Sashe 15
Miji Goma Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Uwani ta ce"Ƙalau, dama a kan wannan yaron ne, na ce ya za a yi da shi? Za ki karɓa ne ko kuwa biya za ku dinga yi tana shayar muku da shi?"
Ta ce"A haba dai ga uwarsa a raye ai bai kamata a raba shi da nonon uwa ba, sai a dinga ba ta wani abun".
Ta ce"To nawa za ku na badawa? Kin ga bayan shayarwa ma a kwai omo, sabulu, famfas kafin kuma ya fara cin abinci".
Maryam da duk matar ta ba ta tausayi ta ce"To babarmu ai ba sai an wani tsadance ba, ko me suka kawo Allah Ya saka masa albarka, ni ma fa É—ana ne".
Uwani ta galla mata harara, ita dai ta yi musu sallama ta tafi, ta ce gobe za ta dawo idan suka yi magana da Hamza.
Tun daga nan duk sati biyu sai babar Hamza ta zo ta gansu, wataran kuma ta tiso shi a gaba su zo tare, su ba su kuɗin shayarwa. Babu laifi Maryam ta samu kulawa sosai a wajen Uwani, yanzu hankalinta a kwance yake tana ra rainon ɗanta da yake ta ƙara girma da wayo. Al'amin yana da wata biyar ta ce za ta fara bussiness da kuɗin da ta siyar da kayan ɗakinta, Uwani ta so daƙile ta, ta nuna mata wannan fa duk cake ne ba samun ciniki ake ba, har gara ma siyar da abincin, ita kuma Maryam ta ga ya za a yi ta sana'ar abinci da ƙaramin ɗa, to da yake Uwanin ta san idan Maryam ɗin ta coge ba a iya ture ta sai ta rabu da ita, ita take zuwa kasuwa da kanta tana yo sarin abubuwa iri-iri, ta tallata a maƙota da kuma status kuma Alhamdulillah Allah sai Ya sakawa abun albarka, Uwani tana kallo take ƙirga ribarta tana adanawa.
Da ta yaye Al'amin sai ta daina zuwa kasuwar da shi, ta fara ɗaukar wanka don shirin fara zawarci, ai kuwa zawarawan suka fara layi, tana ta cafke musu ƴan canji,domin ta koyi roƙo sosai, idan ma kai faƙiri ne ko marowaci soyayyarku da Maryam ba ta taɓa yin ƙarko, bani-bani ne zai kore ka, idan gari ya waye dare ya yi ba su ci kaza ko balangu ba ita da Uwani to sai dai idan ita ce ba ta so ba, ma'ana idan ba ta bawa kowa damar zuwa ba, amma muddin ka ce ga ka nan tafe to za ta lissafo maka abin da za ka taho da shi, ai kuwa har wata ƙiba ta fara yi, ta yi kyau abunta.
Ba ta tsayar da mijin ba, tana ta tantancewa dai, yayin da ƴan'uwanta ƴaƴan Uwani suke yawan yi mata nasiha kan auren shi ne rufin asirinta, idan a gaban Uwani ne kuwa nan za ta hayayyaƙo tana cewa su ba su san ƙaddara ba? Ai ita Maryam ƙaddararta kenan, shi ma Baba ya fara matsa mata, don haka ta tsayar da wani Nasuru, a kasuwa suka haɗu, ya faɗa mata ya taɓa yin aure ƴaƴansa biyu suka rabu da matar, Nasuru ba shi da rowa, sosai yake sakar mata kuɗi, kuma ba shi da wata makusa a halitta, ta ji tana son shi za ta iya auren shi, don haka ta ba shi dama ya turo bayan ta gama shirinta.
A wannan karon wata biyu aka saka, aka ɗaura aure, aka mayar da Al'amin wajen babar Hamza ta ci gaba da kula da shi, a wannan karon Uwani ta san babu buƙatar yiwa ƴar tata wata huɗuba domin ta riga ta haddace karatunta, musamman ma a wannan zawarcin da ta yi ta ƙara samun gogewa ta rayuwa, don haka hankalinta kwance yake, ta san yadda ta tafi haka za ta dawo.
