Sashe 17
Miji Goma Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Maryam ta dage ta dinga zayyanowa Murja jawabai, tana kwaɗaita mata yadda rayuwar zawarci take, Uwani ƙarshe tashi ta yi ta fice daga ɗakin, ta fara kiciniyar ɗora girki gabanta yana faɗuwa da fargabar kar fa Maryam ta yiwa Murja huɗuba, ta zo ta kashe aurenta ta rasa miji, tun da dama can sai da ta basu rubutun farinjini suka samu mijin, tana buduruwa ma kenan, ina ga yanzu da ta yi haihuwa huɗu? Lallai dole ta yi wa tufkar hanci, amma ta yadda Maryam ba za ta gano komai ba.
Ta ƙwallawa Murjar kira, ta fito, Uwani ta rufe ta da faɗa"Kin shige ɗaki kin bar ni da aiki, ni zan yi muku girkin kenan ko? Sai surutan banza kuke yi kamar yau kuka taɓa sanin juna?"
Maryam ma ta fito, Uwani ta ƙaƙalo murmushi ta ce"La Maryam ba da ke nake ba, ke ai kin yi nauyi, ina ke ina aiki? Ki koma ki yi kwanciyarki".
Maryam ta koma tana tunanin shin ta zuga Murja ta kaso aurenta saboda Uwani ta ɗanɗani baƙinciki, ko kuwa Murjar za ta kalla da matsayin ƴan'uwantaka da ke tsakaninsu ta ƙyale ta?
*Mun kusa gama free page fa, za ku iya biyan kuÉ—in karatunku 500 kacal ta nan*
8028966015
Sadiya Abdulrazak opay
Ko ta nan
1869739740
Sadiya Abdulrazak access bank
08028966015
[2/11, 4:53 PM] Sadiya abdulrazak: *MIJI GOMA...*
_(BA UBA GOMA BA NE)_
*SADIYA ABDULRAZAƘ*
*Ƴan magana dai sun ce "Miji goma ba uba goma ba ne" Shin kun yarda? Sannan mene ne hikimar wannan maganar? Kun yarda da ingancinta? Ta kai a kafa hujja da ita a ƙi zaman aure?*
Marubuciyar
ZUCIYAR MACE
WUTAR ƘAIƘAYI
DA WALAKIN...
WANI AUREN
IYA RUWA
MATAR SHIGE. da sauransu
*FIRST CLASS WRITERS*
https://chat.whatsapp.com/G08KLEmlF3gJ3X4npkfIee
PAGE 12
Jin shiru babu motsinsu a tsakar gidan sai ta leƙo ta kuwa ga wayam, alamun suna cikin ɗaki, ta fito ta nufi ɗakin ta laɓe jikin labule tana sauraron su, daidai sanda Uwani take cewa"Shi ne za ki biyewa shirmenta? Ita ba ki ga kalarta ba? Kin manta da farinjininta? Ko kin manta sai da na karɓo muku taimako kafin ki samu mijin? Kina buduruwa ma kenan, ina ga kin zama bazawara? Maza ki tattara ki koma ɗakinki, kishiya ba kanki farau ba, ni ma na zauna da ita ballantana ke!".
Murja ta ce"Amma babarmu..."
Ta daka mata tsawa ta ce"Rufe mini baki! Wallahi sai kin koma, uzuri ɗaya kawai zan yi miki za ki zauna har sai ya zo biko, amma yana zuwa to wallahi ƙafarki ƙafar shi, ni za ki ja wa abun magana a gari?"
Daga nan Maryam ta ja ƙafa ta koma ɗaki jiki a sanyaye, sannan ta yi kokowa da zuciyarta da take ta faɗa mata ta zuga Murja, ta raya a ranta ƴar'uwarta ce, idan ta cuce ta kanta ta cuta, haka kuma idan an kasa gulmarta a tire ba za ta ji daɗi ba, don haka ta share su, kwananta biyu a gidan mijin ya zo, ai kuwa ko Baba ma bai shiga zancen ba, ita ce ta sasanta su, ta bi shi suka tafi, suka ci gaba da zamansu shiru abunsu.
