Sashe 8
Kundi Uku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Boka Tsumbur bai tanka masa ba, ya miƙe a gabansu ya saki fitsari a saman shurin da yake zaune. Sai kuma ya mayar da ganyen jikinsa ba tare ya yi tsarki ba, ya ya ɗebi kasar shurin da ta jike da fitsarin ya miƙa wa Sarki Dikko. A tsantsance Sarkin yake kallonsa, Boka Tsumbur ya zuba masa daƙwa-daƙwa idanunsa sannan ya ce.
"Ka yi imani da wannan ƙasar shurin ita ce mai rayawa kuma mai kashewa. Sannan ita za ta sa na taimaka wa duk matsalar da kake ciki, kuma sai ka yi imani da wannan shurin ya fi abin bautar da kake bautawa."
Jim Sarki Dikko ya yi, cikin sauri Waziri ya ce.
"Ya amince tabbatacan boka."
Sarki Dikko kallon Waziri ya yi, ya fakaici idon Boka Tsumbur ya matsa hannunsa alamar ya ce ya amince. Cikin muryar takaici da ganin gazawarsa Sarki Dikko ya ce.
"Mun amince."
Wata mahaukaciyar dariya Bokan ya saki sannan ya fara yi wa kansa kirari, "Sai ni bokan da har gobe babu wanda ya kai ni, sai ni Tsumbur jikan maguzawa masu abin mamaki. Sai ni waraka ga duk wanda ya raɓe ni, sai ni mai abin bautar da babu wanda ya kai ni." Sai ya waigo ya dubi Sarki Dikko ya cigaba da cewa.
"Matsalar 'ya'yanka ba daga matsalar iyalinka ba ne, wannan matsalar tana da alaƙa da kisan da ka yi wa Boka Damina. Don haka ko yanzu matanka suka tara da wani namijin za su haifi lafiyayyun yara."
"Zafin kishina ba zai bari na saki mace ta yi wani auren ba, babu wanda ya isa ya aikata wannan mummunan aikin a kan macen da na santa."
Sarki Dikko ya furta a fusace, murmushi Boka Tsumbur ya yi ya ce.
"Ƙarfin zuciyarka yana matuƙar birge ni Dikko. Sai dai ka sani daga nan har ka mutu ba za ka taɓa haihuwar lafiyayyun 'ya'ya ba."
A razane Sarki Dikko yake kallonsa, Boka Tsumbur ya cigaba da cewa.
"Sai dai waÉ—annan jariran da aka haifa maka za mu iya warkar da su."
"Ka taimaka mini Boka Tsumbur, wallahi ina cikin tashin hankali domin a yanzu babu ɗa ɗaya ƙwaƙƙwara da zan ɗaga wanda zai gaji karagata."
Boka Tsumbur ya ɗebi ƙasar shurin ya watsa a wutar da ke ci a gabansa, sannan ya ce.
"Za su warke matuƙar ka lamunce da sharaɗin da za mu kafa maka."
Cike da rashin dogon nazari Sarki GiÉ—aÉ—o ya ce.
"Kowanne irin sharaÉ—i ne a shirye nake da na tunkare shi. Na amince da sharaÉ—inka Boka Tsumbur."
"An haifa wa Sarki Gambo tagwayen mata, adaidai gaɓar da iyalinka ta haife maka tagwayen yaranka mace da namiji. Macen da aka haifa maka makauniya ce, shi kuma namijin ƙafafuwa da hannuwansa a shanye suke."
Sarki Dikko ya sunkuyar da kai ƙasa cikin takaici, boka Tsumbur ya cigaba da cigaba da cewa.
"Don haka za mu musanya lalurar 'ya'yanka zuwa kan 'yan tagwayen da Sarki Gambo ya haifa."
"Amma me ya sa sai Sarki Gambo? Boka Tsumbur ko ka san ni da Sarki Gambo kamar wuta da ruwa muke, idan har sarki Gambo yana ƙaunata. Ko kuma idan ina ƙaunar Sarki Gambo to zan ƙaunaci mutuwata, ta yaya 'ya'yana za su yi amfani da surar 'ya'yan maƙiyina?"