An kai amarya lafiya, zamansu da Nasuru lafiya ƙalau babu wata matsala daga farko, haka kuma shi yana son haihuwa ba kamar Hamza ba, don da ta samu ciki ya nuna mata kulawa sosai, bai taɓa nuna ƙosawa da yanayin laulayinta ba. Yaran shi suna zuwa gidan, wani lokacin ma har su kwana biyu idan sun zo ranar Juma'a sai ya mayar da su ranar Asabar, a yadda ta lura da alamunsa yana son yaran su zauna a wajenta, ita ma kuma ba ta ɗauki hakan a komai ba, tun da ba ƙananu ba ne sosai ballantana ta ce za ta ci kashinsu da fitsari, babban shekararaa tara, sai ƙanwarsa shekararta baƙwai, to da yake komai na gidan aurenta a tafin hannun Uwani yake ita ce ta nuna mata sam kar ta sake ta riƙe masa ƴaƴa, ɗan kishiya ruƙon mai haƙuri ne, ta zuga ta a kan idan ta haihu tana kallo zai yi ta fifita yaran a kan wanda za ta haifa, saboda an fi marmarin ɗan fari, haka dai ta harhaɗa mata raunana hujjoji marasa tushe bare makama, sai ta hau kai ta zauna ta fara baya-baya da yaran.
Nasuru ɗan kasuwa ne, dole ba zai rabu da mata a waya ba, musamman yanzu da kasuwancin ya koma na online, sannan da daddare ne yake samun damar zama ya nutsu ya duba saƙƙonnin da bai duba ba, sannan ya yi ta saka hotunan kaya a groups ɗin shi, ita kuma Maryam wannan karkata da yake yi a kan waya yana mugun ba ta haushi, ko kuma ta ga wata ta kira shi suna magana, duk da ga shi a zahiri tana ji zancen kaya ake yi, amma sai ta yi ta yi masa tijara tana cewa ƙarya yake yi alaye yake yi mata, kurman baƙi ne kawai suke yi saboda a gabanta ne, kuma da fari ba haka take yi ba, ta yarda da shi sosai, nan ma Uwani ce ta zuga ta ta ɗora ta a keken ɓera ta ce duk ƙarya ce, dama ƴan kasuwa ba a isa a raba su da mata ba, ga su da watsewa da masu abinci, har da cewa Allah Ya sa ma bai ɗebo mata alaƙaƙai ba.
Tun daga ranar da Maryam ta ji haka shikenan ta kasa zaune ta kasa tsaye a gidan aure, ta matsewa Nasuru lamba take tuhumarsa babu dare babu rana, dayake yana sonta haka yake ba ta hujjojin kare kansa, daga ƙarshe ma ta ce munafurci ne yasa yake saka password a waya dole sai ya cire, kuma ta cire ɗin saboda a zauna lafiya, don haka ta samu damar bincikar wayarsa kullum, tsakar dare za ta tashi ta ɗauki wayar ta fice falo ta yi ta bincikenta, yana kallonta amma bai damu ba tun da ya san babu komai ba rashin gaskiya da za ta gani.
Ana haka ne ya sayi wata waya sakan a wajen abokinsa, ya ɗora wani daga cikin layinsa a kai, da yamma ya karɓi wayar bai ma duba ya ga mene ne a ciki ba, ashe da fina-finan batsa kala-kala, ta ɗauki wayar ta duba ta gani, shi ne ta tashe shi tsakar dare suka yi tijara har ya sake ta, tana ganin ba komai ba ne don aurenta ya mutu, sai kuma ta dawo a ranar ta san matsayinta da gadar kwalin da Uwani ta sakawa rayuwarta ta hau kai ta kwanta a rashin sani.
Wannan shi ne abin da ya faru a baya, yanzu za a ci gaba da labari.
08028966015
[2/11, 4:53 PM] Sadiya abdulrazak: *MIJI GOMA...*
_(BA UBA GOMA BA NE)_
*SADIYA ABDULRAZAƘ*
*Ƴan magana dai sun ce "Miji goma ba uba goma ba ne" Shin kun yarda? Sannan mene ne hikimar wannan maganar? Kun yarda da ingancinta? Ta kai a kafa hujja da ita a ƙi zaman aure?*
Marubuciyar
ZUCIYAR MACE
WUTAR ƘAIƘAYI
DA WALAKIN...
