← Book details Kundi Uku Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 24

Sashe 15

Kundi Uku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jakadiya tana fita daga sashen Fulani Zainaba kai tsaye sashen Fulani Sadiya ta nufa. A lokacin da ta ƙarasa Baiwa Sakina tana zaune tana matsa wa Fulanin ƙafa, kamar an jefo ta daga sama haka Jakadiya ta faɗa ɗakin tana sauke numfashi ta ce.
"Barka da hutawa ranki shi daÉ—e, barka da wannan lokaci gatan marar gata. Shugabar kowa mai tausayin talakawa, Allah Ya taimaki tauraruwa mai haske sasarin samaniya. Hutawarki lafiya giwar sarki kuma 'yar gaban goshinsa."
Kafin Jakadiya ta gama bambaɗanci, tuni Fulani Sadiya ta gama karantar akwai wata muhimmiyar maganar da ke tafe da ita. Don haka cikin isa da ƙasaita ta ce, "Jakadiya muna saurarenki."

Satar kallon Baiwa Sakina ta yi ta ce.
"Allah Ya taimake ki maganar tana buƙatar sirri."
Fulani Sadiya ta dubi Baiwa Sakina, don ta fahimci abin da take nufi amma sai ta ce.
"Tafi kanki tsaye Jakadiya babu wata damuwa."
Baiwa Sakina ta cigaba da matsa mata ƙafa, kanta a sunkuye tamkar ba ta san wainar da ake toyawa ba. Jakadiya ta gyara zama sannan ta zayyane wa Fulani Sadiya duk yadda suka yi da Fulani Zainaba, sannan ta ɗora da cewa.

"Ranki shi daɗe babban abin da ya ba ni mamaki, da na ji Fulani tana cewa koda ta mutu ɓoyayyan ɗanta da ke cikin masarautar nan zai maye gurbin muradinta domin jini ba wasa ba ne."

A hargitse Baiwa Sakina ta ɗago, saboda tashin hankali har sai da ta ƙware da tari. Amma da yake maganar Jakadiya ta girgiza Fulani Sadiya sai ba ta lura da yanayin da Sakina take ciki ba, cikin tsananin mamaki Fulani ta ce.
"Jakadiya kina nufin ita Zainaba ce take da É—a a cikin masarautar nan?"
Cikin son gwaninta da neman suna Jakadiya ta gyaÉ—a kai ta ce.
"Na rantse da Ubangiji mai girma abin da ta faÉ—a kenan ranki shi daÉ—e." Shiru Fulani ta yi tana nazari, sai kuwa ta ce.
"Idan kuwa da gaske É—an Zainaba yana raye to waye Sarki Gambo ya kashe? Domin kuwa duka duniya kowa ya shaida an kai masa jariri, kuma Zainaba ta haihu a wannan lokacin."
Jakadiya ta zuba tagumi cikin nazari ta ce, "Abin da ya ɗaure mini kai kenan ranki shi daɗe, domin kuwa uwar bayi ce ta karɓi haihuwar Zainaba, idan kuwa haka ne ya zama wajibi ta amsa duka waɗannan tambayoyin."
Da sauri Fulani Sadiya ta jinjina kai ta saki murmushi mai É—auke da ma'anoni sannan ta ce.
"Jakadiya!"
Yadda Fulani ta ambaci sunan Jakadiya ya sa ta É—ago gabanta yana faÉ—uwa, sai ta ga Fulani ta dubi Baiwa Sakina ta ce.

"Kin yi mini mai wuya da har kika binciko mini wannan maganar Jakadiya, sai dai akwai yuwuwar ki sake zuba mini ido a kanta sosai domin akwai muhimman bayanan da zan samu daga gare ki."
Jakadiya ta jinjina kai, sai Fulani Sadiya ta sake duban Baiwa Sakina ta ce.

"Ke kuma Sakina! Ina son damƙa miki kaso mafi girma na bincikena a hannunki."

A É—an hargitse Baiwa Sakina ta ce, "Na'am... iye ranki shi daÉ—e."
Fulani Sadiya ta yi mata kallon tsaf sannan ta ce.
"Ina son ki nutsu, domin tun a wancan lokacin na ce miki ƙofa a buɗe take da za ki cigaba da sanin waɗansu sirrikana."
Gumi ya shiga karyo wa Sakina, ta shiga gyaÉ—a kai gabanta yana cigaba da faÉ—uwa.

