Sashe 16
Miji Goma Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nan fa marasa ilimi suka ƙara gasgata lallai aljani ne ya auri Hansatu, bayan ta fita daga takaba babu zato babu tsammani mijin Uwani ya ce zai aure ta, Uwani irin matan nan ne ma su tsananin kishi don haka ta girgiza matuƙa da jin zancen, ta tada hankali ta ce ba ta san zance ba, a cewarta Hansatu fa aljani ne ya aure ta, idan ya aure ta shi ma mutuwa zai yi, shi kenan ya bar ta da marayun ƴaƴa, ta ci kuka ta yi magiya, shi kuwa namiji idan ya so ƙara aure babu mai hana shi sai Allah, don haka ya ɗaura ɗamara, musamman da ya kasance ita Hansatu tana son shi ta karɓe shi hannu biyu-biyu, duk kuwa da caccakar da ake ta yi masu a gari ita da iyayenta na cewar za su yi auren cin amana, a haka dai aka yi auren nan tun da Allah Ya ƙaddara, kuma ana yi aka samu rabon cikin Maryam.
Sam ba a ga miciji a zaman nasu, duk yadda Hansatu ta so su sasanta Uwani ta ƙi ba ta dama, masifar yau da ban ta gobe da ban, a haka har aka haifi Maryam, sai kuma Allah Ya jarabci Uwani da son Maryam, idan ta rarrafo ta fito waje haka za ta ɗauke ta, sai ta ga fitowar Hansatu sannan ta ajiye ta ta shige ɗaki, to da Maryam ta girma take shiga ɗakin Uwani sai suka ja ta a jiki sosai, yaran suka haɗe kansu kamar ba ƴaƴan kishiyoyi ba, shekarar Maryam bakwai a duniya mahaifiyarta ta rasu, wajen haihuwa ta biyu, dama tun farkon cikin ya zo da matsala, kuma Allah Ya yi cikin ma abokin tafiya ne, ba ta haihu ba ta rasu, kuma dama tun da ta fara naƙuda aka tabbatar ɗan ya mutu a cikinta.
Kowa ya ji tausayin Æ´ar marainiyar nan Maryam, mutane sun yi mamakin yadda Uwani ta saka ta a jikinta ta rungume tsam, ta hana dangin babarta tafiya da ita, dama shi ma Baba ya hana, saboda ya san kishin Uwani da uwar kawai take yi tana son Æ´ar, haka aka bar mata Maryam, ana ta yabonta a gari, ita kuwa ta haÉ—e ta da Æ´aÆ´anta aka ci gaba da yaruwa.
Sai dai me? Mayam ita ce ƙarama a kan ƴaƴan Uwani Mardiyya da Murja, amma samari ita suke hari tun tana ƙwailarta, ita a tunaninta Maryam za ta yo ƙashin baƙin jini irin na babarta, sai ga shi ta ga saɓanin hakan, nan hassada ta fara shiga zuciyarta sannu-sannu, ta fara jin haushin Maryam ɗin, su kuwa su Mardiyya ba su damu ba, don sun ɗauki Maryam ƙanwarsu kamar uwa ɗaya suke, sai Uwani ta dinga nuna musu suna cikin matsala sanadin haka, a cewarta babarta ce kafin ta rasu take yi mata maganin farinjini, su dai ba su saka a ka ba.
Da farko sai ta samu Baba kamar abun arziƙi take nuna masa illar wannan farin jinin na Maryam, ta ce tana da ƙuruciya mazan za su iya amfani da wannan damar su hillace ta, saboda haka a samu wani Malamin wanda zai iya dakatar da maza daga kanta zuwa sanda za ta yi hankali ta isa aure, Baba ya nuna sam bai yarda ba, duk da shi ma abun yana ba shi tsoro, musamman da ya kasance ita ta fi ta zakka da sauran yaran gidan, ita ba ta jin magana sosau, ga yawon bin gidajen ƙawaye, wani feleƙe da rawar kai da son girma ga kwalliya kamar babbar budurwa, Baba ya ce ko maza dubu ne za su zo babu wani dakatarwar Malami da ake buƙata, tun da dai ba zance ta fara yi a ɓoye ba, to a barwa Allah komai, kuma ba yanzu zai yi mata aure ba ai, sai ta gama sakandari, haka Uwani ta haƙura ta bar zancen.