Boka Tsumbur ya yi saurin katse Sarki Dikko da cewar.
"Saboda ba ka san jinin wace ce a jikin 'ya'yan Gambo ba, da ace ka san wace ce mahaifiyar yaran nan. Na tabbata da ka zabarce ta cikin rayuwarka tun kafin mutuwarta, kamar yadda wani ƙudurin Sarki Gambo ya sa shi aurenta ba don yana sonta ba."
Ajiyar zuciya Waziri ya sauke, ya yi ƙasa da murya yana yi wa Sarki Giɗaɗo raɗa.
"Ranka shi daɗe ka ajiye batun gabarku a gefe, ka fuskanci abin da yake gabanka. Wannan wata dama ce ta idan ta kuɓuce ba lallai mu sake samun ta ba, kada ka manta ranka shi daɗe. A ƙalla yau shekara biyar kenan ina bibiyar Boka Tsumbur a kan ya ba mu damar ganinsa, amma sai yau ya ba mu wannan damar." Shiru Sarki Giɗaɗo ya yi yana nazari, cikin zafin nama ya ce.
"Mun amince Boka Tsumbur."
Dariya Bokan ya saki marar daɗin sauraro, sai ya saka hannunsa a cikin wutar gabansa. Ya ɗauko wani allon farin ƙarfe, ya soka a jikin shirun sannan ya fara biya ɗalasiman tsafi, yana kiran sunayen manyan aljanun da suke yi masa aiki. Wani ruwa mai kamar jini da ke tafasa ya ɗiba ya watsa a kan allon, nan take hoton jariran Sarki Gambo da ke kwance Unguwar zoma tana yanke musu cibi suka bayyana. Daga gefe kuma jariran Sarki Dikko ne kwance a saman gadon mahaifiiyarsu, ruwan ya sake watsa musu lokaci ɗaya jarirai huɗun suka fashe da kuka jikinsu yana wata irin karkarwa. Har sai da Sarki Dikko ya tsorata da ganin abin da yake faruwa da su, Boka Tsumbur ya ɗago ya dube su ya ce.
"A yanzu haka duk irin tawaya da nakasar da ke jikin jariranka, sun koma yaran Sarki Gambo. Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba."
Da sauri Sarki Dikko ya dube shi yana shirin yin magana suka ji tsibirin ya yi wata irin tsawa mai razanarwa.
*Ummmou Aslam Bint Adam*🌚
07062062624
[24/11, 15:59] Ameerah Adam: *KUNDI UKU*
©AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
GargaÉ—i: Ban amince a sarrafa mini littafi ta kowacce siga, ba tare da izinina ba. Yin hakan yana iya kai wa ga matakin Hukuma, don haka a kiyaye.
Tsokaci: Daga Masarautu, Sarakuna da sunayen yanki duka ƙirƙira ne. Idan ya yi daidai da labarin wani/wata arashi ne.
SHAFI NA SHIDA
Masarautar Kajjura
A haukace Sarki Gambo ya ƙarasa cikin zafin rai, ya maƙure wuyan Fulani Sadiya har sai da ta fara kakari. Murya a kausashe ya ce.
"Saboda me za ku kashe mana iyali? Saboda me za ku raba mu da uwar 'ya'yanmu?"
Fulani Sadiya ta tattara ƙarfinta ta fisge hannunta da ƙyar, sannan ta gyara zaman rigarta ta ce.
"Saboda har yanzu ba ka gama karantata ba, saboda har yanzu ba ka tantance maƙiyin ɓoye da na zahiri ba." Ta yi jim tana shafa wuyanta da har lokacin yake yi mata raɗaɗi sannan ta cigaba da cewa.
"Ranka shi daɗe! Kana tsammanin zan kashe Fulani Khadija sannan na bar 'ya'yan da ta haifa? Me ya sa ban haɗa har su na hallaka ba? Mai martaba! Yana da kyau ka nutsu domin ka san wanɗanda suke zagaye da kai. Amma Allah Ya taimake ka, ka san ba zan taɓa cutar da kai ba."
