Sashe 12
Miji Goma Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta ce"Hamza ashe haka kake ba ka da kirki ba ka san ya kamata ba? Yanzu idan da tausayi ina ta wahala da cikinka za ka kalle ni ka ce na cire shi? To bari ka ji na faÉ—a maka, ko cikin shege na yi ba zan cire shi ba sai na haife shi, ballantana na halak, idan ka ga ba za ka iya zama da ni a haka ba ka sallame ni, ba a kanka na fara rabuwa da miji ba, miji goma ba uba goma ba ne!".
Tun da ta furta masa ba shi da kirki ya kafe ta da ido cike da mamaki, duk da ya san Maryam ko a wajen siyar da abinci ba kanwar lasa ba ce amma bai yi zaton za ta iya kallon mijinta ta ce masa ba shi da kirki ba, ya ce"Kina cikin hayyacinki kuwa? Ni ne ba ni da kirki?"
Tana yi masa wani mugun kallo ta ce"Akwai ƙarshen rashin kirkin da ya fi wannan? Ina fama da cikinka a maimakon ka tausaya mini sai ka ce a cire?"
Ya ce"Kin ga, ni fa ba tausayinki ne ba na yi ba, kawai dai dama can na tsara idan na yi aure matata ba za ta haihu da wuri ba".
Ta ce"To da ka san haka me ya hana ka zuge tazugen wandonka? Ai ka ga da ba zan ma samu cikin ba ballantana ka ce a zubar na ƙi".
Ya yi shiru ya rasa abun cewa, ta ce"Hamza! Na aureka ne saboda ina sonka, wallahi son da nake yi maka ba zai saka na ɗauki wulaƙanci daga gareka ba, idan ka san ba za ka iya ba tun wuri ka sallame ni, na je na raini cikina a gaban iyayena".
Tsaki kawai ya yi ya tashi ya fita.
Yana fita kuwa ta ɗakko waya, ta kira babarta ta juye mata komai, Uwani a zaune take amma sai da ta miƙe tsaye, a ranta tana faɗin 'lokaci ya yi'
Ta ce"Innalillahi! Ke dai Maryam ba kya dacen mazan aure, shi kuma ba ya son haihuwa? To ai har gara ma Nazifin shi matsalar babar shi ne, shi fa miji da ba ya son haihuwa ya fi uban kowa matsala a rayuwar aure, kin ga wannan maganar ma ai ba ta waya ba ce, gobe zan zo mu baje ta a faifai, ina! Ai ba ki ga wajen zama ba".
Maryam ta ce"To Allah Ya kaimu".
Haka kuwa aka yi, washegari da yamma ta je gidan nata, tana ganinta ta fara salati tana tafe hannu ta ce"Maryam kin ga yadda kika zama kuwa? Kamar wata horuwa! Mun shiga uku, nan duk cikin ne babu yunwa?"
Ba ta ce komai ba, ta gaishe ta ta kawo mata ruwa da abinci, ta ce"Ai Maryam ba zan iya cin komai ba, wai me ma kika ce mini? Har ya ce a cire cikin?"
Ta ce"Haka ya ce, ni kuwa babu mai saka ni na cire cikin nan wallahi!".
Uwani gabanta ya faÉ—i jin ba za ta yarda a cire cikin ba, ta san halin Maryam sarai idan ba ta son abu babu wanda zai mata dole, sai dai da siyasa da dabara.
Ta ce"Maryam kin san matsalar wanda ba ya son haihuwa kuwa? Kin ga na farko dai idan kika samu ciki a wulaƙance zai dinga kallonki, ga wahalar laulayi ga wulaƙanci da rashin kulawa, irin su gani suke ma asara ce su kashewa cikin kuɗi, sai ki ga mace idan ba sana'a take yi ba zuwa awo ma ya gagare ta, wani kuma hanawa zai yi ko da kuɗin nata, ke akwai wacce tana naƙuda mijin ya kulleta a ɗaki tana ihu tana magiya har sai da ta haifo ɗan ya mutu sannan ya buɗe..."
Dariyar da Maryam ta yi ce ta katse ta daga shararo ƙaryarta, ta ce"Maryam! Dariya ma kike yi?"
Maryam ta ce"To ai abun dariya ma ya bani, ya rufe ta a É—aki fa?"
Ta ƙara sautin dariyar ta ce"Lallai wannan ba shi da kirki, ai kuwa da ni ce idan na fito kai ma sai na shaƙe ka ka mutu".