Amma ta kasa haƙura, sai da ƙawarta ta zuga ta ta karɓo rubutun farinjini take bawa ƴaƴanta ba tare da sanin Maryam ba, a haka dai har suka samu mijin, a rana ɗaya aka haɗa na Mardiyya da Murja, dama daga su sai Maryam sannan ƙaramar ƴarta Fatima, wanda tsirarsu kaɗan ne da Maryam, don bai kai shekara ba.
To ita ma Maryam ɗin da yake ba ta jin magana, sam babu auren a gabanta, duk wanda zancen aure ne ya kawo shi ba ta fiya sauraron shi ba, tun ba a farga ba har aka gane, Uwani ta fara farinciki tana tunanin ƙila ita ma ƙaddararsu ɗaya da mahaifiyarta.
A hankali shaiɗan ya tunzurata, take tuna auren da ta kira da na cin amanarta da aka yi tsakanin ƙawarta da mijinta, ta ji a ranta lokaci ya zo da ya kamata ta ɗauki fansa a kan Maryam, ta yi ta tunanin abin da za ta yi mata, kafin ta yanke shawarar hana ta zaman aure, ba ta yin shirya kuma ba ta so ta yi a kan Maryam, sannan idan ta yi mata cutarwa ta ƙiri-ƙiri mutane za su gane da wuri, a yi mata terere, ta ruguje yardar da aka yi mata akan Maryam, shiyasa ta ga gara ta yi mata kisan mummuƙe, ta so a ce ta ƙi aure kamar babarta, yadda za ta fake da dama gado ta yi, sai ga shi ta tsayar da Nazifi, don bayan auren ƙanwarta Fatima sai Baba ya matsa da zancen auren nata.
Tabbas Maryam ta shiga ƙunci, ta ji baƙinciki da takaici, ta yi kuka tsakar dare ta share, wanda ta saka a ranta ba za ta sake hawaye saboda butulcin babarsu a gare ta ba, sannan ta saka a ranta ko da wasa ba za ta taɓa nuna mata ta san mummunan ƙudirinta a kanta ba, Uwani ta nuna mata so, ko da a ce ba so ba ne duka taku ne to fa tabbas ta yi ƙoƙari, don wasu ba sa iya sarrafa kansu har su danne ƙiyayyar mutum, sannan ta kasa yarda ma da cewar Uwani ba ta sonta, kawai ta fi yarda da shaiɗan ne da zugar ƙawayen banza ya sa take aikata mata haka, ko kuma ta ce ta aikata haka a baya, saboda komai da Uwani ta yi mata na hana ta zaman aure ya wuce a zuciyar Maryam, ta saka a ranta yanzu sabuwar rayuwa za ta fara yi, sai yanzu ta gane tabbas ta yi kuskure, ta kuma yi nadama.
Baya ta wuce, yanzu ta gaba ake yi, gaba ake iya gyarawa ba baya ba, don haka dole za ta yi gyara a rayuwarta, yanzu ita dai ba za ta fito ƙarara ta nunawa Uwani ta ajiye zancenta na miji goma ba uba goma ba ne, saboda shi maƙiyi ba ka ba shi ƙafar sanin abin da yake ranka, saboda kar ya canza taku ya shigo maka ta bayan gida.
A wannan daren Maryam ta ɗaukarwa kanta wani alwashi, ta ƙudure a ranta tabbas sai ta ba wa Uwani kunya, sai ta rusa mata burikanta, kuma ta hanya ɗaya hakan zai tabbata shi ne ta ɗaura ɗamarar jure zaman aure, ta saka a ranta za ta yi aure na mutu-ka-raba, idan ta gama idda ta yi aure ko wa ta aura, kuma ko wace matsala ta tarar a gidan auren, za ta yi haƙuri da ita, za ta zauna ta jure duk wani ƙalubale, kawai saboda mafarkin Uwani ya zama ƙarya.
Duk da tana kallon abun da kamar wuya gurguwa da auren nesa, saboda ta riga ta ginu a kan kalaman Uwani na ƙanzon kurege, ta san ba abu ba ne mai sauƙi a ce a lokaci a ɗaya ta sauka daga kan wannan hanyar da ta yi nisan tafiya a kanta, wannan ƙudurin da ta ɗauka daidai yake da mayar da kanta ƙasƙantacciya, a yanayin halittarta dama can ba ta da haƙuri, to ta ya za ta koyi wannan haƙurin ta dinga jure halin mijin da za ta aura ko yaya yake? Wannan shi ne babban ƙalubalen da take ganin za ta fuskanta, amma ta saka a ranta za ta jure ta kuma haɗa da addu'ar Allah Ya tallafe ta Ya zama gatanta.