Fulani Sadiya tana zuwa nan sai ta fara zubar da hawaye, jikinsa ne ya yi sanyi. Ya riƙo ta a jikinsa, sai Fulani Sadiya ta sake fashewa da kuka ta ce.
"Na yi mamaki da har kake tsammanin zan iya cutar da Fulani Khadija, a duk tsawon shekarun da muka ɗauka. Ban taɓa tsammanin za ka yi mini mummunar shaida ba, ko don ban haihu ba kake yi mini haka oho?"
Ta sake fashewa da kukan kissa, nan take tausayinta ya kama shi. Cikin tattausan lafazi ya ce.
"Ku yi haƙuri Fulani, mutuwar Fulani Khadija ta gigita mu."
"Ina yi maka ta'aziyya ranka shi daÉ—e."
Fulani Sadiya ta sake furtawa tana kwantar da kai.
A gaggauce Sarki Gambo ya fita daga É—akinsa, ya koma rumfar ya zauna. Abin duniya goma da ashirin ya haÉ—e masa, dafe kansa ya yi da hannuwa biyu yana nazarin al'amuran baya da suka shiga tsakaninsa da Fulani Khadija.
Unguwar Zoma
Lami tana zaune tana yankewa tagwayen Sarki Gambo cibi, ta ga jikinsu ya fara wata irin karkarwa. A É—an tsorace ta ajiye su tana kallo, tana cikin haka Jakadiya ta shiga É—akin tana wurga mata tambaya.
"Me ya faru Lami? Me ya samu jariran nan? Lami kada ki jefa mu a masifa mu shiga uku, kin ga dai uwarsu a hannunmu ta mutu. Yanzu idan wani abin ya samu yaran nan me za mu cewa Mai martaba?"
Jikin Unguwar zoma nan take ya cigaba da karkarwa, bakinta yana rawa ta ce.
"Wallahi ban san me ya faru da su ba Jakadiya, ki yadda da ni haka na ga suna karkarwa ba tare da komai ba."
Unguwar zoma ba ta gama rufe baki ba, suka ga ɗaya daga cikin jariran ta fara jijjiga kai. Nan take wani ruwa mai kamar na ɗaurayar nama ya fara zuba daga idonta a madadin hawaye. Ɗayar kuma ƙafafuwnata suka shiga karkarwa, irin ruwan da ke fita daga idanun ɗayar shi ma ya fara tsattsafowa daga jikin ƙafafuwanta.
Jakadiya da Unguwar zoma kallon juna suka yi cike da tsoro, Jakadiya ta yi ƙasa da murya ta ce.
"Lami kina ganin abin da idanuna suke gani?"
"Ina gani Jakadiya, magana ta Allah na jima ban ga haihuwar da ta zo mini da al'ajabi kamar wannan ba."
Lami za ta yi magana, suka ji muryar Shamaki daga dokin ƙofa. A daidai lokacin uwar Bayi ta shiga ɗakin, duk suka yi carko-carko. Daɗin da suka ji a lokacin jariran sun dakata da kukan da suke yi, kuma ruwa da karkarwar da suke yi duk sun daina. A ɗan ɗarara Lami ta ɗauke ta ta cigaba gaba da gyara su, sannan Jakadiya ta ɗauke su ta fita da su. Dangin Fulani Khadija ne suka yi wa gidan sarautar tsinke, mahaifiyarta ban da kuka babu abin da take yi. Koda aka nuna musu jariran ba su bi ta kansu ba, suna shiga da suka ga irin kisan da aka yi mata duk sai jikinsu ya sake yin sanyi. Mahaifiyarta ta dubi mahaifin Fulani ta ce.
"Malam dama sai da na ce maka ba na son auren nan na Hadiza a gidan sarauta amma ka ƙi ka ji, dubi yadda makircin masarautar nan ya sa aka hallaka mana ita."
"Fatima! Ke musulma ce, kuma kin sani da Khadija ta yi aure a nan da mu aurar da ita a wani wurin ba nan ba. Duk abin da Allah Ya ƙaddara a cikin rayuwarta sai ya faru, abin da za ki yi mata a yanzu addu'a ce. Idan har 'yata Khadija ba ta da haƙƙi a wannan kisan da aka yi mata, na tabbata sai Ubangiji Ya yi mata sakayya."