Uwani ta ce"Kina wasa da iskancin maza, to ai ni ba ma wannan gaɓar ce ta fi damuna ba, kin san kuwa idan aka haifi ɗan shi da babu duk ɗaya a wajensa? Wallahi ko sutura ba yi masa zai yi ba, wani ma sai ki ga yana tsangwamar yaron kamar ba jininsa ba, wani agolan ma ya fi shi gata, sannan kina nan zaune sake da baki zai auro yarinya ta yi planing su yi ta soyayyarsu suna ƙunsa miki takaici".
Maryam ta ce"Kamar dole? Wallahi babu namijin da zai yi mini haka".
Uwani ta ce"To kuwa maganin kar a yi kar a fara, muddin ba za ki iya ɗaukar wannan ba gara ma ki cire cikin nan, kuma ki nemi saki, don haihuwa da irin wannan mijin ba ƙaramar matsala ba ce".
Maryam ta ce"Ni fa ba zan cire cikin nan ba, haka kawai nake jin ina son abin da zan haifa, idan na haihu komai sai ya biyo baya".
Uwani ta ce"Kina nufin za ki jure cin mutuncin shi kafin haihuwar?"
Ta ce"Ba zai ma fara ba".
Duk ta inda Uwani ya ɓullo sai Maryam ta kauce, saboda ita ba za ta zubar da ciki ba, don haka Uwani ta tattara ta tafi, lokacin dab da sallar magriba.
A ƙofar gida suka yi kiciɓus da Hamza zai shiga, ya rage tsayi ya gaishe ta, ta amsa tana cewa"Ya mai jikin?"
Ya ce"Da sauƙi".
Ta ce"Ai yau dai na ce bari na zo na duba ta, ashe haka ta zama ta yi yarab kamar haihuwa ta goma? Na ci to Hamza dai sai haƙuri ba a samu damar angwancewa ba, to wannan yaushe mutum ta tada komaɗarsa? Ana ta jigilar amai da yawu".
Hamza ya ce"Wallahi kuwa, sai haƙuri".
Ta ce"Haƙuri ya zama dole ai, tun da abun nata na gado ne, uwarta ma fa haka ta yi, idan ta samu ciki duk haƙurin Malam sai ya ƙosa, ƙarshe daina rabon kwana yake da ita, kuma ba ma wannan ba, haka take haifo ɗan a yaƙune da cutar tamowa, duk mutuwa suka yi sai Maryam ɗin ce ta rayu, amma fa ta ci wuya, an kashe kuɗi maƙudai, idan aka kwantar da ita kamar gawa, a yaƙune, uwar ta sha mantawa ta fizgota ta yi zaton zani ne babu mutum a ciki".
Hamza ya cika da mamakin surutun matar nan, gefen zuciyarsa kuwa cike yake da tsoron kar a haifo masa É—a irin wannan.
Ta ƙara da faɗin"Kai dai ka fara banki kawai, don da alama ita ma gado ta yo, sai anjima Allah Ya sawaƙe".
Ya ce"Bari na raka ki titi".
Suna tafe tana ƙara zuga shi da ƙarairayi kala-kala, shi kuwa ya hau kai ya zauna daram, ya sake jin haushin Maryam da ƙin zubar da cikin da ta yi, ya samar mata adaidaita sahu ya biya kuɗin sannan ya koma gida.
Ya tarar da ita tana sallah, ya yi alwala shi ma ya fita masallaci, da ya dawo ya zauna ta kawo masa abinci, ya ci kaɗan, saboda yanzu abincin nata ma ƙyanƙyamin shi yake ji saboda amai da tofe-tofen yawun da take yi, shi a yadda yake jin labarin haihuwa wannan jinin biƙin da sauransu bai ma san yadda zai zauna da ita inuwa ɗaya ba idan ta haihu, dole dai ta tafi gida dab da za ta haihu, idan ɗan ya yi wata uku sai ta dawo, saboda shi ko wata mata ce a unguwarsu take siyar da wani abu, daga ranar da aka ce ta haihu to fa ya daina siyan abu a wajenta, ƙyanƙyami yake ji, har sai ya manta ɗan ta ɓa girma sannan ya ci gaba da siya, ballantana kuma a ce matarsa wacce dole ya ci abincinta.