Duk wata jarumta da dauriya Maryam ta yi, wajen nunawa Uwani ba ta gano komai na shirinta a kanta ba, ita kuwa Uwani da ba ta san wainar da Maryam take toyawa a zuciyarta ba sai ta ci gaba da biya mata karatunta, wanda sai yanzu ne Maryam ta ƙara gasgata lallai ita doluwa ce a baya ta yi wasa da damarta.
Ba ta ma gama tsinkewa da lamarin ba sai ranar da Murja ta yo yaji, saboda mijinta zai ƙara aure, ta ce ita wallahi sai dai ya sake ta, tun kafin Uwani ta ce wani abu a kai Maryam ta yi farat ta ce"Lallai wannan miji naki akwai ɗan banza! Duk zamanku nai ƙara aure ba sai yanzu? Wallahi kar ki yarda, da ki zauna da kishiya gara ki yi zaman gida, ai miji goma ba uba goma ba ne".
Uwani ta yi wuƙi-wuƙi ta ce"Amma Murja wa za ki barwa ƴaƴanki?"
Maryam ta ce"Ƴaƴa kuma ai dama tarbiyyarsu a hannun Allah take, ta bar masa su can su ƙarata ya riƙe su, ta nemi wanda ya fishi ta aura, ai wallahi wanda ya rasa Anti Murja shi ya yi asara, kalle ta fa sankaɗaziyya da ita, ƙila ma ta samu wani saurayin ya yi wuf da ita".
Murja ta yi dariya ta ce"Kai Maryam, ni kuwa wani saurayi ne zai kwashe ni? Kina kallon yadda wahala ta fara mokaÉ—ar da ni?"
Maryam ta gyara zama har da kamo hannun Murja ta ce"Wallahi Anti Murja ni nan na yi miki alƙawarin sai na samo miki miji na gagari ko ba saurayi ba, ke dai ki yi ƙoƙari ya sake ki kawai, ina haihuwa na tsige yaron ko yarinyar mu fara falla zawarci, yasin sai na wayar da ke, idan kika fantama a gari sai an taro ki, wai wa ya ga Anti Murja a gaban motar wani Alhajin!".
Ta kwashe da dariya tana kallon yadda fuskar Uwani ta nuna rashin jin daɗi, hakan kuwa ya ƙara raunana zuciyarta tabbas wata kishiyar uwar ba uwa ba ce, kuma ba za ta zama uwar wani ba har abada.
Sam ba a ga miciji a zaman nasu, duk yadda Hansatu ta so su sasanta Uwani ta ƙi ba ta dama, masifar yau da ban ta gobe da ban, a haka har aka haifi Maryam, sai kuma Allah Ya jarabci Uwani da son Maryam, idan ta rarrafo ta fito waje haka za ta ɗauke ta, sai ta ga fitowar Hansatu sannan ta ajiye ta ta shige ɗaki, to da Maryam ta girma take shiga ɗakin Uwani sai suka ja ta a jiki sosai, yaran suka haɗe kansu kamar ba ƴaƴan kishiyoyi ba, shekarar Maryam bakwai a duniya mahaifiyarta ta rasu, wajen haihuwa ta biyu, dama tun farkon cikin ya zo da matsala, kuma Allah Ya yi cikin ma abokin tafiya ne, ba ta haihu ba ta rasu, kuma dama tun da ta fara naƙuda aka tabbatar ɗan ya mutu a cikinta.
Kowa ya ji tausayin Æ´ar marainiyar nan Maryam, mutane sun yi mamakin yadda Uwani ta saka ta a jikinta ta rungume tsam, ta hana dangin babarta tafiya da ita, dama shi ma Baba ya hana, saboda ya san kishin Uwani da uwar kawai take yi tana son Æ´ar, haka aka bar mata Maryam, ana ta yabonta a gari, ita kuwa ta haÉ—e ta da Æ´aÆ´anta aka ci gaba da yaruwa.