Nasiru ya zo ya kawowa Maryam kayan abinci, sannan ya ba ta kuɗi don a yi siyayyar jariri, a haka rayuwa ta ci gaba da tafiya har Allah Ya sauke ta lafiya, ta haifi ɗanta namiji, aka yi suna yaro ya ci sunan mahaifin Nasiru Yusufa, suna ce masa Abba, duk wata sai ya zo ya ba ta dubu ashirin, amma sam bai yi zancen kome ba, wanda a lokacin a yadda Maryam take ƙishin yin aure da burin ta yi zaman aure babu abin da zai hana ta yarda ta koma gidan nasa, sau tari takan tuna da Nazifi ta ce dama ya dawo ya ce ta koma da za ta zauna da Gwaggo lafiya, to amma damarta ta wuce sai dai ta gaba, sai ta ci gaba da kula da ɗanta, ta kuma koma kasuwancinta, tana ra adana ribarta.
Taimako É—aya da Allah Ya yi mata ma shi ne tana da farinjinin masoyan, wannan karon ma tun kafin ta yaye Abba maza suka fara sallama da ita, sai dai ta ce musu sai ta yaye É—anta. Akwai wani Alhaji Haruna da suka haÉ—u da shi a kasuwa, ya fi kowa naci cikin masu sonta, don har cewa ya yi zai aure ta a hakan, amma ta ce a'a sai ta yaye, ita bai ma wani kwanta mata sosai ba, saboda yana da matarsa da Æ´aÆ´a huÉ—u, ita kuma tana da kishi, sam ba ta son zama da kishiya, amma ta sani tun da ita ma yanzu ba buduruwa ba ce dole ta jingine burinta a gefe, aurenta uku da Æ´aÆ´a biyi ba zai yiwu ta ce sai saurayi ba, don haka take É—an kula shi.
Sanda ta yaye Abba ta fara zancen aure sai Nasiru ya ce to zai ɗauki ɗansa, don har ma ya yi wani auren, nan Uwani ta fara subaɗaɗi tana cewa a bar mata shi, a cewarta yaron ya shiga ranta, ba za ta iya rabuwa da shi ba, ita kuma Maryam ta fi zargin wannan dubu ashirin ɗin da yake kawowa duk wata ce ta ruɗe ta, don haka ta ce a'a gara ya ɗauke shi ɗin, ba ta so a ɗora mata wahala, haka dai Nasiru ya ɗauki ɗansa, gidan iyayensa ya kai shi, tun da ba a daɗe da yin auren na shi ba, kar ya hana su cin amarci, duk sati ake kawo mata yaran nata su wuni wataran ma su kwana ɗaya sai a mayar da su, tana jin babu daɗi a ranta, saboda fargabar yadda tarbiyyar yaran za ta kasance, idan ba ƙaddara ba me zai saka uwa tana raye a raba ta da ɗanta? Haka dai take danne damuwarta tana bin su da addu'a, kwanciyar hankalinta ɗaya ce duk mariƙan yaran suna son su, ba ta ga alamar wahala a tare da su ba.
Wata ɗaya da mayar da Abba, Alhaji Haruna ya zo da zancen aure faka-faka, ya ce sati biyu za a saka, Maryam da yake har lokacin ba sosai take son shi ba sai ta fara yi masa kwana-kwana, a wannan karon aure take son yi na har abada, saboda haka yana da kyau ta samu wanda zuciyarta ta amince da shi ɗari bisa ɗari, shi auren wanda kake yi wa so sahihi fa yana da alfanu, saboda idan zama ya yi zama saɓani ya fara shiga tsakaninku wannan son da kake yiwa mutum yana taka muhimmiyar rawa wajen haƙurtar da zuciyarka ka ci gaba da zama da shi, kana jure wasu abubuwa, saɓanin wacce ta yi auren manufa babu son miji a zuciyarta, daga wannan abin da ta aure shi don shi ya gushe, shikenan sai ta tsane shi, tun da dama babu so tun farko, idan kuwa ka tsani mutum ba za ka taɓa yi masa uzuri ba, komai ya yi na laifi sai ka yi masa hukunci.
Ƙiri-ƙiri Uwani ta nuna ba ta son wannan auren, saboda ganin yadda Alhaji Haruna yake son Maryam kamar bai taɓa aure ba, sai bushasha yake yi mata da kuɗi kamar ba ya so, da alama duk ya fi mazajen ƴaƴanta rufin asiri, dama mijin Mardiyya shi ne abun tutiyarta da nunawa a gari ƴarta ta yi goshi tana auren mai kuɗi, sai ga shi Maryam za ta dusashe tauraruwar Mardiyyar, don haka ta ɗauki hassadar duniya ta saka a ranta, ta yi ta zuga Maryam a kan kar ta aure shi, ta ce"Ke yanzu Maryam da ajinki da kyaunki da komai za ki auri babban mutum mai mata da ƴaƴa huɗu? Ni sai nake ganin kamar kin faɗo"
Maryam ta yi murmushi ta ce"Ba faɗuwa ba ne babarmu, kin ga zaman gidan ba shi da wani amfani, kuma idan kika duba kika gani ni ma fa kullum ƙara girma nake, ban yi ƙanƙantar da za a ce Alhaji ya yi mini girma ba, saboda haka wannan ba komai ba ne, Allah dai ya ba mu zaman lafiya".
