murmushi takuma yi tace." Eh to mudin aka gaya muku na wasane" yadda tayi magar harda juya idanu tabasu dariya daddy yace." Inafa na wasa tunda har twins dina suka kasa tan tanceki,"
tana dariya tamike tace barima naje naga autata nayi kewan ta sosai jiya ta yini babu mamanta"
Binta daddy yayi yana cewa aikuwa baza ayi babu niba bari nazo naga yadda idanun twins zasuyi" yana fita su muhammad suka rufa masa baya suna cewa suma baza ah barsu a bayaba😅😅!

TAKU A KULLUM NANA BMB

08147110349

TSOKACI!!

Daga sabon book dina mesuna.

JARABTAR MU

Hannu yasa yakama kuma tunta gami da sakar mata murmushin dayake tafiya da zuciyan ta aduk sanda yayi shi,cikin sanya yay yar muryar sa yace." my beautiful wife ya kike?" kasa jurema kallon sa tayi ta lumshe idanun ta, seda yakare mata kallo tukunna ya hura mata iska a face din tata bashiri tabude idonta, murmushin kawai yayi yakoma kan kujera yazauna gami da gyaran murya yace." mufeeda ina mummy? kafin tayi magana sukaji saukowan ta daga sama yakuwa zuba mata idanu harta zauna shikuma yasauka kasa yazauna yana me gaisheta, sedai ko inda yake bata kalla bah don dama tuni annurin fuskarta yadauke na ganin shi datayi, ita da mufeeda TV kawai suka zubawa ido duk da ita rabin hankalin ta nakanshi tana satar kallon shi, seda ya sauke ajiyan zuciya yace." mummy kinga JARAFTAR MU! mu kuma" muryanshi sosai ta canza kamar zeyi kuka yacigaba dacewa" Heedaya ta haifamin 'yan uku yau"
Suduka cikin firgici suke kallon sa, tsam mufeeda ta mike tazo ta tsugunna gefensa tace." Ya adnan kasan abinda kake cewa kuwa? kuka mummy tafara tana cewa." Allah ya isanmu Adnan shikenan ka gurbata mana zuri armu ka lalata mana suna, 'ya'yan zina a cikin family din mu! INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI UN! shikawai take nana tawa, " Kacuci rayuwarka Adnan da tuni matarka mufeeda keda wan nan yaran! tahanyar zina zaka fara tara naka iyalin wan nan waca irin kaddarar rayuwace?.....

LITTAFIN JARABTAR MU! NA KUDINE ZEZO MUKU A FARASHI ME SAUKI👌

ALLAH KASA MU DACE DUNIYA DA LAHIRA!
[8/31, 3:39 PM] Nana BMB: ❣ RABON KWADO....!!

BOOK 3

NA NANA BMB

GARKUWA WRITTER'S ASSOCIATION
{ Marubuta masu garkuwa da alkalami domin fadakar da al'ummah }

page 45 - 46

Koda mujaheed yatafi bajumawa muhammad yaraka sameer da iyalansa suka tafi suma mummy tanatayi musu godiya suduka saboda sunji dadi sosai abinda sukayi musu komai dasu akaita kujiba kujiba, zara kuwa maman ta tace tayi zamanta gurin mom kafin sugama case dinta da imam.
Meenal suna zaune a parlour tunda tayi musu girgi suka zauna hira itada 'yan kanen nata sallah kawai take tadasu tunda take bata tabajin farin ciki makaman cin wan nan bah wai itace haka da kanne sun zagaye ta anata hira dukda rashin magana ta usain sakewa yayi shima abinsa anata hira yini daya wata irin shakuwa me karfi ce tashiga tsakanin su, nabiha tanata zuba musu shagwaba har suka nufi makwanci meenal tanata lallabata tayi bacci sannan ta tashi tana nata shirin baccin tana cikin zura rigar baccin tane wayan ta ta soma ruri, koda ta isa ga wayan tagame kiran nata idanunta ta rintse donji takema kamar bazata iyay masa maganaba, seda kiran yakusa tsikewa tadaga, a yadda take masa magana ne tabashi dariya duk da haka yacigaba da janta da hira,

Bangaren Dr maryam kuwa 'yan hospital lamarin sedai du a ei don tunda ta tashi taketa wasu irin surutai matasa kan gado tana ambatun safiyya sokana iri iri gashi anyi faman duniya tashiga wanka takiyi har nurses aka kira sumata tanemi ma ta dakesu dole haka aka kyaleta mahaifiyar Dr tayi kuka harta gaji saboda kamai daya faru kawu musa yagaya mata harda abinda tayiwa safiyya da hukuncin da daddy ya yanke kan cewar ta rasu, abin yataba mata zuciya sosai hakanne yasata tafiya gida tabarta a nan se matar kawu musa itama jikinta yayi sanyi don tana zaune yabada labarin, nana tayi kukan itama harta siki sedai hawaye tsoron duniya yana kara kamata wai yau auntien tace takoma haka, sosai abin yake daga mata hankali ita kadaice yanzu gurinta saboda matar kawu musan ma tunda ta tafi yo girki bata dawoba shi daddy kashe wayan sa yayi donkar su kirashi yace hutawa shima zeyi abinsa ya gaji.