Ya yi nisa a duniyar tunani ya ji muryar Maryam ta ce"Wai me yasa yanzu ka rage cin abinci?"
Ya ce"Babu komai".
Sannan ya tashi ya fice daga gidan.
Tun daga ranar ya yi mugun jan baya da ita, duka ya canza mata, a da yana biyo ta ɗakin da ta koma da kwana su kwana tare ko ba ta so, daga baya ya daina, tsakaninta da shi da safe idan ya fito zau tafi aiki ya zauna ya karya, da yana dawowa ya ci na rana daga baya ya daina, sai na dare shi ma ba kullum yake ci ba, sannan ba ya dawowa gidan da wuri, sai ya kai sha biyu a waje, kuma tun da gara ta ƙare ta lura shi mutum ne mai maƙo da bin diddigin abinci, idan ya auno shinkafa kwana ɗaya sai ya yi ta mitar ta ƙare da wuri, ya ce duk cikin nan ne yake saka ta cin abinci, idan ta yi faɗawa Uwani ba ta ba ta shawarar komai sai ta cire ciki, wanda ita kuma ba ta so, don haka ma ta daina faɗa mata komai, jira take kawai ta haihu ya sake ta ta ƙara gaba.
Cikin yana wata biyar wataran ya shigo mata da balangu da lemo, ta manta rabon da ya siyo mata nama, ko ƴar kankana da lemon nan ba ya siyo mata, cike da marmari kuwa ta cinye tass, ta shanye lemon dama jarka ɗaya ne, babu jimawa kuwa ta fara jin ciwon mara, abu kamar wasa ciwon yana ra ƙaruwa, fitsari ya matseta, tana shiga banɗaki ta ga jini, ga shi ita kaɗai a gidan, ta nemo wayarta don ta sanar masa ta rasa ta, don ya ɗauka ya fita da ita, a tunaninta ba za ta nemi wata mafitar ba sai ta zauna har cikin ya zube.
Da ta ga abun ba na wasa ba ne, sai ta saka hijjabinta ta tafi gidan iyayen shi, da yake ba su da nisa, a jigace ta shiga gidan, tana shiga ta durƙushe a gaban Umman shi dake zaune a tabarma tare da ƙannen shi, da yake da hasken wutar nefa ta gane ta, ta ɗago ta tana faɗin"Maryam lafiya?"
Ta ce"Marara ciwo take kuma na ga jini".
Umma ta hau salati ta ce"Tashi mu tafi asibiti wannan ai ba ƙaramar matsala ba ce".
Tun da ta furta masa ba shi da kirki ya kafe ta da ido cike da mamaki, duk da ya san Maryam ko a wajen siyar da abinci ba kanwar lasa ba ce amma bai yi zaton za ta iya kallon mijinta ta ce masa ba shi da kirki ba, ya ce"Kina cikin hayyacinki kuwa? Ni ne ba ni da kirki?"
Tana yi masa wani mugun kallo ta ce"Akwai ƙarshen rashin kirkin da ya fi wannan? Ina fama da cikinka a maimakon ka tausaya mini sai ka ce a cire?"
Ya ce"Kin ga, ni fa ba tausayinki ne ba na yi ba, kawai dai dama can na tsara idan na yi aure matata ba za ta haihu da wuri ba".
Ta ce"To da ka san haka me ya hana ka zuge tazugen wandonka? Ai ka ga da ba zan ma samu cikin ba ballantana ka ce a zubar na ƙi".
Ya yi shiru ya rasa abun cewa, ta ce"Hamza! Na aureka ne saboda ina sonka, wallahi son da nake yi maka ba zai saka na ɗauki wulaƙanci daga gareka ba, idan ka san ba za ka iya ba tun wuri ka sallame ni, na je na raini cikina a gaban iyayena".
Tsaki kawai ya yi ya tashi ya fita.
Yana fita kuwa ta ɗakko waya, ta kira babarta ta juye mata komai, Uwani a zaune take amma sai da ta miƙe tsaye, a ranta tana faɗin 'lokaci ya yi'
Ta ce"Innalillahi! Ke dai Maryam ba kya dacen mazan aure, shi kuma ba ya son haihuwa? To ai har gara ma Nazifin shi matsalar babar shi ne, shi fa miji da ba ya son haihuwa ya fi uban kowa matsala a rayuwar aure, kin ga wannan maganar ma ai ba ta waya ba ce, gobe zan zo mu baje ta a faifai, ina! Ai ba ki ga wajen zama ba".