Uwani ta ce"Amma Maryam za ki iya zaman kishi kuwa? Ba mu san halin matarsa ba".
Ta ce"Babu ruwana da ita, ba zamanta nake yi ba, idan kin ji kanmu to ita ce ta so hakan".
Duk inda ta yi sai Maryam ta tare, haka dai ta rabu da ita ta zubawa sarautar Allah ido, tana jira a yi auren ta ji ta ina matsala za ta fara, ita dai ta san a yadda ta tafi haka za ta dawo, ko ta dawo da ciki ta ƙara haihuwa a gida, haka za ta yi ta rabon yara gida-gida.
Sai da Alhaji Haruna ya je wajen Baba da ƙoƙon bara kan a yi wa Maryam magana ta amince da auren da wuri, saboda babu amfanin jinkirtawar, Baba ya zaunar da Maryam ya yi mata nasiha sosai, saboda ya yaba da hankalin mutumin, kuma shi ma a yanzu ya fi so ta auri babba, kamar zai fi haƙuri da halinta, saɓanin yara da ƙuruciya kawai ake zabgawa a zaman auren, ya faɗawa Maryam shi Alhajin ya ce zai yi mata komai na kayan ɗaki, don haka ba ta da wani uzuri na cewa ba ta shirya ba, ta ce shikenan ta amince, Baba sai ya bi ta da kallon tausayi, ba ya jin daɗin wannan mace-macen auren nata, ga shi kwana biyun nan ya ganta duk a sanyaye kamar tana da wata damuwa, duka ta rage tsiwa har ma yawon bin ƙawaye.
Yayin da Maryam ta amince da auren Alhaji Haruna, shi kuma yana can ana gumurzu a gidan shi, matar shi Rabi masifaffiyar mace ce, tun da ya yi zancen ƙara auren shikenan ta kasa zaune ta kasa tsaye, sai tijara take yi, amma shi ya ce mata aure babu gudu ba ja da baya, sai ya yi, wannan ne karo na uku da yake niyyar yin aure, amma sai ta je gidan su yarinyar ta tada tarzoma har a fasa, don haka wannan karon sai ya zaɓi sanarwa Maryam halinta.
Ta ƙwallawa Murjar kira, ta fito, Uwani ta rufe ta da faɗa"Kin shige ɗaki kin bar ni da aiki, ni zan yi muku girkin kenan ko? Sai surutan banza kuke yi kamar yau kuka taɓa sanin juna?"
Maryam ma ta fito, Uwani ta ƙaƙalo murmushi ta ce"La Maryam ba da ke nake ba, ke ai kin yi nauyi, ina ke ina aiki? Ki koma ki yi kwanciyarki".
Maryam ta koma tana tunanin shin ta zuga Murja ta kaso aurenta saboda Uwani ta ɗanɗani baƙinciki, ko kuwa Murjar za ta kalla da matsayin ƴan'uwantaka da ke tsakaninsu ta ƙyale ta?
*Mun kusa gama free page fa, za ku iya biyan kuÉ—in karatunku 500 kacal ta nan*
8028966015
Sadiya Abdulrazak opay
Ko ta nan
1869739740
Sadiya Abdulrazak access bank
08028966015
[2/11, 4:53 PM] Sadiya abdulrazak: *MIJI GOMA...*
_(BA UBA GOMA BA NE)_
*SADIYA ABDULRAZAƘ*
*Ƴan magana dai sun ce "Miji goma ba uba goma ba ne" Shin kun yarda? Sannan mene ne hikimar wannan maganar? Kun yarda da ingancinta? Ta kai a kafa hujja da ita a ƙi zaman aure?*
Marubuciyar
ZUCIYAR MACE
WUTAR ƘAIƘAYI
DA WALAKIN...