Mahaifin Fulani Kgadija ya furta yana ɓoye hawayen da ke gangarowa daga idonsa.
Fulani Sadiya
"Ka yi imani da wannan ƙasar shurin ita ce mai rayawa kuma mai kashewa. Sannan ita za ta sa na taimaka wa duk matsalar da kake ciki, kuma sai ka yi imani da wannan shurin ya fi abin bautar da kake bautawa."
Jim Sarki Dikko ya yi, cikin sauri Waziri ya ce.
"Ya amince tabbatacan boka."
Sarki Dikko kallon Waziri ya yi, ya fakaici idon Boka Tsumbur ya matsa hannunsa alamar ya ce ya amince. Cikin muryar takaici da ganin gazawarsa Sarki Dikko ya ce.
"Mun amince."
Wata mahaukaciyar dariya Bokan ya saki sannan ya fara yi wa kansa kirari, "Sai ni bokan da har gobe babu wanda ya kai ni, sai ni Tsumbur jikan maguzawa masu abin mamaki. Sai ni waraka ga duk wanda ya raɓe ni, sai ni mai abin bautar da babu wanda ya kai ni." Sai ya waigo ya dubi Sarki Dikko ya cigaba da cewa.
"Matsalar 'ya'yanka ba daga matsalar iyalinka ba ne, wannan matsalar tana da alaƙa da kisan da ka yi wa Boka Damina. Don haka ko yanzu matanka suka tara da wani namijin za su haifi lafiyayyun yara."
"Zafin kishina ba zai bari na saki mace ta yi wani auren ba, babu wanda ya isa ya aikata wannan mummunan aikin a kan macen da na santa."
Sarki Dikko ya furta a fusace, murmushi Boka Tsumbur ya yi ya ce.
"Ƙarfin zuciyarka yana matuƙar birge ni Dikko. Sai dai ka sani daga nan har ka mutu ba za ka taɓa haihuwar lafiyayyun 'ya'ya ba."
A razane Sarki Dikko yake kallonsa, Boka Tsumbur ya cigaba da cewa.
"Sai dai waÉ—annan jariran da aka haifa maka za mu iya warkar da su."
"Ka taimaka mini Boka Tsumbur, wallahi ina cikin tashin hankali domin a yanzu babu ɗa ɗaya ƙwaƙƙwara da zan ɗaga wanda zai gaji karagata."
Boka Tsumbur ya ɗebi ƙasar shurin ya watsa a wutar da ke ci a gabansa, sannan ya ce.
"Za su warke matuƙar ka lamunce da sharaɗin da za mu kafa maka."
Cike da rashin dogon nazari Sarki GiÉ—aÉ—o ya ce.
"Kowanne irin sharaÉ—i ne a shirye nake da na tunkare shi. Na amince da sharaÉ—inka Boka Tsumbur."
"An haifa wa Sarki Gambo tagwayen mata, adaidai gaɓar da iyalinka ta haife maka tagwayen yaranka mace da namiji. Macen da aka haifa maka makauniya ce, shi kuma namijin ƙafafuwa da hannuwansa a shanye suke."
Sarki Dikko ya sunkuyar da kai ƙasa cikin takaici, boka Tsumbur ya cigaba da cigaba da cewa.
"Don haka za mu musanya lalurar 'ya'yanka zuwa kan 'yan tagwayen da Sarki Gambo ya haifa."
"Amma me ya sa sai Sarki Gambo? Boka Tsumbur ko ka san ni da Sarki Gambo kamar wuta da ruwa muke, idan har sarki Gambo yana ƙaunata. Ko kuma idan ina ƙaunar Sarki Gambo to zan ƙaunaci mutuwata, ta yaya 'ya'yana za su yi amfani da surar 'ya'yan maƙiyina?"
Boka Tsumbur ya yi saurin katse Sarki Dikko da cewar.