"Don haka, na ɗora miki alhakin binciko mini yadda wannan yanayin ya kasance, zan kira Uwar Bayi na ji daga gare ta. Ke kuma daga yau ne za ki fara shiga jikin Zainaba, domin ki gano mini a wurin da ɗanta yake a cikin masarautar nan. Haka kuma, ina son ki kasance mata lumbu-lumbu wutar ƙaiƙayi, ta yadda zan dinga samun bayanan sirri daga gare ki. Idan ta kama ma..."
Sai kuma Fulani ta yi shiru kamar mai nazari sai ta cigaba, "Wannan wata magana ce daban zan neme ki."
HaÉ—iye yawu Sakina ta yi cikin tsananin tashin hankali ta ce. "An gama ranki shi daÉ—e."

"Koda wasa, idan har kuka kuskura kuka munafunce ni, ko kuka ci amana. Ko kuma na gano wani abu da kaina, na rantse da girman Yesu mai ceto sai na shayar da ku ruwan mamakin da har gawarku ta ɓace a ƙarƙashin ƙasa ba za ku taɓa mantawa da ni ba." Baiwa Sakina ba, hatta Jakadiya sai da ta razana da jin furucin Fulani Sadiya da kalaman rantsuwarta na ƙarshe. Sai kuma suka ji ta saki dariya ta ce.
"Ita kuma Fulani Zainaba ku bar ni da ita, sai na shirya mata tuggun da za ta da gwammaci mutuwarta a kan rayuwarta. Domin sai ta yi danasanin shiga ɗakin sirrin Sarki Gambo da za ta yi, ba zan sa ya kashe ta ba. Zan bar ta ne har zuwa lokacin da zan gano wanne jinin nata ne yake numfashi a doron ƙasa da take cin alwashinsa."
Duk jikinsu ne ya yi sanyi, tsoron Fulani Sadiya da kaidinta ya mamaye zuciyoyinsu. Ban da gyaÉ—a kai babu abin da suke yi, Fulani ta dube su ta ce.
"Za ku iya tafiya, zuwa an jima kowaccenku zan aiko mata da da turmin zani da kallabi. Idan Allah Ya kai mu gobe da safe, ku zo zan shirya liyafa tare da ku. Wannan somin taɓi ne daga irin manyan darajojin da zan ɗaga ku a gidan, matuƙar kuka cigaba da yi mini biyayya."

Duk da sun ji daɗi amma har lokacin zuƙatansu cike suke da fargaba da tashin hankali, cikin yaƙe suka russuna suka ce.
"Godiya muke ranki shi daÉ—e."
Umarnin fita ta ba su, bayan sun fita ta cigaba da zagayen É—akin tana nazari sannan ta ce.
"Lokaci ya yi da zan yi amfani da ku, da zarar na gama cin moriyar ganga sai kuma na yasar da kwauronta."
Fulani Sadiya ta ƙarasa maganar tana sakin murmushin ƙeta.

Sarki Gambo

A hargitse Sarki Gambo ya miƙe tsaye cikin ƙaɗuwa da tashin hankali. Jikinsa har yawa yake idanunsa suka ƙanƙance, wata sharɓeɓiyar takobin da ke rataye a jikin bango ya zaro ya saita daidai wuyan Malami ya ce.
"Ka sanar da mu gaskiyar abin da kuka faÉ—a, idan ba haka ba za mu datse kanku."
A madadin Malami ya razana, sai ya saki murmushi ya ce.
"Ba za ka iya kashe ni ba Sarki Gambo koda kuwa a sume nake, kai ko ina gargarar mutuwa na fi ƙarfinka!"
Kalaman Malami suka ƙara harzuƙa Sarki Gambo, da sauri ya wurgar da takobin ya cakumi wuyan Malami ya shaƙe ya ce.
"Kada ku sake furta munanan kalamai akan jininmu, kun yi sa'a kune Malami. Da mun rantse da ubangiji haske sai mun azabatar da ku."
Duk da jikin Malami yana rawa irin na tsufa, amma hakan bai hana shi tattara ƙarfinsa ya hankaɗe Sarki Gambo ba. Ya furzar da iska mai zafi sannan ya ce.
"Da za ka ajiye zafin ranka a gefe, da na taimaka maka har ka samu ka ga hasken da zai haska maka hanya. Idan kuma kana tunanin hanyar da ka bi ita ce mafita, ga fili nan ga doki sukuwa kawai ya rage maka." Jikin Sarki Gambo ya yi sanyi, don haka ya zauna daɓar, kamar wanda aka zarewa laka a jiki. Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ce.
"Malami zuciyarmu ta gagara aminta da mummunan labarin da kuka sanar da mu. Ta yaya aka haihu a ragaya? Me ya sa sai tagwayenmu? Wane ne ya aikata mana haka?"