Sai dai me? Mayam ita ce ƙarama a kan ƴaƴan Uwani Mardiyya da Murja, amma samari ita suke hari tun tana ƙwailarta, ita a tunaninta Maryam za ta yo ƙashin baƙin jini irin na babarta, sai ga shi ta ga saɓanin hakan, nan hassada ta fara shiga zuciyarta sannu-sannu, ta fara jin haushin Maryam ɗin, su kuwa su Mardiyya ba su damu ba, don sun ɗauki Maryam ƙanwarsu kamar uwa ɗaya suke, sai Uwani ta dinga nuna musu suna cikin matsala sanadin haka, a cewarta babarta ce kafin ta rasu take yi mata maganin farinjini, su dai ba su saka a ka ba.
Da farko sai ta samu Baba kamar abun arziƙi take nuna masa illar wannan farin jinin na Maryam, ta ce tana da ƙuruciya mazan za su iya amfani da wannan damar su hillace ta, saboda haka a samu wani Malamin wanda zai iya dakatar da maza daga kanta zuwa sanda za ta yi hankali ta isa aure, Baba ya nuna sam bai yarda ba, duk da shi ma abun yana ba shi tsoro, musamman da ya kasance ita ta fi ta zakka da sauran yaran gidan, ita ba ta jin magana sosau, ga yawon bin gidajen ƙawaye, wani feleƙe da rawar kai da son girma ga kwalliya kamar babbar budurwa, Baba ya ce ko maza dubu ne za su zo babu wani dakatarwar Malami da ake buƙata, tun da dai ba zance ta fara yi a ɓoye ba, to a barwa Allah komai, kuma ba yanzu zai yi mata aure ba ai, sai ta gama sakandari, haka Uwani ta haƙura ta bar zancen.
Amma ta kasa haƙura, sai da ƙawarta ta zuga ta ta karɓo rubutun farinjini take bawa ƴaƴanta ba tare da sanin Maryam ba, a haka dai har suka samu mijin, a rana ɗaya aka haɗa na Mardiyya da Murja, dama daga su sai Maryam sannan ƙaramar ƴarta Fatima, wanda tsirarsu kaɗan ne da Maryam, don bai kai shekara ba.
To ita ma Maryam ɗin da yake ba ta jin magana, sam babu auren a gabanta, duk wanda zancen aure ne ya kawo shi ba ta fiya sauraron shi ba, tun ba a farga ba har aka gane, Uwani ta fara farinciki tana tunanin ƙila ita ma ƙaddararsu ɗaya da mahaifiyarta.
A hankali shaiɗan ya tunzurata, take tuna auren da ta kira da na cin amanarta da aka yi tsakanin ƙawarta da mijinta, ta ji a ranta lokaci ya zo da ya kamata ta ɗauki fansa a kan Maryam, ta yi ta tunanin abin da za ta yi mata, kafin ta yanke shawarar hana ta zaman aure, ba ta yin shirya kuma ba ta so ta yi a kan Maryam, sannan idan ta yi mata cutarwa ta ƙiri-ƙiri mutane za su gane da wuri, a yi mata terere, ta ruguje yardar da aka yi mata akan Maryam, shiyasa ta ga gara ta yi mata kisan mummuƙe, ta so a ce ta ƙi aure kamar babarta, yadda za ta fake da dama gado ta yi, sai ga shi ta tsayar da Nazifi, don bayan auren ƙanwarta Fatima sai Baba ya matsa da zancen auren nata.
Tabbas Maryam ta shiga ƙunci, ta ji baƙinciki da takaici, ta yi kuka tsakar dare ta share, wanda ta saka a ranta ba za ta sake hawaye saboda butulcin babarsu a gare ta ba, sannan ta saka a ranta ko da wasa ba za ta taɓa nuna mata ta san mummunan ƙudirinta a kanta ba, Uwani ta nuna mata so, ko da a ce ba so ba ne duka taku ne to fa tabbas ta yi ƙoƙari, don wasu ba sa iya sarrafa kansu har su danne ƙiyayyar mutum, sannan ta kasa yarda ma da cewar Uwani ba ta sonta, kawai ta fi yarda da shaiɗan ne da zugar ƙawayen banza ya sa take aikata mata haka, ko kuma ta ce ta aikata haka a baya, saboda komai da Uwani ta yi mata na hana ta zaman aure ya wuce a zuciyar Maryam, ta saka a ranta yanzu sabuwar rayuwa za ta fara yi, sai yanzu ta gane tabbas ta yi kuskure, ta kuma yi nadama.