"Saboda ba ka san jinin wace ce a jikin 'ya'yan Gambo ba, da ace ka san wace ce mahaifiyar yaran nan. Na tabbata da ka zabarce ta cikin rayuwarka tun kafin mutuwarta, kamar yadda wani ƙudurin Sarki Gambo ya sa shi aurenta ba don yana sonta ba."
Ajiyar zuciya Waziri ya sauke, ya yi ƙasa da murya yana yi wa Sarki Giɗaɗo raɗa.
"Ranka shi daɗe ka ajiye batun gabarku a gefe, ka fuskanci abin da yake gabanka. Wannan wata dama ce ta idan ta kuɓuce ba lallai mu sake samun ta ba, kada ka manta ranka shi daɗe. A ƙalla yau shekara biyar kenan ina bibiyar Boka Tsumbur a kan ya ba mu damar ganinsa, amma sai yau ya ba mu wannan damar." Shiru Sarki Giɗaɗo ya yi yana nazari, cikin zafin nama ya ce.
"Mun amince Boka Tsumbur."
Dariya Bokan ya saki marar daɗin sauraro, sai ya saka hannunsa a cikin wutar gabansa. Ya ɗauko wani allon farin ƙarfe, ya soka a jikin shirun sannan ya fara biya ɗalasiman tsafi, yana kiran sunayen manyan aljanun da suke yi masa aiki. Wani ruwa mai kamar jini da ke tafasa ya ɗiba ya watsa a kan allon, nan take hoton jariran Sarki Gambo da ke kwance Unguwar zoma tana yanke musu cibi suka bayyana. Daga gefe kuma jariran Sarki Dikko ne kwance a saman gadon mahaifiiyarsu, ruwan ya sake watsa musu lokaci ɗaya jarirai huɗun suka fashe da kuka jikinsu yana wata irin karkarwa. Har sai da Sarki Dikko ya tsorata da ganin abin da yake faruwa da su, Boka Tsumbur ya ɗago ya dube su ya ce.
"A yanzu haka duk irin tawaya da nakasar da ke jikin jariranka, sun koma yaran Sarki Gambo. Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba."
Da sauri Sarki Dikko ya dube shi yana shirin yin magana suka ji tsibirin ya yi wata irin tsawa mai razanarwa.
*Ummmou Aslam Bint Adam*🌚
07062062624
[24/11, 15:59] Ameerah Adam: *KUNDI UKU*
©AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
GargaÉ—i: Ban amince a sarrafa mini littafi ta kowacce siga, ba tare da izinina ba. Yin hakan yana iya kai wa ga matakin Hukuma, don haka a kiyaye.
Tsokaci: Daga Masarautu, Sarakuna da sunayen yanki duka ƙirƙira ne. Idan ya yi daidai da labarin wani/wata arashi ne.
SHAFI NA SHIDA
Masarautar Kajjura
A haukace Sarki Gambo ya ƙarasa cikin zafin rai, ya maƙure wuyan Fulani Sadiya har sai da ta fara kakari. Murya a kausashe ya ce.
"Saboda me za ku kashe mana iyali? Saboda me za ku raba mu da uwar 'ya'yanmu?"
Fulani Sadiya ta tattara ƙarfinta ta fisge hannunta da ƙyar, sannan ta gyara zaman rigarta ta ce.
"Saboda har yanzu ba ka gama karantata ba, saboda har yanzu ba ka tantance maƙiyin ɓoye da na zahiri ba." Ta yi jim tana shafa wuyanta da har lokacin yake yi mata raɗaɗi sannan ta cigaba da cewa.
"Ranka shi daɗe! Kana tsammanin zan kashe Fulani Khadija sannan na bar 'ya'yan da ta haifa? Me ya sa ban haɗa har su na hallaka ba? Mai martaba! Yana da kyau ka nutsu domin ka san wanɗanda suke zagaye da kai. Amma Allah Ya taimake ka, ka san ba zan taɓa cutar da kai ba."
Fulani Sadiya tana zuwa nan sai ta fara zubar da hawaye, jikinsa ne ya yi sanyi. Ya riƙo ta a jikinsa, sai Fulani Sadiya ta sake fashewa da kuka ta ce.