Maryam ta ce"To Allah Ya kaimu".
Haka kuwa aka yi, washegari da yamma ta je gidan nata, tana ganinta ta fara salati tana tafe hannu ta ce"Maryam kin ga yadda kika zama kuwa? Kamar wata horuwa! Mun shiga uku, nan duk cikin ne babu yunwa?"
Ba ta ce komai ba, ta gaishe ta ta kawo mata ruwa da abinci, ta ce"Ai Maryam ba zan iya cin komai ba, wai me ma kika ce mini? Har ya ce a cire cikin?"
Ta ce"Haka ya ce, ni kuwa babu mai saka ni na cire cikin nan wallahi!".
Uwani gabanta ya faÉ—i jin ba za ta yarda a cire cikin ba, ta san halin Maryam sarai idan ba ta son abu babu wanda zai mata dole, sai dai da siyasa da dabara.
Ta ce"Maryam kin san matsalar wanda ba ya son haihuwa kuwa? Kin ga na farko dai idan kika samu ciki a wulaƙance zai dinga kallonki, ga wahalar laulayi ga wulaƙanci da rashin kulawa, irin su gani suke ma asara ce su kashewa cikin kuɗi, sai ki ga mace idan ba sana'a take yi ba zuwa awo ma ya gagare ta, wani kuma hanawa zai yi ko da kuɗin nata, ke akwai wacce tana naƙuda mijin ya kulleta a ɗaki tana ihu tana magiya har sai da ta haifo ɗan ya mutu sannan ya buɗe..."
Dariyar da Maryam ta yi ce ta katse ta daga shararo ƙaryarta, ta ce"Maryam! Dariya ma kike yi?"
Maryam ta ce"To ai abun dariya ma ya bani, ya rufe ta a É—aki fa?"
Ta ƙara sautin dariyar ta ce"Lallai wannan ba shi da kirki, ai kuwa da ni ce idan na fito kai ma sai na shaƙe ka ka mutu".
Uwani ta ce"Kina wasa da iskancin maza, to ai ni ba ma wannan gaɓar ce ta fi damuna ba, kin san kuwa idan aka haifi ɗan shi da babu duk ɗaya a wajensa? Wallahi ko sutura ba yi masa zai yi ba, wani ma sai ki ga yana tsangwamar yaron kamar ba jininsa ba, wani agolan ma ya fi shi gata, sannan kina nan zaune sake da baki zai auro yarinya ta yi planing su yi ta soyayyarsu suna ƙunsa miki takaici".
Maryam ta ce"Kamar dole? Wallahi babu namijin da zai yi mini haka".
Uwani ta ce"To kuwa maganin kar a yi kar a fara, muddin ba za ki iya ɗaukar wannan ba gara ma ki cire cikin nan, kuma ki nemi saki, don haihuwa da irin wannan mijin ba ƙaramar matsala ba ce".
Maryam ta ce"Ni fa ba zan cire cikin nan ba, haka kawai nake jin ina son abin da zan haifa, idan na haihu komai sai ya biyo baya".
Uwani ta ce"Kina nufin za ki jure cin mutuncin shi kafin haihuwar?"
Ta ce"Ba zai ma fara ba".
Duk ta inda Uwani ya ɓullo sai Maryam ta kauce, saboda ita ba za ta zubar da ciki ba, don haka Uwani ta tattara ta tafi, lokacin dab da sallar magriba.
A ƙofar gida suka yi kiciɓus da Hamza zai shiga, ya rage tsayi ya gaishe ta, ta amsa tana cewa"Ya mai jikin?"
Ya ce"Da sauƙi".
Ta ce"Ai yau dai na ce bari na zo na duba ta, ashe haka ta zama ta yi yarab kamar haihuwa ta goma? Na ci to Hamza dai sai haƙuri ba a samu damar angwancewa ba, to wannan yaushe mutum ta tada komaɗarsa? Ana ta jigilar amai da yawu".
Hamza ya ce"Wallahi kuwa, sai haƙuri".
Ta ce"Haƙuri ya zama dole ai, tun da abun nata na gado ne, uwarta ma fa haka ta yi, idan ta samu ciki duk haƙurin Malam sai ya ƙosa, ƙarshe daina rabon kwana yake da ita, kuma ba ma wannan ba, haka take haifo ɗan a yaƙune da cutar tamowa, duk mutuwa suka yi sai Maryam ɗin ce ta rayu, amma fa ta ci wuya, an kashe kuɗi maƙudai, idan aka kwantar da ita kamar gawa, a yaƙune, uwar ta sha mantawa ta fizgota ta yi zaton zani ne babu mutum a ciki".