"Tambayar da ni kaina nake wurga wa kaina kenan, sai dai har kawo yanzu da nake yi maka wannan maganar ban hangi wata alama, haske ko tauraron wanda ya aikata wannan mummunan sihirin ba."
Malami ya furta cikin damuwa, jin haka ya sa Sarki Gambo ya fashe da kuka. Cikin mamaki Malami ya girgiza kai, ya dafa kafaÉ—arsa ya ce.
"Haƙiƙa na haɗu da jajirtattun sarakuna, na yi mu'amala da sadaukai kuma jaruman mazaje. Amma ban taɓa cin karo da ingarman namiji mai dakakkiyar zuciya kamar kai ba Sarki Gambo, tabbas wannan hawayen naka na tabbata ba zai tashi a banza ba. Don na tabbata ƙashin gwiwar kura har abada ya gagari fiƙar gawurtattun karnuka."
Lokaci É—aya Sarki Gambo ya goge hawayen idanunsa, ya dubi malami cikin cin alwashi, zafin zuciya da kalaman É—aukar fansa ya ce.
"Mun yi rantsu da fatalwar iyayenmu, mun yi rantsuwa da abar bauta tsumbutuwa. Mun rantse da abar bautar da kakannin kakaninmu suka mutu a wurin bautarsu, haka kuma mun yi rantse da duk wani kaifin tsini da rashin imaninmu. Duk wanda ya aikata mana wannan mummunan al'amarin, sai mun azabtar da ruhinsa azaba mai raɗaɗi. Sai mum shayar da shi ruwan dalmar da har a ƙare danginsu za su dawwama a ƙarƙashin uƙubarmu. Malami!"
Ya kira sunan Malami da wata irin murya, yadda idanun Sarki Gambo suka kaɗa jajir ya sa tsoro ya ɗarsu a zuciyar Malami, don bai taɓa ganin mummunan yanayin haka a tatare da shi ba. Jiki a sanyaye Malami ya amsa, Sarki Gambo ya cigaba da ce.
"Ko numfashi da arzkinmu za su ƙare, ko bayi da sarautarmu za su ƙare ko lafiya da jininmu duka mutanen yankin nan zai ƙare, mun rantse da hasken rana sai mun ɗauki mummuna mataki a kan duk wani mahaluki da yake da saka hannu a wannan mummunan al'amarin."
Malami ya dafa hannunsa ya ce, "Ina tare da kai ɗari bisa ɗari sadaukin sadaukai, ni mai haska maka kowacce hanya ce da za ta bayyana gaskiya. Musamman da ya kasance waɗannan yara su kaɗai za ka iya mallaka har ƙarshen rayuwarka..."

"Mene ne mafita malami? Kuma ta ina za mu fara?"
Sarki Gambo ya katse shi, wani kan ƙwarangwal Malami ya ɗauka ya rubuta wata aya da alƙalami da tawada a tsakiyar kansa. Sai ya kafe shi a kan allon farin ƙarfe, ya hura masa wuta yana kiran waɗansu sunayen aljanu. Ya jima yana abu ɗaya sannan ya ɗago fuskarsa da ta haɗa gumi sharkaf ya ce.
"Na hango mafita guda biyu, wacce idan muka bi su za mu samu sukunin kamo bakin zaren."

Tsoho Sulaimanu
Chapter 15 · 0% Book details