Baya ta wuce, yanzu ta gaba ake yi, gaba ake iya gyarawa ba baya ba, don haka dole za ta yi gyara a rayuwarta, yanzu ita dai ba za ta fito ƙarara ta nunawa Uwani ta ajiye zancenta na miji goma ba uba goma ba ne, saboda shi maƙiyi ba ka ba shi ƙafar sanin abin da yake ranka, saboda kar ya canza taku ya shigo maka ta bayan gida.
A wannan daren Maryam ta ɗaukarwa kanta wani alwashi, ta ƙudure a ranta tabbas sai ta ba wa Uwani kunya, sai ta rusa mata burikanta, kuma ta hanya ɗaya hakan zai tabbata shi ne ta ɗaura ɗamarar jure zaman aure, ta saka a ranta za ta yi aure na mutu-ka-raba, idan ta gama idda ta yi aure ko wa ta aura, kuma ko wace matsala ta tarar a gidan auren, za ta yi haƙuri da ita, za ta zauna ta jure duk wani ƙalubale, kawai saboda mafarkin Uwani ya zama ƙarya.
Duk da tana kallon abun da kamar wuya gurguwa da auren nesa, saboda ta riga ta ginu a kan kalaman Uwani na ƙanzon kurege, ta san ba abu ba ne mai sauƙi a ce a lokaci a ɗaya ta sauka daga kan wannan hanyar da ta yi nisan tafiya a kanta, wannan ƙudurin da ta ɗauka daidai yake da mayar da kanta ƙasƙantacciya, a yanayin halittarta dama can ba ta da haƙuri, to ta ya za ta koyi wannan haƙurin ta dinga jure halin mijin da za ta aura ko yaya yake? Wannan shi ne babban ƙalubalen da take ganin za ta fuskanta, amma ta saka a ranta za ta jure ta kuma haɗa da addu'ar Allah Ya tallafe ta Ya zama gatanta.
Duk wata jarumta da dauriya Maryam ta yi, wajen nunawa Uwani ba ta gano komai na shirinta a kanta ba, ita kuwa Uwani da ba ta san wainar da Maryam take toyawa a zuciyarta ba sai ta ci gaba da biya mata karatunta, wanda sai yanzu ne Maryam ta ƙara gasgata lallai ita doluwa ce a baya ta yi wasa da damarta.
Ba ta ma gama tsinkewa da lamarin ba sai ranar da Murja ta yo yaji, saboda mijinta zai ƙara aure, ta ce ita wallahi sai dai ya sake ta, tun kafin Uwani ta ce wani abu a kai Maryam ta yi farat ta ce"Lallai wannan miji naki akwai ɗan banza! Duk zamanku nai ƙara aure ba sai yanzu? Wallahi kar ki yarda, da ki zauna da kishiya gara ki yi zaman gida, ai miji goma ba uba goma ba ne".
Uwani ta yi wuƙi-wuƙi ta ce"Amma Murja wa za ki barwa ƴaƴanki?"
Maryam ta ce"Ƴaƴa kuma ai dama tarbiyyarsu a hannun Allah take, ta bar masa su can su ƙarata ya riƙe su, ta nemi wanda ya fishi ta aura, ai wallahi wanda ya rasa Anti Murja shi ya yi asara, kalle ta fa sankaɗaziyya da ita, ƙila ma ta samu wani saurayin ya yi wuf da ita".
Murja ta yi dariya ta ce"Kai Maryam, ni kuwa wani saurayi ne zai kwashe ni? Kina kallon yadda wahala ta fara mokaÉ—ar da ni?"
Maryam ta gyara zama har da kamo hannun Murja ta ce"Wallahi Anti Murja ni nan na yi miki alƙawarin sai na samo miki miji na gagari ko ba saurayi ba, ke dai ki yi ƙoƙari ya sake ki kawai, ina haihuwa na tsige yaron ko yarinyar mu fara falla zawarci, yasin sai na wayar da ke, idan kika fantama a gari sai an taro ki, wai wa ya ga Anti Murja a gaban motar wani Alhajin!".
Ta kwashe da dariya tana kallon yadda fuskar Uwani ta nuna rashin jin daɗi, hakan kuwa ya ƙara raunana zuciyarta tabbas wata kishiyar uwar ba uwa ba ce, kuma ba za ta zama uwar wani ba har abada.