WANI AUREN
IYA RUWA
MATAR SHIGE. da sauransu
*FIRST CLASS WRITERS*
https://chat.whatsapp.com/G08KLEmlF3gJ3X4npkfIee
PAGE 11
Wunin ranar Maryam ba ta bar zuciyarta ta huta ba, tunani kawai take yi na irin zuciyar wasu mutanen, ta ɗauki Uwani tamkar mahaifiyarta, tana yi mata kallon gatanta, kusan ma za ta iya cewa ta fi sonta fiye da mahaifinta, saboda yadda take riƙe ta da amana, tun tana yarinya take kula da ita bayan rasuwar mahaifiyarta, ba ta taɓa ganin wani abu na nuna bambanci a tsakaninta da ƴaƴan da ta haifa ba, kuma da yake ita ma Maryam tana da sakin jiki da mutane da surutu sai ya zamana ba ta rakuɓewa kamar na ƴaƴan da babu uwarsu a gida, sabgarta kawai take kamar Uwani ce ta haife ta.
Ita Hansatu mahaifiyar Maryam ƙawar Uwani ce tun ta ƙuruciya, kowa ya san amincinsu komai tare suke yi, ƙawance irin na da mai cike da tsafta da yarda da juna, musamman da suka kasance maƙota, ga gida ga gida, Uwani ta samu miji da wuri ta yi aure, saɓanin Hansatu da ta samu jinkirin aure, har ana cewa aljani ne ya aure ta sai da ta girma Uwani ta yi haihuwa uku sannan ta samu miji, shi ma abokin mijin Uwanin ne, wanda bai yi auren wuri ba shi ma abun ya damu iyayensa, kawai sai mijin Uwani ya yi wani tunani, ya ce tun da ƙaddararsu ta zo ɗaya da Hansatu kawai a haɗa su a gani ko za a dace, kamar wasa aka haɗa su suka fara soyayya, kuma sai abun ya ɗore har aka yi aure, wata biyu da auren Hansatu da Malam Habu Allah Ya yi masa rasuwa, sanadin hatsarin mota, da yake direba ne shi, yana kai kaya Legas.
Ta ce"A haba dai ga uwarsa a raye ai bai kamata a raba shi da nonon uwa ba, sai a dinga ba ta wani abun".
Ta ce"To nawa za ku na badawa? Kin ga bayan shayarwa ma a kwai omo, sabulu, famfas kafin kuma ya fara cin abinci".
Maryam da duk matar ta ba ta tausayi ta ce"To babarmu ai ba sai an wani tsadance ba, ko me suka kawo Allah Ya saka masa albarka, ni ma fa É—ana ne".
Uwani ta galla mata harara, ita dai ta yi musu sallama ta tafi, ta ce gobe za ta dawo idan suka yi magana da Hamza.
Tun daga nan duk sati biyu sai babar Hamza ta zo ta gansu, wataran kuma ta tiso shi a gaba su zo tare, su ba su kuɗin shayarwa. Babu laifi Maryam ta samu kulawa sosai a wajen Uwani, yanzu hankalinta a kwance yake tana ra rainon ɗanta da yake ta ƙara girma da wayo. Al'amin yana da wata biyar ta ce za ta fara bussiness da kuɗin da ta siyar da kayan ɗakinta, Uwani ta so daƙile ta, ta nuna mata wannan fa duk cake ne ba samun ciniki ake ba, har gara ma siyar da abincin, ita kuma Maryam ta ga ya za a yi ta sana'ar abinci da ƙaramin ɗa, to da yake Uwanin ta san idan Maryam ɗin ta coge ba a iya ture ta sai ta rabu da ita, ita take zuwa kasuwa da kanta tana yo sarin abubuwa iri-iri, ta tallata a maƙota da kuma status kuma Alhamdulillah Allah sai Ya sakawa abun albarka, Uwani tana kallo take ƙirga ribarta tana adanawa.