"Na yi mamaki da har kake tsammanin zan iya cutar da Fulani Khadija, a duk tsawon shekarun da muka ɗauka. Ban taɓa tsammanin za ka yi mini mummunar shaida ba, ko don ban haihu ba kake yi mini haka oho?"
Ta sake fashewa da kukan kissa, nan take tausayinta ya kama shi. Cikin tattausan lafazi ya ce.
"Ku yi haƙuri Fulani, mutuwar Fulani Khadija ta gigita mu."
"Ina yi maka ta'aziyya ranka shi daÉ—e."
Fulani Sadiya ta sake furtawa tana kwantar da kai.
A gaggauce Sarki Gambo ya fita daga É—akinsa, ya koma rumfar ya zauna. Abin duniya goma da ashirin ya haÉ—e masa, dafe kansa ya yi da hannuwa biyu yana nazarin al'amuran baya da suka shiga tsakaninsa da Fulani Khadija.
Unguwar Zoma
Lami tana zaune tana yankewa tagwayen Sarki Gambo cibi, ta ga jikinsu ya fara wata irin karkarwa. A É—an tsorace ta ajiye su tana kallo, tana cikin haka Jakadiya ta shiga É—akin tana wurga mata tambaya.
"Me ya faru Lami? Me ya samu jariran nan? Lami kada ki jefa mu a masifa mu shiga uku, kin ga dai uwarsu a hannunmu ta mutu. Yanzu idan wani abin ya samu yaran nan me za mu cewa Mai martaba?"
Jikin Unguwar zoma nan take ya cigaba da karkarwa, bakinta yana rawa ta ce.
"Wallahi ban san me ya faru da su ba Jakadiya, ki yadda da ni haka na ga suna karkarwa ba tare da komai ba."
Unguwar zoma ba ta gama rufe baki ba, suka ga ɗaya daga cikin jariran ta fara jijjiga kai. Nan take wani ruwa mai kamar na ɗaurayar nama ya fara zuba daga idonta a madadin hawaye. Ɗayar kuma ƙafafuwnata suka shiga karkarwa, irin ruwan da ke fita daga idanun ɗayar shi ma ya fara tsattsafowa daga jikin ƙafafuwanta.
Jakadiya da Unguwar zoma kallon juna suka yi cike da tsoro, Jakadiya ta yi ƙasa da murya ta ce.
"Lami kina ganin abin da idanuna suke gani?"
"Ina gani Jakadiya, magana ta Allah na jima ban ga haihuwar da ta zo mini da al'ajabi kamar wannan ba."
Lami za ta yi magana, suka ji muryar Shamaki daga dokin ƙofa. A daidai lokacin uwar Bayi ta shiga ɗakin, duk suka yi carko-carko. Daɗin da suka ji a lokacin jariran sun dakata da kukan da suke yi, kuma ruwa da karkarwar da suke yi duk sun daina. A ɗan ɗarara Lami ta ɗauke ta ta cigaba gaba da gyara su, sannan Jakadiya ta ɗauke su ta fita da su. Dangin Fulani Khadija ne suka yi wa gidan sarautar tsinke, mahaifiyarta ban da kuka babu abin da take yi. Koda aka nuna musu jariran ba su bi ta kansu ba, suna shiga da suka ga irin kisan da aka yi mata duk sai jikinsu ya sake yin sanyi. Mahaifiyarta ta dubi mahaifin Fulani ta ce.
"Malam dama sai da na ce maka ba na son auren nan na Hadiza a gidan sarauta amma ka ƙi ka ji, dubi yadda makircin masarautar nan ya sa aka hallaka mana ita."
"Fatima! Ke musulma ce, kuma kin sani da Khadija ta yi aure a nan da mu aurar da ita a wani wurin ba nan ba. Duk abin da Allah Ya ƙaddara a cikin rayuwarta sai ya faru, abin da za ki yi mata a yanzu addu'a ce. Idan har 'yata Khadija ba ta da haƙƙi a wannan kisan da aka yi mata, na tabbata sai Ubangiji Ya yi mata sakayya."
Mahaifin Fulani Kgadija ya furta yana ɓoye hawayen da ke gangarowa daga idonsa.
Fulani Sadiya