A hankali mujaheed ya bude kofa yashiga yamaidata ya kulle kaitsaye kitchen ya wuce da ledojin hannunsa ya aje su, yana shiga bedroom yahangeta tawani cure guri daya can gefen gadon zuwa lokacin bacci yasoma figarta sam bataji shigowar saba sedai taji ya jaye bargon jikinta firgigit tamike zaune suka hada ido yana mata murmushi yabata umarnin ta tashi tayo alwala wucewa yay yafara yo alwalar don ywtsaya kallonta kam alwalan nan bazata yiwu bah bare sallah!
Koda ta dauro alwala hijab tazura haryana jan kasa, koda suka idar dasallan gefenta ya juya yasoma zuba mata addu ah wanda hakanne yasa hawaye fara bulbulowa daga idanun ta don tasoma ganin take taken na mijin nata, seda yagama addu ah suka shafa tare, kana kuma yasoma zaiyano mata tsarikan shi da abinda yakeso da wanda bayaso don a fahimtar juna har yanzu dasaura a tsakaninsu, to amma sedai sannu sannu bata hana zuwa,
kitchen yawuce yaje yajuyo musu lafiyayyan kaza a tray da sauran drinks daya shigo dasu yana dawowa yaganta harta koma ta kudun dune, seda ya rage kayan jikinshi tukunna yaje cak yadauko ta a bed din ya zare hajib din nata tayi saurin matse jikinta gami da rufe idonta ganin yadda bakaya a jikinsa se boxer, zaunar da ita yayi dakanshi yabata kazar tanaci eanda tsoro da fargaba sam yahanata tantance dadin kazar haka yake turo mata, seda suka gama tsaf yace to taje takai kwanukan kitchen,

Nokewa tayi kamar zatayi kuka cikin tura baki tace." Nidai tsoro nakeji bazan iya zuwaba"
Mujaheed yasauke ajiyan zuciya yana murmushi me sauti saboda yasan kome takeyi wa sam batason tashi yaganta ahaka ne,mikewa yay gamida kamata yace " to muje narakaki " Bayadda ta iya dole ta dauki tray din yasata a gaba yana binta a baya ahankali take tafiya dukdan kada jikinta ya motsa sedai ta makaro don tuni ta kamar masa da yawun baki, koda suka dawo wucewa yay bayi ya wanke bakinsa gamida watsa ruwa yafito daure da towel seda yagama kashe light na ko ina yadawo yafesa turare yaje yazauna gefenta tana jinshi kuwa tasake kudun dunewa kamar wata alkaki tsoron da yaga yakama ta ne dayawa yasa shi mikewa yace." So u need to sleep, bari na lullube ki se Allah yakaimu" kods mimi taji haka wani irin dadine ya cikata rufeta yay abinsa yadauki laptop dinsa yana aiki Sosai ya juma yana dannata har mimi tayi bacci kana ya kashetabya ajiye, dama dagashi se towel yahau kan bed din cikin bacci mimi tajee hannun mujaheed ko ina yana zagawa ajikinta zuciyanta yasoma wani bugu jin irin rikon daya mata dakyar take motsi ma hatta suturar tama yaraba ta dasu,
To daganan kuma salo yasauya takunsa, dole mimi tana kuka ta saduda domin ganin babu sauki se gurin Allah dole tayi hakuri tabashi hakkin sa don taga al amarin mijin nata babbane, tausayin tane yakamashi hakan yasa ya kyaleta tsam ya matseta a jikinsa domin kam shifa harga Allah tsokalowa kansa yayi kamar beyi komai bama yakeji, mimi ita kadai tasan halin da take ciki ayanzun ajiyan zuciya kawai tame saukewa na kukan da tayi ga tsoron daya kara shigarta hankalinta ya tashi jin haryanzu joystick din mijin nata taki la asar 😅! tana cikin wan nan tunanin ne taji yayi sama da ita zuwa bathroom seda ya tsarkake jikinsa tukunna yahada mata ruwa me dan zafi yafito yabarta don yaga yace zemata wankan ma zasu shawota ganin yanzuma tabi ta nade jikinta, tana kuka tana wankan tana tunanin yanzun wan nan rayuwar zata cigaba dayi da mijin nata, kafin ta fito ya gyara bed din, da dan towel dinta tafito tana tafiya tana cije baki be bari tatsaya yin komaiba yakama mata hannu suka kwanta, dukda halin da take ciki kalaman mujaheed seda suka sanyaya mata zuciya irin dada dan kalaman dayake mata da addu ah.

Washe gari

Tunda muhammad yatashi ya kagu a shirya a tafi saboda da begen matarsa shima yay bacci jiya, su auntie safiyya sun hana kowa shiga part din amarya kowa shirinsa yake a nan gurin mummy se 11 da wani abu mujaheed yashigo bangaren nasu lokacin ma har kowa ya gama shirin sa na tafiya annurin fuskar sa kawai zaka kalla kasan yacika ango, hakanne yasa mummy binsa da wani irin kallo, sosai kunya yakamashi yana gama gaishesu ya wuce dakinsa yasami muhammad a kwance, yana ganinsa yasaki murmushi yana cewa " Ango ango kasha kamshi" Haba mujaheed yarike cikin shakiyan cinsa yace." Ah! Sosai kuwa niko nasha kamshi malam kabari kawai"

Dariya muhammad yay yace." To wai wai shiru dae wai uwar kwagwa ta mutu, jarabar data taso seta kwanta, ya kanwar tawa ina fata dai lpy koh"
Mujaheed yana shafa kansa yace "Amarya tana lpy smul don tama fika lpy" hararar sa kawai muhammad yay yace " wlh karya kake rainawa wasu hankali amma baniba"
Yana dariya yace "wai ina sameer ne?"
" Sun tafi gidansu suma ko tsayawa zasuyi jiranka"

Mujaheed yace " Kawai dai guduwa yay ashe kuma koyw tsaya muyi sallama dasu mom"

" Bakasan inda suke bane" muhammad yafada yana hararar sa,keya mujaheed ya soso yana murmushi yace "kuma yanzu mummy tace wai zaku wuce"
Chapter 20 · 0% Book details