Da ta yaye Al'amin sai ta daina zuwa kasuwar da shi, ta fara ɗaukar wanka don shirin fara zawarci, ai kuwa zawarawan suka fara layi, tana ta cafke musu ƴan canji,domin ta koyi roƙo sosai, idan ma kai faƙiri ne ko marowaci soyayyarku da Maryam ba ta taɓa yin ƙarko, bani-bani ne zai kore ka, idan gari ya waye dare ya yi ba su ci kaza ko balangu ba ita da Uwani to sai dai idan ita ce ba ta so ba, ma'ana idan ba ta bawa kowa damar zuwa ba, amma muddin ka ce ga ka nan tafe to za ta lissafo maka abin da za ka taho da shi, ai kuwa har wata ƙiba ta fara yi, ta yi kyau abunta.
Ba ta tsayar da mijin ba, tana ta tantancewa dai, yayin da ƴan'uwanta ƴaƴan Uwani suke yawan yi mata nasiha kan auren shi ne rufin asirinta, idan a gaban Uwani ne kuwa nan za ta hayayyaƙo tana cewa su ba su san ƙaddara ba? Ai ita Maryam ƙaddararta kenan, shi ma Baba ya fara matsa mata, don haka ta tsayar da wani Nasuru, a kasuwa suka haɗu, ya faɗa mata ya taɓa yin aure ƴaƴansa biyu suka rabu da matar, Nasuru ba shi da rowa, sosai yake sakar mata kuɗi, kuma ba shi da wata makusa a halitta, ta ji tana son shi za ta iya auren shi, don haka ta ba shi dama ya turo bayan ta gama shirinta.
A wannan karon wata biyu aka saka, aka ɗaura aure, aka mayar da Al'amin wajen babar Hamza ta ci gaba da kula da shi, a wannan karon Uwani ta san babu buƙatar yiwa ƴar tata wata huɗuba domin ta riga ta haddace karatunta, musamman ma a wannan zawarcin da ta yi ta ƙara samun gogewa ta rayuwa, don haka hankalinta kwance yake, ta san yadda ta tafi haka za ta dawo.
An kai amarya lafiya, zamansu da Nasuru lafiya ƙalau babu wata matsala daga farko, haka kuma shi yana son haihuwa ba kamar Hamza ba, don da ta samu ciki ya nuna mata kulawa sosai, bai taɓa nuna ƙosawa da yanayin laulayinta ba. Yaran shi suna zuwa gidan, wani lokacin ma har su kwana biyu idan sun zo ranar Juma'a sai ya mayar da su ranar Asabar, a yadda ta lura da alamunsa yana son yaran su zauna a wajenta, ita ma kuma ba ta ɗauki hakan a komai ba, tun da ba ƙananu ba ne sosai ballantana ta ce za ta ci kashinsu da fitsari, babban shekararaa tara, sai ƙanwarsa shekararta baƙwai, to da yake komai na gidan aurenta a tafin hannun Uwani yake ita ce ta nuna mata sam kar ta sake ta riƙe masa ƴaƴa, ɗan kishiya ruƙon mai haƙuri ne, ta zuga ta a kan idan ta haihu tana kallo zai yi ta fifita yaran a kan wanda za ta haifa, saboda an fi marmarin ɗan fari, haka dai ta harhaɗa mata raunana hujjoji marasa tushe bare makama, sai ta hau kai ta zauna ta fara baya-baya da yaran.
Nasuru ɗan kasuwa ne, dole ba zai rabu da mata a waya ba, musamman yanzu da kasuwancin ya koma na online, sannan da daddare ne yake samun damar zama ya nutsu ya duba saƙƙonnin da bai duba ba, sannan ya yi ta saka hotunan kaya a groups ɗin shi, ita kuma Maryam wannan karkata da yake yi a kan waya yana mugun ba ta haushi, ko kuma ta ga wata ta kira shi suna magana, duk da ga shi a zahiri tana ji zancen kaya ake yi, amma sai ta yi ta yi masa tijara tana cewa ƙarya yake yi alaye yake yi mata, kurman baƙi ne kawai suke yi saboda a gabanta ne, kuma da fari ba haka take yi ba, ta yarda da shi sosai, nan ma Uwani ce ta zuga ta ta ɗora ta a keken ɓera ta ce duk ƙarya ce, dama ƴan kasuwa ba a isa a raba su da mata ba, ga su da watsewa da masu abinci, har da cewa Allah Ya sa ma bai ɗebo mata alaƙaƙai ba.