Hamza ya cika da mamakin surutun matar nan, gefen zuciyarsa kuwa cike yake da tsoron kar a haifo masa É—a irin wannan.
Ta ƙara da faɗin"Kai dai ka fara banki kawai, don da alama ita ma gado ta yo, sai anjima Allah Ya sawaƙe".
Ya ce"Bari na raka ki titi".
Suna tafe tana ƙara zuga shi da ƙarairayi kala-kala, shi kuwa ya hau kai ya zauna daram, ya sake jin haushin Maryam da ƙin zubar da cikin da ta yi, ya samar mata adaidaita sahu ya biya kuɗin sannan ya koma gida.
Ya tarar da ita tana sallah, ya yi alwala shi ma ya fita masallaci, da ya dawo ya zauna ta kawo masa abinci, ya ci kaɗan, saboda yanzu abincin nata ma ƙyanƙyamin shi yake ji saboda amai da tofe-tofen yawun da take yi, shi a yadda yake jin labarin haihuwa wannan jinin biƙin da sauransu bai ma san yadda zai zauna da ita inuwa ɗaya ba idan ta haihu, dole dai ta tafi gida dab da za ta haihu, idan ɗan ya yi wata uku sai ta dawo, saboda shi ko wata mata ce a unguwarsu take siyar da wani abu, daga ranar da aka ce ta haihu to fa ya daina siyan abu a wajenta, ƙyanƙyami yake ji, har sai ya manta ɗan ta ɓa girma sannan ya ci gaba da siya, ballantana kuma a ce matarsa wacce dole ya ci abincinta.
Ya yi nisa a duniyar tunani ya ji muryar Maryam ta ce"Wai me yasa yanzu ka rage cin abinci?"
Ya ce"Babu komai".
Sannan ya tashi ya fice daga gidan.
Tun daga ranar ya yi mugun jan baya da ita, duka ya canza mata, a da yana biyo ta ɗakin da ta koma da kwana su kwana tare ko ba ta so, daga baya ya daina, tsakaninta da shi da safe idan ya fito zau tafi aiki ya zauna ya karya, da yana dawowa ya ci na rana daga baya ya daina, sai na dare shi ma ba kullum yake ci ba, sannan ba ya dawowa gidan da wuri, sai ya kai sha biyu a waje, kuma tun da gara ta ƙare ta lura shi mutum ne mai maƙo da bin diddigin abinci, idan ya auno shinkafa kwana ɗaya sai ya yi ta mitar ta ƙare da wuri, ya ce duk cikin nan ne yake saka ta cin abinci, idan ta yi faɗawa Uwani ba ta ba ta shawarar komai sai ta cire ciki, wanda ita kuma ba ta so, don haka ma ta daina faɗa mata komai, jira take kawai ta haihu ya sake ta ta ƙara gaba.
Cikin yana wata biyar wataran ya shigo mata da balangu da lemo, ta manta rabon da ya siyo mata nama, ko ƴar kankana da lemon nan ba ya siyo mata, cike da marmari kuwa ta cinye tass, ta shanye lemon dama jarka ɗaya ne, babu jimawa kuwa ta fara jin ciwon mara, abu kamar wasa ciwon yana ra ƙaruwa, fitsari ya matseta, tana shiga banɗaki ta ga jini, ga shi ita kaɗai a gidan, ta nemo wayarta don ta sanar masa ta rasa ta, don ya ɗauka ya fita da ita, a tunaninta ba za ta nemi wata mafitar ba sai ta zauna har cikin ya zube.
Da ta ga abun ba na wasa ba ne, sai ta saka hijjabinta ta tafi gidan iyayen shi, da yake ba su da nisa, a jigace ta shiga gidan, tana shiga ta durƙushe a gaban Umman shi dake zaune a tabarma tare da ƙannen shi, da yake da hasken wutar nefa ta gane ta, ta ɗago ta tana faɗin"Maryam lafiya?"
Ta ce"Marara ciwo take kuma na ga jini".
Umma ta hau salati ta ce"Tashi mu tafi asibiti wannan ai ba ƙaramar matsala ba ce".