WANI AUREN
IYA RUWA
MATAR SHIGE. da sauransu
*FIRST CLASS WRITERS*
https://chat.whatsapp.com/G08KLEmlF3gJ3X4npkfIee
PAGE 12
Jin shiru babu motsinsu a tsakar gidan sai ta leƙo ta kuwa ga wayam, alamun suna cikin ɗaki, ta fito ta nufi ɗakin ta laɓe jikin labule tana sauraron su, daidai sanda Uwani take cewa"Shi ne za ki biyewa shirmenta? Ita ba ki ga kalarta ba? Kin manta da farinjininta? Ko kin manta sai da na karɓo muku taimako kafin ki samu mijin? Kina buduruwa ma kenan, ina ga kin zama bazawara? Maza ki tattara ki koma ɗakinki, kishiya ba kanki farau ba, ni ma na zauna da ita ballantana ke!".
Murja ta ce"Amma babarmu..."
Ta daka mata tsawa ta ce"Rufe mini baki! Wallahi sai kin koma, uzuri ɗaya kawai zan yi miki za ki zauna har sai ya zo biko, amma yana zuwa to wallahi ƙafarki ƙafar shi, ni za ki ja wa abun magana a gari?"
Daga nan Maryam ta ja ƙafa ta koma ɗaki jiki a sanyaye, sannan ta yi kokowa da zuciyarta da take ta faɗa mata ta zuga Murja, ta raya a ranta ƴar'uwarta ce, idan ta cuce ta kanta ta cuta, haka kuma idan an kasa gulmarta a tire ba za ta ji daɗi ba, don haka ta share su, kwananta biyu a gidan mijin ya zo, ai kuwa ko Baba ma bai shiga zancen ba, ita ce ta sasanta su, ta bi shi suka tafi, suka ci gaba da zamansu shiru abunsu.
Nasiru ya zo ya kawowa Maryam kayan abinci, sannan ya ba ta kuɗi don a yi siyayyar jariri, a haka rayuwa ta ci gaba da tafiya har Allah Ya sauke ta lafiya, ta haifi ɗanta namiji, aka yi suna yaro ya ci sunan mahaifin Nasiru Yusufa, suna ce masa Abba, duk wata sai ya zo ya ba ta dubu ashirin, amma sam bai yi zancen kome ba, wanda a lokacin a yadda Maryam take ƙishin yin aure da burin ta yi zaman aure babu abin da zai hana ta yarda ta koma gidan nasa, sau tari takan tuna da Nazifi ta ce dama ya dawo ya ce ta koma da za ta zauna da Gwaggo lafiya, to amma damarta ta wuce sai dai ta gaba, sai ta ci gaba da kula da ɗanta, ta kuma koma kasuwancinta, tana ra adana ribarta.
Taimako É—aya da Allah Ya yi mata ma shi ne tana da farinjinin masoyan, wannan karon ma tun kafin ta yaye Abba maza suka fara sallama da ita, sai dai ta ce musu sai ta yaye É—anta. Akwai wani Alhaji Haruna da suka haÉ—u da shi a kasuwa, ya fi kowa naci cikin masu sonta, don har cewa ya yi zai aure ta a hakan, amma ta ce a'a sai ta yaye, ita bai ma wani kwanta mata sosai ba, saboda yana da matarsa da Æ´aÆ´a huÉ—u, ita kuma tana da kishi, sam ba ta son zama da kishiya, amma ta sani tun da ita ma yanzu ba buduruwa ba ce dole ta jingine burinta a gefe, aurenta uku da Æ´aÆ´a biyi ba zai yiwu ta ce sai saurayi ba, don haka take É—an kula shi.
Sanda ta yaye Abba ta fara zancen aure sai Nasiru ya ce to zai ɗauki ɗansa, don har ma ya yi wani auren, nan Uwani ta fara subaɗaɗi tana cewa a bar mata shi, a cewarta yaron ya shiga ranta, ba za ta iya rabuwa da shi ba, ita kuma Maryam ta fi zargin wannan dubu ashirin ɗin da yake kawowa duk wata ce ta ruɗe ta, don haka ta ce a'a gara ya ɗauke shi ɗin, ba ta so a ɗora mata wahala, haka dai Nasiru ya ɗauki ɗansa, gidan iyayensa ya kai shi, tun da ba a daɗe da yin auren na shi ba, kar ya hana su cin amarci, duk sati ake kawo mata yaran nata su wuni wataran ma su kwana ɗaya sai a mayar da su, tana jin babu daɗi a ranta, saboda fargabar yadda tarbiyyar yaran za ta kasance, idan ba ƙaddara ba me zai saka uwa tana raye a raba ta da ɗanta? Haka dai take danne damuwarta tana bin su da addu'a, kwanciyar hankalinta ɗaya ce duk mariƙan yaran suna son su, ba ta ga alamar wahala a tare da su ba.