Tun daga ranar da Maryam ta ji haka shikenan ta kasa zaune ta kasa tsaye a gidan aure, ta matsewa Nasuru lamba take tuhumarsa babu dare babu rana, dayake yana sonta haka yake ba ta hujjojin kare kansa, daga ƙarshe ma ta ce munafurci ne yasa yake saka password a waya dole sai ya cire, kuma ta cire ɗin saboda a zauna lafiya, don haka ta samu damar bincikar wayarsa kullum, tsakar dare za ta tashi ta ɗauki wayar ta fice falo ta yi ta bincikenta, yana kallonta amma bai damu ba tun da ya san babu komai ba rashin gaskiya da za ta gani.
Ana haka ne ya sayi wata waya sakan a wajen abokinsa, ya ɗora wani daga cikin layinsa a kai, da yamma ya karɓi wayar bai ma duba ya ga mene ne a ciki ba, ashe da fina-finan batsa kala-kala, ta ɗauki wayar ta duba ta gani, shi ne ta tashe shi tsakar dare suka yi tijara har ya sake ta, tana ganin ba komai ba ne don aurenta ya mutu, sai kuma ta dawo a ranar ta san matsayinta da gadar kwalin da Uwani ta sakawa rayuwarta ta hau kai ta kwanta a rashin sani.
Wannan shi ne abin da ya faru a baya, yanzu za a ci gaba da labari.
08028966015
[2/11, 4:53 PM] Sadiya abdulrazak: *MIJI GOMA...*
_(BA UBA GOMA BA NE)_
*SADIYA ABDULRAZAƘ*
*Ƴan magana dai sun ce "Miji goma ba uba goma ba ne" Shin kun yarda? Sannan mene ne hikimar wannan maganar? Kun yarda da ingancinta? Ta kai a kafa hujja da ita a ƙi zaman aure?*
Marubuciyar
ZUCIYAR MACE
WUTAR ƘAIƘAYI
DA WALAKIN...
WANI AUREN
IYA RUWA
MATAR SHIGE. da sauransu
*FIRST CLASS WRITERS*
https://chat.whatsapp.com/G08KLEmlF3gJ3X4npkfIee
PAGE 11
Wunin ranar Maryam ba ta bar zuciyarta ta huta ba, tunani kawai take yi na irin zuciyar wasu mutanen, ta ɗauki Uwani tamkar mahaifiyarta, tana yi mata kallon gatanta, kusan ma za ta iya cewa ta fi sonta fiye da mahaifinta, saboda yadda take riƙe ta da amana, tun tana yarinya take kula da ita bayan rasuwar mahaifiyarta, ba ta taɓa ganin wani abu na nuna bambanci a tsakaninta da ƴaƴan da ta haifa ba, kuma da yake ita ma Maryam tana da sakin jiki da mutane da surutu sai ya zamana ba ta rakuɓewa kamar na ƴaƴan da babu uwarsu a gida, sabgarta kawai take kamar Uwani ce ta haife ta.
Ita Hansatu mahaifiyar Maryam ƙawar Uwani ce tun ta ƙuruciya, kowa ya san amincinsu komai tare suke yi, ƙawance irin na da mai cike da tsafta da yarda da juna, musamman da suka kasance maƙota, ga gida ga gida, Uwani ta samu miji da wuri ta yi aure, saɓanin Hansatu da ta samu jinkirin aure, har ana cewa aljani ne ya aure ta sai da ta girma Uwani ta yi haihuwa uku sannan ta samu miji, shi ma abokin mijin Uwanin ne, wanda bai yi auren wuri ba shi ma abun ya damu iyayensa, kawai sai mijin Uwani ya yi wani tunani, ya ce tun da ƙaddararsu ta zo ɗaya da Hansatu kawai a haɗa su a gani ko za a dace, kamar wasa aka haɗa su suka fara soyayya, kuma sai abun ya ɗore har aka yi aure, wata biyu da auren Hansatu da Malam Habu Allah Ya yi masa rasuwa, sanadin hatsarin mota, da yake direba ne shi, yana kai kaya Legas.