Wata ɗaya da mayar da Abba, Alhaji Haruna ya zo da zancen aure faka-faka, ya ce sati biyu za a saka, Maryam da yake har lokacin ba sosai take son shi ba sai ta fara yi masa kwana-kwana, a wannan karon aure take son yi na har abada, saboda haka yana da kyau ta samu wanda zuciyarta ta amince da shi ɗari bisa ɗari, shi auren wanda kake yi wa so sahihi fa yana da alfanu, saboda idan zama ya yi zama saɓani ya fara shiga tsakaninku wannan son da kake yiwa mutum yana taka muhimmiyar rawa wajen haƙurtar da zuciyarka ka ci gaba da zama da shi, kana jure wasu abubuwa, saɓanin wacce ta yi auren manufa babu son miji a zuciyarta, daga wannan abin da ta aure shi don shi ya gushe, shikenan sai ta tsane shi, tun da dama babu so tun farko, idan kuwa ka tsani mutum ba za ka taɓa yi masa uzuri ba, komai ya yi na laifi sai ka yi masa hukunci.
Ƙiri-ƙiri Uwani ta nuna ba ta son wannan auren, saboda ganin yadda Alhaji Haruna yake son Maryam kamar bai taɓa aure ba, sai bushasha yake yi mata da kuɗi kamar ba ya so, da alama duk ya fi mazajen ƴaƴanta rufin asiri, dama mijin Mardiyya shi ne abun tutiyarta da nunawa a gari ƴarta ta yi goshi tana auren mai kuɗi, sai ga shi Maryam za ta dusashe tauraruwar Mardiyyar, don haka ta ɗauki hassadar duniya ta saka a ranta, ta yi ta zuga Maryam a kan kar ta aure shi, ta ce"Ke yanzu Maryam da ajinki da kyaunki da komai za ki auri babban mutum mai mata da ƴaƴa huɗu? Ni sai nake ganin kamar kin faɗo"
Maryam ta yi murmushi ta ce"Ba faɗuwa ba ne babarmu, kin ga zaman gidan ba shi da wani amfani, kuma idan kika duba kika gani ni ma fa kullum ƙara girma nake, ban yi ƙanƙantar da za a ce Alhaji ya yi mini girma ba, saboda haka wannan ba komai ba ne, Allah dai ya ba mu zaman lafiya".
Uwani ta ce"Amma Maryam za ki iya zaman kishi kuwa? Ba mu san halin matarsa ba".
Ta ce"Babu ruwana da ita, ba zamanta nake yi ba, idan kin ji kanmu to ita ce ta so hakan".
Duk inda ta yi sai Maryam ta tare, haka dai ta rabu da ita ta zubawa sarautar Allah ido, tana jira a yi auren ta ji ta ina matsala za ta fara, ita dai ta san a yadda ta tafi haka za ta dawo, ko ta dawo da ciki ta ƙara haihuwa a gida, haka za ta yi ta rabon yara gida-gida.
Sai da Alhaji Haruna ya je wajen Baba da ƙoƙon bara kan a yi wa Maryam magana ta amince da auren da wuri, saboda babu amfanin jinkirtawar, Baba ya zaunar da Maryam ya yi mata nasiha sosai, saboda ya yaba da hankalin mutumin, kuma shi ma a yanzu ya fi so ta auri babba, kamar zai fi haƙuri da halinta, saɓanin yara da ƙuruciya kawai ake zabgawa a zaman auren, ya faɗawa Maryam shi Alhajin ya ce zai yi mata komai na kayan ɗaki, don haka ba ta da wani uzuri na cewa ba ta shirya ba, ta ce shikenan ta amince, Baba sai ya bi ta da kallon tausayi, ba ya jin daɗin wannan mace-macen auren nata, ga shi kwana biyun nan ya ganta duk a sanyaye kamar tana da wata damuwa, duka ta rage tsiwa har ma yawon bin ƙawaye.
Yayin da Maryam ta amince da auren Alhaji Haruna, shi kuma yana can ana gumurzu a gidan shi, matar shi Rabi masifaffiyar mace ce, tun da ya yi zancen ƙara auren shikenan ta kasa zaune ta kasa tsaye, sai tijara take yi, amma shi ya ce mata aure babu gudu ba ja da baya, sai ya yi, wannan ne karo na uku da yake niyyar yin aure, amma sai ta je gidan su yarinyar ta tada tarzoma har a fasa, don haka wannan karon sai ya zaɓi sanarwa Maryam halinta.